< Ezekiyel 11 >

1 Sa’an nan Ruhu ya ɗaga ni sama ya kawo ni ƙofar gidan Ubangiji wadda take fuskantar gabas. Can a mashigi zuwa ƙofar akwai mutum ashirin da biyar, na kuma ga a cikinsu akwai Ya’azaniya ɗan Azzur da Felatiya ɗan Benahiya, shugabannin jama’a.
Et l'esprit me ravit, et il me conduisit sur la porte de la façade du temple du Seigneur, celle qui regarde l'Orient. Et voilà qu'il y avait sur le portique environ vingt-cinq hommes, et je vis au milieu d'eux Jéchonias, fils d'Ezer, et Phaltias, fils de Banaias, princes du peuple.
2 Ubangiji ya ce mini, “Ɗan mutum, waɗannan su ne mutanen da suke ƙulla mugunta suna kuma ba da muguwa shawara a cikin wannan birni.
Et le Seigneur me dit: Fils de l'homme, voici des hommes qui conçoivent des vanités, et tiennent de mauvais conseils en cette ville,
3 Suna cewa, ‘Lokaci bai yi kusa da za a gina gidaje ba? Wannan birni yana tukunyar dahuwa, mu ne kuwa naman.’
Disant: Est-ce que ce temple a été bâti récemment? Il est chaudière, et la chair, c'est nous.
4 Saboda haka yi annabci a kansu; yi annabci, ɗan mutum.”
À cause de cela, prophétise contre eux, prophétise, fils de l'homme.
5 Sai Ruhun Ubangiji ya sauko a kaina, ya kuma faɗa mini in ce, “Ga abin da Ubangiji yana cewa, haka kuke cewa, ya gidan Isra’ila, amma na san abin da yake a zuciyarku.
Et sur moi l'esprit du Seigneur tomba, et il me dit: Parle, voici ce que dit le Seigneur: C'est ainsi que vous parlez, maison d'Israël; les conseils téméraires de votre esprit, je les connais.
6 Kun kashe mutane da yawa a wannan birni kuka kuma cika titunanta da gawawwaki.
Vous avez multiplié vos meurtres en cette ville, et vous avez rempli ses rues de cadavres.
7 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa gawawwakin da kuka zubar a can su ne naman, wannan birni kuwa ita ce tukunya, amma zan kore ku daga cikinta.
À cause de cela, voici ce que dit le Seigneur: Les morts que vous avez frappés au milieu de cette ville, sont les chairs, cette ville est la chaudière, et vous, je vous chasserai du milieu de cette ville.
8 Kuna jin tsoron takobi, kuma takobi ne zan kawo muku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Vous avez peur du glaive, et c'est le glaive que j'amènerai sur vous, dit le Seigneur.
9 Zan kore ku daga birnin in miƙa ku a hannuwan baƙi in kuma azabtar da ku.
Et je vous chasserai du milieu de cette ville, et je vous livrerai à des étrangers, et j'exécuterai mes jugements sur vous.
10 Za ku mutu ta wurin takobi, zan kuma hukunta ku a iyakokin Isra’ila. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
Vous tomberez sous le glaive; je vous jugerai sur les montagnes d'Israël, et vous reconnaîtrez que je suis le Seigneur.
11 Wannan birni ba za tă zama muku tukunya ba, ba kuwa za ku zama nama a cikinta ba; zan hukunta ku a iyakokin Isra’ila.
[La ville] ne sera pas pour vous comme une chaudière, au milieu de laquelle vous seriez la viande. Je vous jugerai sur les limites d'Israël.
12 Za ku kuwa san cewa ni ne Ubangiji, gama ba ku bi ƙa’idodina ba balle ku kiyaye dokokina, amma kuka bi hanyoyin al’ummai kewaye da ku.”
Et vous saurez que je suis le Seigneur.
13 Yanzu yayinda nake yin annabci, sai Felatiya ɗan Benahiya ya mutu. Sai na fāɗi rubda ciki na kuma yi kuka da babbar murya na ce, “Kash, Ubangiji Mai Iko Duka! Za ka hallaka raguwar Isra’ila ƙaƙaf ne?”
