< Ezekiyel 11 >

1 Sa’an nan Ruhu ya ɗaga ni sama ya kawo ni ƙofar gidan Ubangiji wadda take fuskantar gabas. Can a mashigi zuwa ƙofar akwai mutum ashirin da biyar, na kuma ga a cikinsu akwai Ya’azaniya ɗan Azzur da Felatiya ɗan Benahiya, shugabannin jama’a.
I vznesl mne Duch, a přivedl mne k bráně východní domu Hospodinova, kteráž patří na východ, a aj, ve vratech brány té pětmecítma mužů, mezi kterýmiž jsem viděl Jazaniáše syna Azurova, a Pelatiáše syna Banaiášova, knížata lidu.
2 Ubangiji ya ce mini, “Ɗan mutum, waɗannan su ne mutanen da suke ƙulla mugunta suna kuma ba da muguwa shawara a cikin wannan birni.
Tedy řekl mi: Synu člověčí, to jsou ti muži, kteříž smýšlejí nepravost, a skládají radu zlou v městě tomto,
3 Suna cewa, ‘Lokaci bai yi kusa da za a gina gidaje ba? Wannan birni yana tukunyar dahuwa, mu ne kuwa naman.’
Říkajíce: Nestavějme domů blízko, sic město bude hrnec a my maso.
4 Saboda haka yi annabci a kansu; yi annabci, ɗan mutum.”
Protož prorokuj proti nim, prorokuj, synu člověčí.
5 Sai Ruhun Ubangiji ya sauko a kaina, ya kuma faɗa mini in ce, “Ga abin da Ubangiji yana cewa, haka kuke cewa, ya gidan Isra’ila, amma na san abin da yake a zuciyarku.
I sstoupil na mne Duch Hospodinův, a řekl mi: Rci: Takto dí Hospodin: Tak říkáte, dome Izraelský. Nebo což vám koli vstupuje na mysl, o tom já vím.
6 Kun kashe mutane da yawa a wannan birni kuka kuma cika titunanta da gawawwaki.
Veliké množství zmordovali jste v městě tomto, a naplnili jste ulice jeho zbitými.
7 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa gawawwakin da kuka zubar a can su ne naman, wannan birni kuwa ita ce tukunya, amma zan kore ku daga cikinta.
Protož takto praví Panovník Hospodin: Ti, kteříž jsou zbiti od vás, kteréž jste skladli u prostřed něho, oniť jsou maso, město pak hrnec, ale vás vyvedu z prostředku jeho.
8 Kuna jin tsoron takobi, kuma takobi ne zan kawo muku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Báli jste se meče, ale meč uvedu na vás, praví Panovník Hospodin.
9 Zan kore ku daga birnin in miƙa ku a hannuwan baƙi in kuma azabtar da ku.
A vyvedu vás z prostředku jeho, a dám vás v ruku cizích, a vykonám nad vámi soudy.
10 Za ku mutu ta wurin takobi, zan kuma hukunta ku a iyakokin Isra’ila. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
Mečem padnete, na pomezí Izraelském souditi vás budu, a zvíte, že já jsem Hospodin.
11 Wannan birni ba za tă zama muku tukunya ba, ba kuwa za ku zama nama a cikinta ba; zan hukunta ku a iyakokin Isra’ila.
Město nebude vám hrnec, aniž vy budete u prostřed něho maso, na pomezí Izraelském souditi vás budu.
12 Za ku kuwa san cewa ni ne Ubangiji, gama ba ku bi ƙa’idodina ba balle ku kiyaye dokokina, amma kuka bi hanyoyin al’ummai kewaye da ku.”
I zvíte, že já jsem Hospodin, poněvadž jste v ustanoveních mých nechodili, a soudů mých nečinili, a podlé soudů těch národů, kteříž jsou vůkol vás, činili jste.
13 Yanzu yayinda nake yin annabci, sai Felatiya ɗan Benahiya ya mutu. Sai na fāɗi rubda ciki na kuma yi kuka da babbar murya na ce, “Kash, Ubangiji Mai Iko Duka! Za ka hallaka raguwar Isra’ila ƙaƙaf ne?”
