< Ezekiyel 10 >
1 Na duba, sai na ga kamannin kursiyin saffaya a kan sararin da yake a bisa kawunan kerubobi.
Och jag såg, och si, på himmelen, ofvan Cherubims hufvud, var lika som en saphir, och ofvanpå honom var lika som en stol.
2 Sai Ubangiji ya ce wa mutumin da yake saye da lilin, “Ka shiga cikin da’irorin da suke ƙarƙashin kerubobi. Ka cika hannuwanka da garwashin wuta wanda yake tsakanin kerubobin ka kuma watsar da su a kan birnin.” Yayinda nake dubawa, sai ya shiga.
Och han sade till den mannen i linnkläden: Gack in emellan hjulen under Cherub, och tag händerna fulla med glödande kol, som emellan Cherubim äro, och strö dem öfver staden; och han gick in, så att jag såg då han der ingick.
3 Kerubobin kuwa suna tsaye a gefen kudu na haikali sa’ad da mutumin ya shiga, sai girgije ya cika filin da yake can ciki.
Men Cherubim stod på högra sidone i husena och gården vardt innantill full med töckno.
4 Sai ɗaukakar Ubangiji ya tashi daga bisa kerubobi ya tafi zuwa madogarar ƙofar haikali. Girgijen ya cika haikali, filin kuwa ya cika da hasken ɗaukakar Ubangiji.
Och Herrans härlighet reste sig upp af Cherub, allt intill huströskelen, och huset vardt fullt med töckno, och gården full med sken af Herrans härlighet.
5 Sai aka ji ƙarar fikafikan kerubobin har a filin waje, kamar muryar Allah Maɗaukaki sa’ad da ya yi magana.
Och man hörde vingarna af Cherubim döna, allt ut uppå gården, lika som allsmägtigs Guds röst, då han talar.
6 Sa’ad da Ubangiji ya umarci mutumin da yake saye da lilin cewa, “Ka ɗibi wuta daga cikin tsakanin da’irorin, daga tsakanin kerubobin,” sai mutumin ya shiga ya tsaya kusa da da’irar.
Och då han hade budit mannenom i de linna kläden, och sagt: Tag eld emellan hjulen under Cherubim; gick han derin, och trädde intill hjulet.
7 Sa’an nan ɗaya daga cikin kerubobin ya miƙa hannu zuwa wurin wutar da take tsakaninsu. Ya ɗebo wutar daga ciki ya zuba a hannuwan mutumin da yake saye da lilin, shi kuwa ya karɓa ya fita.
Och Cherub räckte ut sina hand emellan Cherubim till elden, som var emellan Cherubim, tog deraf, och fick mannenom i linnklädomen i händerna; han tog dervid, och gick ut.
8 (A ƙarƙashin fikafikan kerubobin ana iya ganin abin da ya yi kamar hannuwan mutum.)
Och det syntes på Cherubim, lika som ens menniskos hand under deras vingar.
9 Na duba, sai na ga kusa da kerubobin akwai da’irori huɗu, kowanne kusa da kerub guda; da’irorin suna ƙyalli kamar wani dutse mai daraja.
Och jag såg, och si, fyra hjul stodo när Cherubim, vid hvar Cherub ett hjul; och hjulen voro uppåseende lika som en turkos;
10 Game da kamanninsu kuwa, huɗu a cikinsu sun yi kama da juna; kowanne ya yi kamar da da’ira a cikin da’ira.
Och voro alla fyra, det ena såsom det andra, lika som ett hjul hade varit uti de andro.
11 Yayinda suke tafiya, sukan tafi kowane gefe huɗun da kerubobin suka nufa; da’irorin ba sa juyawa yayinda kerubobin suke tafiya. Kerubobin suka tafi kowane gefen da kan ya nufa, ba tare da juyawa ba sa’ad da suke tafiya.
När ett af dem gick så gingo de alla fyra, och de behöfde icke vända sig, när de gingo; utan hvart det främsta gick, dit gingo de efter, och behöfde intet vända sig;
12 Jikunansu gaba ɗaya, har da bayansu, hannuwansu da fikafikansu, sun cika gaba ɗaya da idanu, kamar yadda suke a da’irori huɗun.
Samt med deras hela kropp, rygg, händer och vingar; och hjulen voro full med ögon allt omkring på alla fyra hjulen.
13 Na ji ana kiran da’irorin “da’irorin guguwa.”
Och han kallade hjulen klot, så att jag det hörde.
14 Kowane daga kerubobin yana da fuskoki huɗu. Fuska ɗaya na kerub ne, na biyun fuskar mutum ne, na ukun fuskar zaki ne, na huɗun kuwa fuskar gaggafa ce.
Så voro der ock fyra ansigte; det första ansigtet var en Cherub, det andra var en menniska, det tredje ett lejon, det fjerde en örn;
15 Sai kerubobin suka tashi sama. Waɗannan ne halittu masu ran da na gani kusa da Kogin Kebar.
Och Cherubim sväfde i höjdene; det är rätt detsamma djuret, som jag såg vid den älfvena Chebar.
16 Sa’ad da kerubobin suka motsa, sai da’irorin da suke kusa da su su motsa; kuma sa’ad da kerubobin suka buɗe fikafikansu don su tashi daga ƙasa, da’irorin ba sa barin wurarensu.
När Cherubim gingo, så gingo ock hjulen när dem; och då Cherubim fläktade med vingarna, att de skulle lyfta sig upp ifrå jordene, så gingo ock hjulen intet ifrå dem.
17 Sa’ad da kerubobin suka tsaya cik, su ma sukan tsaya cik; kuma sa’ad da kerubobin suka tashi, sai su ma su tashi tare da su, domin ruhun rayayyun halittun yana a cikinsu.
När de stodo, så stodo desse ock; upplyfte de sig, så upplyfte ock desse sig; ty ett starkt väder var i dem.
18 Sai ɗaukakar Ubangiji ya tashi daga bisa madogarar ƙofar haikali ya kuma tsaya a bisa kerubobi.
Och Herrans härlighet gick återigen ifrå huströskelen, och satte sig ofvanpå Cherubim.
19 Yayinda nake duba, kerubobin suka buɗe fikafikansu suka kuma tashi daga ƙasa, yayinda suka tafi kuwa, da’irorin suka tafi tare da su. Suka tsaya a mashigin ƙofar gabas na gidan Ubangiji, ɗaukakar Allah na Isra’ila kuwa yana a kansu.
Då fläktade Cherubim med sina vingar, och upplyfte sig ifrå jordene för min ögon; och då de utgingo, gingo hjulen när dem, och de trädde uti dörrena af Herrans hus östantill, och Israels Guds härlighet var ofvanuppå dem.
20 Waɗannan ne rayayyun halittun da na gani a ƙarƙashin Allah na Isra’ila kusa da Kogin Kebar, na kuma gane cewa su kerubobi ne.
Detta är det djuret, som jag såg under Israels Gud, vid den älfvena Chebar, och förmärkte att det voro Cherubim.
21 Kowanne yana da fuskoki huɗu da fikafikai huɗu, a ƙarƙashin kuwa akwai wani abin da ya yi kamar hannuwan mutum.
Och hvartdera hade ju fyra ansigten, och fyra vingar, och under vingomen lika som menniskohänder.
22 Fuskokinsu suna da kamanni ɗaya da waɗanda na gani kusa da Kogin Kebar. Kowanne ya tafi kai tsaye sosai.
Deras ansigte var lika som jag dem såg vid älfvena Chebar; och de gingo rätt framåt.