Et ceci advint: pendant que je prophétisais, Phaltias, fils de Banaias, mourut, et je tombai la face contre terre, et je criai à haute voix, et je dis: Hélas! hélas! Seigneur, allez-vous détruire les restes d'Israël?
14 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et la parole du Seigneur me vint, disant:
15 “Ɗan mutum,’yan’uwanka,’yan’uwanka waɗanda suke danginka na cikinka da kuma dukan gidan Isra’ila su ne waɗanda mutanen Urushalima suka ce, ‘Su ne da nisa daga Ubangiji; an ba mu wannan ƙasa ta zama mallakarmu.’
Fils de l'homme, les frères, et les hommes avec toi captifs, et toute la maison d'Israël, ce sont tous ceux à qui les habitants de Jérusalem ont dit: Retirez-vous loin du Seigneur; c'est à nous que cette terre a été donnée pour héritage.
16 “Saboda haka ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ko da yake na kore su zuwa cikin al’ummai na kuma warwatsa su cikin ƙasashe, duk da haka na zama wuri mai tsarki a gare su a ƙasashen da suka tafi.’
À cause de cela, dis-leur: Ainsi parle le Seigneur: Je les chasserai parmi les nations; je les disperserai en toute terre, et je serai pour eux comme un petit sanctuaire, en toutes les contrées où ils iront résider.
17 “Saboda haka, ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan tattaro ku daga al’ummai in kuma dawo da ku daga ƙasashen da aka warwatsa ku, zan kuwa sāke mayar muku da ƙasar Isra’ila.’
À cause de cela, dis-leur: Ainsi parle le Seigneur: Je les recueillerai parmi les nations; je les rassemblerai des contrées où je les aurai dispersés, et je leur donnerai la terre d'Israël.
18 “Za su dawo gare ta su kawar da dukan mugayen siffofi da gumaka masu banƙyama.
Et ils y rentreront, et ils en déracineront toutes les abominations et toutes les iniquités.
19 Zan ba su zuciya ɗaya in kuma sa sabon ruhu a cikinsu; zan fid da zuciyar dutse daga gare su in kuma ba su zuciya ta nama.
Et je leur donnerai un autre cœur, et je mettrai en eux un esprit nouveau, et je retirerai de leur chair le cœur de pierre, et je leur donnerai un cœur de chair;
20 Sa’an nan za su bi ƙa’idodina su kuma yi hankali ga kiyaye dokokina. Za su zama mutanena, ni kuwa zan zama Allahnsu.
Afin qu'ils marchent en mes commandements, et qu'ils gardent mes ordonnances et les accomplissent; et ils seront mon peuple, et je serai leur Dieu.
21 Amma game da waɗanda zukatansu suka karkata ga bin mugayen siffofi da gumakan banƙyama, zan sāka musu gwargwadon ayyukansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
Pour ceux dont le cœur a cheminé, comme leur cœur, en des abominations et des iniquités, je ferai retomber leurs voies sur leurs têtes, dit le Seigneur.
22 Sa’an nan kerubobi, tare da da’irori kusa da su, suka buɗe fikafikansu, ɗaukakar Allah kuwa tana a bisansu.
Et les chérubins déployèrent leurs ailes, et ils s'élevèrent ayant à côté d'eux les roues, et au-dessus d'eux la gloire du Dieu d'Israël.
23 Ɗaukakar Ubangiji ta haura daga cikin birnin ta sauka a bisa dutse gabas da shi.
Et la gloire du Seigneur monta du milieu de la ville, et elle s'arrêta en face de la ville sur les montagnes
24 Ruhu ya ɗaga ni sama ya kuma kawo ni ga masu zaman bauta a ƙasar Babilon cikin wahayin da Ruhun Allah ya bayar. Sa’an nan wahayin da na gani ya rabu da ni,
Et l'esprit me ravit; et en ma vision venant de l'Esprit de Dieu il me ramena sur la terre des Chaldéens, parmi les captifs. Et je descendis de la vision que j'avais eue.
25 na kuwa faɗa wa masu zaman bautan dukan abin da Ubangiji ya nuna mini.
Et je répétai aux captifs toutes les paroles que Dieu m'avait révélées.

< Ezekiyel 11 >