< Ezekiyel 10 >

1 Na duba, sai na ga kamannin kursiyin saffaya a kan sararin da yake a bisa kawunan kerubobi.
Потом видех, и гле, на небу које беше над главама херувимима показа се над њима као камен сафир на очи као престо.
2 Sai Ubangiji ya ce wa mutumin da yake saye da lilin, “Ka shiga cikin da’irorin da suke ƙarƙashin kerubobi. Ka cika hannuwanka da garwashin wuta wanda yake tsakanin kerubobin ka kuma watsar da su a kan birnin.” Yayinda nake dubawa, sai ya shiga.
И проговори човеку обученом у платно, и рече: Уђи међу точкове под херувимима, и узми пуне прегршти жеравице између херувима и разаспи на град. И уђе на моје очи.
3 Kerubobin kuwa suna tsaye a gefen kudu na haikali sa’ad da mutumin ya shiga, sai girgije ya cika filin da yake can ciki.
А херувими стајаху с десне стране дома кад уђе човек, и облак напуни унутрашњи трем.
4 Sai ɗaukakar Ubangiji ya tashi daga bisa kerubobi ya tafi zuwa madogarar ƙofar haikali. Girgijen ya cika haikali, filin kuwa ya cika da hasken ɗaukakar Ubangiji.
И слава Господња подиже се с херувима на праг од дома, и напуни се дом облака, а трем се напуни светлости славе Господње.
5 Sai aka ji ƙarar fikafikan kerubobin har a filin waje, kamar muryar Allah Maɗaukaki sa’ad da ya yi magana.
И лупа крила у херувима чујаше се до спољашњег трема као глас Бога Свемогућег кад говори.
6 Sa’ad da Ubangiji ya umarci mutumin da yake saye da lilin cewa, “Ka ɗibi wuta daga cikin tsakanin da’irorin, daga tsakanin kerubobin,” sai mutumin ya shiga ya tsaya kusa da da’irar.
И кад заповеди човеку обученом у платно говорећи: Узми огња између точкова између херувима; он уђе и стаде код точкова.
7 Sa’an nan ɗaya daga cikin kerubobin ya miƙa hannu zuwa wurin wutar da take tsakaninsu. Ya ɗebo wutar daga ciki ya zuba a hannuwan mutumin da yake saye da lilin, shi kuwa ya karɓa ya fita.
И један херувим пружи руку своју између херувима к огњу који беше међу херувимима, и узе и метну у прегршти обученом у платно и он прими и изиђе.
8 (A ƙarƙashin fikafikan kerubobin ana iya ganin abin da ya yi kamar hannuwan mutum.)
А виђаше се у херувима као рука човечија под крилима.
9 Na duba, sai na ga kusa da kerubobin akwai da’irori huɗu, kowanne kusa da kerub guda; da’irorin suna ƙyalli kamar wani dutse mai daraja.
И видех, и гле, четири точка код херувима, по један точак код једног херувима, и точкови беху на очи као камен хрисолит.
10 Game da kamanninsu kuwa, huɗu a cikinsu sun yi kama da juna; kowanne ya yi kamar da da’ira a cikin da’ira.
И на очи беху сва четири точка једнака, и као да је точак у точку.
11 Yayinda suke tafiya, sukan tafi kowane gefe huɗun da kerubobin suka nufa; da’irorin ba sa juyawa yayinda kerubobin suke tafiya. Kerubobin suka tafi kowane gefen da kan ya nufa, ba tare da juyawa ba sa’ad da suke tafiya.
Кад иђаху, иђаху сва четири, сваки на своју страну, и идући не скретаху, него куда гледаше глава онамо иђаху и идући не скретаху.
12 Jikunansu gaba ɗaya, har da bayansu, hannuwansu da fikafikansu, sun cika gaba ɗaya da idanu, kamar yadda suke a da’irori huɗun.
А све им тело и леђа и руке и крила и точкови, сва четири точка њихова, беху пуна очију свуда унаоколо.
13 Na ji ana kiran da’irorin “da’irorin guguwa.”
А точкови се зваху како чух: кола.
14 Kowane daga kerubobin yana da fuskoki huɗu. Fuska ɗaya na kerub ne, na biyun fuskar mutum ne, na ukun fuskar zaki ne, na huɗun kuwa fuskar gaggafa ce.
А четири лица имаше свака животиња: једно лице херувимско, друго лице човечије и треће лице лавово и четврто лице орлово.
15 Sai kerubobin suka tashi sama. Waɗannan ne halittu masu ran da na gani kusa da Kogin Kebar.
И подигоше се херувими у вис; то беху исте животиње које видех на реци Хевару.
16 Sa’ad da kerubobin suka motsa, sai da’irorin da suke kusa da su su motsa; kuma sa’ad da kerubobin suka buɗe fikafikansu don su tashi daga ƙasa, da’irorin ba sa barin wurarensu.
А кад иђаху херувими, иђаху и точкови уз њих, и кад херувими махаху крилима својим да се подигну од земље, точкови се не одмицаху од њих.
17 Sa’ad da kerubobin suka tsaya cik, su ma sukan tsaya cik; kuma sa’ad da kerubobin suka tashi, sai su ma su tashi tare da su, domin ruhun rayayyun halittun yana a cikinsu.
Кад се они устављаху, устављаху се и точкови; а кад се они подизаху, подизаху се и точкови; јер беше дух животињски у њима.
18 Sai ɗaukakar Ubangiji ya tashi daga bisa madogarar ƙofar haikali ya kuma tsaya a bisa kerubobi.
И слава Господња отиде изнад прага од дома, и стаде над херувиме.
19 Yayinda nake duba, kerubobin suka buɗe fikafikansu suka kuma tashi daga ƙasa, yayinda suka tafi kuwa, da’irorin suka tafi tare da su. Suka tsaya a mashigin ƙofar gabas na gidan Ubangiji, ɗaukakar Allah na Isra’ila kuwa yana a kansu.
И херувими махнувши крилима подигоше се од земље преда мном полазећи, и точкови према њима; и стадоше на источним вратима дома Господњег, и слава Бога Израиљевог беше озго над њима.
20 Waɗannan ne rayayyun halittun da na gani a ƙarƙashin Allah na Isra’ila kusa da Kogin Kebar, na kuma gane cewa su kerubobi ne.
То беху исте животиње које видех под Богом Израиљевим на реци Хевару, и познах да су херувими.
21 Kowanne yana da fuskoki huɗu da fikafikai huɗu, a ƙarƙashin kuwa akwai wani abin da ya yi kamar hannuwan mutum.
Свака имаше четири лица и четири крила, и као рука човечија беше им под крилима.
22 Fuskokinsu suna da kamanni ɗaya da waɗanda na gani kusa da Kogin Kebar. Kowanne ya tafi kai tsaye sosai.
И лица им беху иста која видех на реци Хевару; обличја беху иста, исти беху; сваки иђаше право на према се.

< Ezekiyel 10 >