< Ezekiyel 11 >

1 Sa’an nan Ruhu ya ɗaga ni sama ya kawo ni ƙofar gidan Ubangiji wadda take fuskantar gabas. Can a mashigi zuwa ƙofar akwai mutum ashirin da biyar, na kuma ga a cikinsu akwai Ya’azaniya ɗan Azzur da Felatiya ɗan Benahiya, shugabannin jama’a.
And a spirit bore me up, and brought me unto the east gate of the house of the Lord, which looketh eastward: and behold, there were at the entrance of the gate five and twenty men; and I saw in the midst of them Yaazanyah the son of 'Azzur, and Pelatyahu the son of Benayahu, princes of the people.
2 Ubangiji ya ce mini, “Ɗan mutum, waɗannan su ne mutanen da suke ƙulla mugunta suna kuma ba da muguwa shawara a cikin wannan birni.
Then said he unto me, Son of man, these are the men that devise wickedness, and give evil counsel in this city;
3 Suna cewa, ‘Lokaci bai yi kusa da za a gina gidaje ba? Wannan birni yana tukunyar dahuwa, mu ne kuwa naman.’
Who say, [The evil] is not near; so let us build houses: this [city] is the pot, and we are the flesh.
4 Saboda haka yi annabci a kansu; yi annabci, ɗan mutum.”
Therefore prophesy against them, prophesy, O son of man.
5 Sai Ruhun Ubangiji ya sauko a kaina, ya kuma faɗa mini in ce, “Ga abin da Ubangiji yana cewa, haka kuke cewa, ya gidan Isra’ila, amma na san abin da yake a zuciyarku.
And the Spirit of the Lord fell upon me, and said unto me, Speak, Thus hath said the Lord, Thus have ye said, O house of Israel; and whatever cometh into your mind, do I know full well.
6 Kun kashe mutane da yawa a wannan birni kuka kuma cika titunanta da gawawwaki.
Ye have multiplied those slain by you in this city, and ye have filled its streets with the slain.
7 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa gawawwakin da kuka zubar a can su ne naman, wannan birni kuwa ita ce tukunya, amma zan kore ku daga cikinta.
Therefore thus hath said the Lord Eternal, Those slain by you whom ye have struck down in the midst of it, —they are the flesh, and this place is the pot; but you are to be removed out of the midst of it.
8 Kuna jin tsoron takobi, kuma takobi ne zan kawo muku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
The sword have ye feared: and the sword will I bring over you, saith the Lord Eternal.
9 Zan kore ku daga birnin in miƙa ku a hannuwan baƙi in kuma azabtar da ku.
And I will remove you out of the midst of it, and I will give you up into the hand of strangers, and will execute punishments among you.
10 Za ku mutu ta wurin takobi, zan kuma hukunta ku a iyakokin Isra’ila. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
By the sword shall ye fall; on the boundary of Israel will I judge you: and ye shall know that I am the Lord.
11 Wannan birni ba za tă zama muku tukunya ba, ba kuwa za ku zama nama a cikinta ba; zan hukunta ku a iyakokin Isra’ila.
This place shall not be unto you as a pot, so that you should be as flesh in the midst of it; but on the boundary of Israel will I judge you.
12 Za ku kuwa san cewa ni ne Ubangiji, gama ba ku bi ƙa’idodina ba balle ku kiyaye dokokina, amma kuka bi hanyoyin al’ummai kewaye da ku.”
And ye shall know that I am the Lord: because in my statutes have ye not walked, and my ordinances have ye not executed; but ye have done after the ordinances of the nations that are round about you.
13 Yanzu yayinda nake yin annabci, sai Felatiya ɗan Benahiya ya mutu. Sai na fāɗi rubda ciki na kuma yi kuka da babbar murya na ce, “Kash, Ubangiji Mai Iko Duka! Za ka hallaka raguwar Isra’ila ƙaƙaf ne?”
And it came to pass, as I was prophesying, that Pelatyahu the son of Benayah died. Then fell I down upon my face, and cried with a loud voice, and said, Ah Lord Eternal! wilt thou make a full end of the remnant of Israel?
14 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Then came the word of the Lord unto me, saying,
15 “Ɗan mutum,’yan’uwanka,’yan’uwanka waɗanda suke danginka na cikinka da kuma dukan gidan Isra’ila su ne waɗanda mutanen Urushalima suka ce, ‘Su ne da nisa daga Ubangiji; an ba mu wannan ƙasa ta zama mallakarmu.’
Son of man, thy brethren, even thy brethren, the men of thy kindred, and the whole house of Israel altogether, are they unto whom the inhabitants of Jerusalem have said, Remain you far from the Lord: unto us is this land given for a possession.
16 “Saboda haka ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ko da yake na kore su zuwa cikin al’ummai na kuma warwatsa su cikin ƙasashe, duk da haka na zama wuri mai tsarki a gare su a ƙasashen da suka tafi.’
Therefore say, Thus hath said the Lord Eternal, Although I have removed them far away among the nations, and although I have scattered them among the countries: yet will I be to them as a minor sanctuary in the countries whither they are come.
17 “Saboda haka, ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan tattaro ku daga al’ummai in kuma dawo da ku daga ƙasashen da aka warwatsa ku, zan kuwa sāke mayar muku da ƙasar Isra’ila.’
Therefore say, Thus hath said the Lord Eternal, I will both gather you from the people, and assemble you out of the countries whether ye have been scattered, and I will give you the land of Israel.
18 “Za su dawo gare ta su kawar da dukan mugayen siffofi da gumaka masu banƙyama.
And they shall come thither, and they shall remove all its detestable things, and all its abominations out of it.
19 Zan ba su zuciya ɗaya in kuma sa sabon ruhu a cikinsu; zan fid da zuciyar dutse daga gare su in kuma ba su zuciya ta nama.
And I will give them one single heart, and a new spirit will I put within you; and I will remove the heart of stone out of their body, and I will give unto them a heart of flesh:
20 Sa’an nan za su bi ƙa’idodina su kuma yi hankali ga kiyaye dokokina. Za su zama mutanena, ni kuwa zan zama Allahnsu.
In order that they may walk in my statutes, and keep my ordinances, and do them; and they shall be unto me for a people, and I will indeed be unto them for a God.
21 Amma game da waɗanda zukatansu suka karkata ga bin mugayen siffofi da gumakan banƙyama, zan sāka musu gwargwadon ayyukansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
But as for those whose heart walketh after the heart of their detestable things and their abominations, their way do I bring upon their own head, saith the Lord Eternal.
22 Sa’an nan kerubobi, tare da da’irori kusa da su, suka buɗe fikafikansu, ɗaukakar Allah kuwa tana a bisansu.
Then did the cherubim lift up their wings, and the wheels at the same time with them; and the glory of the God of Israel was over them above.
23 Ɗaukakar Ubangiji ta haura daga cikin birnin ta sauka a bisa dutse gabas da shi.
And the glory of the Lord ascended from the midst of the city, and halted upon the mount which is on the east side of the city.
24 Ruhu ya ɗaga ni sama ya kuma kawo ni ga masu zaman bauta a ƙasar Babilon cikin wahayin da Ruhun Allah ya bayar. Sa’an nan wahayin da na gani ya rabu da ni,
But a spirit bore me up, and brought me into Chaldea, to those in exile, in the appearance through the spirit of God: and then ascended away from me the appearance which I had seen.
25 na kuwa faɗa wa masu zaman bautan dukan abin da Ubangiji ya nuna mini.
Then did I speak unto those in exile all the things that the Lord had shown me.

< Ezekiyel 11 >