< Ezekiyel 11 >
1 Sa’an nan Ruhu ya ɗaga ni sama ya kawo ni ƙofar gidan Ubangiji wadda take fuskantar gabas. Can a mashigi zuwa ƙofar akwai mutum ashirin da biyar, na kuma ga a cikinsu akwai Ya’azaniya ɗan Azzur da Felatiya ɗan Benahiya, shugabannin jama’a.
Un Gars mani pacēla un mani nesa pie Tā Kunga nama priekšējiem vārtiem, kas pret rītiem stāv; un redzi, pie vārtu durvīm bija divdesmit un pieci vīri, un viņu vidū es redzēju Jazaniju, Asura dēlu, un Platiju, Benajas dēlu, ļaužu virsniekus.
2 Ubangiji ya ce mini, “Ɗan mutum, waɗannan su ne mutanen da suke ƙulla mugunta suna kuma ba da muguwa shawara a cikin wannan birni.
Un Viņš uz mani sacīja: cilvēka bērns, šie ir tie vīri, kas netaisnību izdomā un dod ļaunu padomu šinī pilsētā.
3 Suna cewa, ‘Lokaci bai yi kusa da za a gina gidaje ba? Wannan birni yana tukunyar dahuwa, mu ne kuwa naman.’
Tie saka: laiks vēl nav klāt, namus celt! Šī (pilsēta) ir tas pods un mēs tā gaļa.
4 Saboda haka yi annabci a kansu; yi annabci, ɗan mutum.”
Tāpēc sludini pret tiem, sludini, cilvēka bērns!
5 Sai Ruhun Ubangiji ya sauko a kaina, ya kuma faɗa mini in ce, “Ga abin da Ubangiji yana cewa, haka kuke cewa, ya gidan Isra’ila, amma na san abin da yake a zuciyarku.
Tad Tā Kunga Gars krita uz mani un uz mani sacīja: runā: tā saka Tas Kungs: jūs, ak Israēla nams, sakāt tā, jo Es zinu, kādas domas jums nāk prātā.
6 Kun kashe mutane da yawa a wannan birni kuka kuma cika titunanta da gawawwaki.
Varen daudz ir to, ko esat nokāvuši šinī pilsētā, un viņas ielas jūs esat pildījuši ar nokautiem.
7 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa gawawwakin da kuka zubar a can su ne naman, wannan birni kuwa ita ce tukunya, amma zan kore ku daga cikinta.
Tādēļ Tas Kungs Dievs tā saka: jūsu nokautie, ko jūs viņas vidū esat nogāzuši, tie ir tā gaļa, un šī ir tas pods, bet jūs no viņas vidus izvedīs ārā.
8 Kuna jin tsoron takobi, kuma takobi ne zan kawo muku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Jūs bīstaties no zobena, un zobenu Es vedīšu pār jums, saka Tas Kungs Dievs.
9 Zan kore ku daga birnin in miƙa ku a hannuwan baƙi in kuma azabtar da ku.
Es jūs no viņas vidus izvedīšu ārā un jūs nodošu svešiem rokā un nesīšu jums tiesu.
10 Za ku mutu ta wurin takobi, zan kuma hukunta ku a iyakokin Isra’ila. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
Jūs kritīsiet caur zobenu, Es jūs sodīšu pie Israēla robežām, un jūs samanīsiet, ka Es esmu Tas Kungs.
11 Wannan birni ba za tă zama muku tukunya ba, ba kuwa za ku zama nama a cikinta ba; zan hukunta ku a iyakokin Isra’ila.
Šī (pilsēta) jums nebūs par podu, un jūs nebūsiet par gaļu viņas vidū; pie Israēla robežām Es jūs gribu sodīt.
12 Za ku kuwa san cewa ni ne Ubangiji, gama ba ku bi ƙa’idodina ba balle ku kiyaye dokokina, amma kuka bi hanyoyin al’ummai kewaye da ku.”
Un jūs samanīsiet, ka Es esmu Tas Kungs, tāpēc ka neesat staigājuši Manos likumos nedz darījuši Manas tiesas, bet turējušies pēc pagānu tiesām, kas jums visapkārt.
13 Yanzu yayinda nake yin annabci, sai Felatiya ɗan Benahiya ya mutu. Sai na fāɗi rubda ciki na kuma yi kuka da babbar murya na ce, “Kash, Ubangiji Mai Iko Duka! Za ka hallaka raguwar Isra’ila ƙaƙaf ne?”