Stalo se pak, když jsem prorokoval, že Pelatiáš syn Banaiášův umřel. Pročež padl jsem na tvář svou, a zvolal jsem hlasem velikým, řka: Ach, Panovníče Hospodine, skonání, činíš ostatkům Izraelským.
14 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Tedy stalo se slovo Hospodinovo ke mně, řkoucí:
15 “Ɗan mutum,’yan’uwanka,’yan’uwanka waɗanda suke danginka na cikinka da kuma dukan gidan Isra’ila su ne waɗanda mutanen Urushalima suka ce, ‘Su ne da nisa daga Ubangiji; an ba mu wannan ƙasa ta zama mallakarmu.’
Synu člověčí, bratří tvoji, bratří tvoji, příbuzní tvoji, a všecken dům Izraelský, všecken dům, kterýmž říkali obyvatelé Jeruzalémští: Daleko zajděte od Hospodina, nám jest dána země tato v dědictví.
16 “Saboda haka ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ko da yake na kore su zuwa cikin al’ummai na kuma warwatsa su cikin ƙasashe, duk da haka na zama wuri mai tsarki a gare su a ƙasashen da suka tafi.’
Protož rci: Takto praví Panovník Hospodin: Ačkoli daleko zahnal jsem je mezi národy, a ačkoli rozptýlil jsem je do zemí, však budu jim svatyní i za ten malý čas v zemích těch, do kterýchž přijdou.
17 “Saboda haka, ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan tattaro ku daga al’ummai in kuma dawo da ku daga ƙasashen da aka warwatsa ku, zan kuwa sāke mayar muku da ƙasar Isra’ila.’
Protož rci: Takto praví Panovník Hospodin: Shromáždím vás z národů a zberu vás z zemí, do kterýchž rozptýleni jste, a dám vám zemi Izraelskou.
18 “Za su dawo gare ta su kawar da dukan mugayen siffofi da gumaka masu banƙyama.
I vejdou tam, a vyvrhou všecky mrzkosti její, i všecky ohavnosti její z ní.
19 Zan ba su zuciya ɗaya in kuma sa sabon ruhu a cikinsu; zan fid da zuciyar dutse daga gare su in kuma ba su zuciya ta nama.
Nebo dám jim srdce jedno, a Ducha nového dám do vnitřností vašich, a odejmu srdce kamenné z těla jejich, a dám jim srdce masité,
20 Sa’an nan za su bi ƙa’idodina su kuma yi hankali ga kiyaye dokokina. Za su zama mutanena, ni kuwa zan zama Allahnsu.
Aby v ustanoveních mých chodili, a soudů mých ostříhali, a činili je. I budou lidem mým, a já budu jejich Bohem.
21 Amma game da waɗanda zukatansu suka karkata ga bin mugayen siffofi da gumakan banƙyama, zan sāka musu gwargwadon ayyukansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
Kterýchž pak srdce chodilo by po žádostech mrzkostí svých a ohavností svých, těch cestu na hlavu jejich obrátím, praví Panovník Hospodin.
22 Sa’an nan kerubobi, tare da da’irori kusa da su, suka buɗe fikafikansu, ɗaukakar Allah kuwa tana a bisansu.
Tedy vznesli cherubínové křídla svá i kola s nimi, sláva pak Boha Izraelského nad nimi svrchu.
23 Ɗaukakar Ubangiji ta haura daga cikin birnin ta sauka a bisa dutse gabas da shi.
I odešla sláva Hospodinova z prostředku města, a stála na hoře, kteráž jest na východ městu.
24 Ruhu ya ɗaga ni sama ya kuma kawo ni ga masu zaman bauta a ƙasar Babilon cikin wahayin da Ruhun Allah ya bayar. Sa’an nan wahayin da na gani ya rabu da ni,
Duch pak vznesl mne, a zase mne přivedl do země Kaldejské k zajatým, u vidění skrze Ducha Božího. I odešlo ode mne vidění, kteréž jsem viděl.
25 na kuwa faɗa wa masu zaman bautan dukan abin da Ubangiji ya nuna mini.
A mluvil jsem k zajatým všecky ty věci Hospodinovy, kteréž mi ukázal.

< Ezekiyel 11 >