Un notikās, kad es sludināju, tad Platija, Benajas dēls, nomira. Tad es kritu uz savu vaigu un brēcu ar stipru balsi un sacīju: Ak Kungs Dievs, vai tu pavisam galu darīsi Israēla atlikušiem?
14 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Tad Tā Kunga vārds notika uz mani sacīdams:
15 “Ɗan mutum,’yan’uwanka,’yan’uwanka waɗanda suke danginka na cikinka da kuma dukan gidan Isra’ila su ne waɗanda mutanen Urushalima suka ce, ‘Su ne da nisa daga Ubangiji; an ba mu wannan ƙasa ta zama mallakarmu.’
Cilvēka bērns, tie ir tavi brāļi, tavi brāļi, tavi radi, un viss Israēla nams visnotaļ ir tie, uz ko Jeruzālemes iedzīvotāji saka: atkāpjaties tālu no Tā Kunga, šī zeme mums ir dota par mantību.
16 “Saboda haka ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ko da yake na kore su zuwa cikin al’ummai na kuma warwatsa su cikin ƙasashe, duk da haka na zama wuri mai tsarki a gare su a ƙasashen da suka tafi.’
Tādēļ saki: tā saka Tas Kungs Dievs: jebšu Es tos tālu esmu aizvedis starp tautām un tos izkaisījis pa valstīm: taču Es par mazu brīdi tiem būšu par svētumu tanīs valstīs, kur tie nākuši.
17 “Saboda haka, ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan tattaro ku daga al’ummai in kuma dawo da ku daga ƙasashen da aka warwatsa ku, zan kuwa sāke mayar muku da ƙasar Isra’ila.’
Tādēļ saki: tā saka Tas Kungs Dievs: tiešām, Es jūs sapulcināšu no tām tautām un jūs salasīšu no tām valstīm, kur esat izkaisīti, un Es jums došu Israēla zemi.
18 “Za su dawo gare ta su kawar da dukan mugayen siffofi da gumaka masu banƙyama.
Un tie nāks uz turieni un ņems visus viņas gānekļus un visas viņas negantības no tās nost.
19 Zan ba su zuciya ɗaya in kuma sa sabon ruhu a cikinsu; zan fid da zuciyar dutse daga gare su in kuma ba su zuciya ta nama.
Un Es tiem došu vienādu sirdi un Es jums došu jaunu garu, un atņemšu to akmens sirdi no viņu miesām un tiem došu miesīgu sirdi,
20 Sa’an nan za su bi ƙa’idodina su kuma yi hankali ga kiyaye dokokina. Za su zama mutanena, ni kuwa zan zama Allahnsu.
Lai tie staigā Manos likumos un sarga Manas tiesas un tās dara, un tie Man būs par ļaudīm, un Es tiem būšu par Dievu.
21 Amma game da waɗanda zukatansu suka karkata ga bin mugayen siffofi da gumakan banƙyama, zan sāka musu gwargwadon ayyukansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
Bet tiem, kam sirds pēc savu gānekļu un neganto elku prāta dzenās, tiem Es viņu grēkus metīšu uz viņu galvu, saka Tas Kungs Dievs.
22 Sa’an nan kerubobi, tare da da’irori kusa da su, suka buɗe fikafikansu, ɗaukakar Allah kuwa tana a bisansu.
Tad tie ķerubi pacēla savus spārnus un tie skrituļi bija viņiem sānis, un Israēla Dieva godība bija virsū pār tiem.
23 Ɗaukakar Ubangiji ta haura daga cikin birnin ta sauka a bisa dutse gabas da shi.
Un Tā Kunga godība cēlās no pilsētas vidus un nostājās uz tā kalna, kas pilsētai pret rītiem.
24 Ruhu ya ɗaga ni sama ya kuma kawo ni ga masu zaman bauta a ƙasar Babilon cikin wahayin da Ruhun Allah ya bayar. Sa’an nan wahayin da na gani ya rabu da ni,
Tad Gars mani pacēla un mani aizveda parādīšanā un caur Dieva Garu uz Kaldeju pie tiem aizvestiem, un tā parādīšana, ko es biju redzējis, no manis nozuda.
25 na kuwa faɗa wa masu zaman bautan dukan abin da Ubangiji ya nuna mini.
Un es tiem aizvestiem runāju visus Tā Kunga vārdus, ko Viņš man bija parādījis.