< Ezekiyel 10 >
1 Na duba, sai na ga kamannin kursiyin saffaya a kan sararin da yake a bisa kawunan kerubobi.
Et je vis, et voici que sur le firmament qui était au-dessus de la tête des Chérubins, il y avait comme une pierre de saphir; quelque chose paraissant ressembler à un trône apparut au-dessus d’eux.
2 Sai Ubangiji ya ce wa mutumin da yake saye da lilin, “Ka shiga cikin da’irorin da suke ƙarƙashin kerubobi. Ka cika hannuwanka da garwashin wuta wanda yake tsakanin kerubobin ka kuma watsar da su a kan birnin.” Yayinda nake dubawa, sai ya shiga.
Et il dit à l’homme vêtu de lin: « Va dans les intervalles des roues, sous les Chérubins; remplis tes mains de charbons ardents pris d’entre les Chérubins, et répands-les sur la ville. » Et il y alla devant mes yeux.
3 Kerubobin kuwa suna tsaye a gefen kudu na haikali sa’ad da mutumin ya shiga, sai girgije ya cika filin da yake can ciki.
Or les Chérubins se tenaient à droite de la maison quand l’homme y alla, et la nuée remplit le parvis intérieur.
4 Sai ɗaukakar Ubangiji ya tashi daga bisa kerubobi ya tafi zuwa madogarar ƙofar haikali. Girgijen ya cika haikali, filin kuwa ya cika da hasken ɗaukakar Ubangiji.
Et la gloire de Yahweh s’éleva de dessus les Chérubins et vint sur le seuil de la maison; la maison fut remplie de la nuée, et le parvis était plein de l’éclat de la gloire de Yahweh.
5 Sai aka ji ƙarar fikafikan kerubobin har a filin waje, kamar muryar Allah Maɗaukaki sa’ad da ya yi magana.
Le bruit des ailes des Chérubins se fit entendre jusqu’au parvis extérieur, comme la voix du Dieu tout-puissant quand il parle.
6 Sa’ad da Ubangiji ya umarci mutumin da yake saye da lilin cewa, “Ka ɗibi wuta daga cikin tsakanin da’irorin, daga tsakanin kerubobin,” sai mutumin ya shiga ya tsaya kusa da da’irar.
Quand il eut donné cet ordre à l’homme vêtu de lin: « Prends du feu dans l’intervalle des roues, entre les Chérubins, » l’homme vint se tenir à côté des roues.
7 Sa’an nan ɗaya daga cikin kerubobin ya miƙa hannu zuwa wurin wutar da take tsakaninsu. Ya ɗebo wutar daga ciki ya zuba a hannuwan mutumin da yake saye da lilin, shi kuwa ya karɓa ya fita.
Et le Chérubin avança la main entre les Chérubins, vers le feu qui était entre les Chérubins; il en prit et le mit dans les mains de l’homme vêtu de lin, qui le prit et sortit.
8 (A ƙarƙashin fikafikan kerubobin ana iya ganin abin da ya yi kamar hannuwan mutum.)
Or on voyait aux Chérubins une forme de main d’homme sous leurs ailes.
9 Na duba, sai na ga kusa da kerubobin akwai da’irori huɗu, kowanne kusa da kerub guda; da’irorin suna ƙyalli kamar wani dutse mai daraja.
Et je vis, et voici quatre roues auprès des Chérubins, une roue à côté de chaque Chérubin, et l’aspect des roues était comme celui de la pierre de Tharsis.
10 Game da kamanninsu kuwa, huɗu a cikinsu sun yi kama da juna; kowanne ya yi kamar da da’ira a cikin da’ira.
Et quant à leur aspect, toutes quatre étaient semblables, comme si une roue était au milieu d’une autre roue.
11 Yayinda suke tafiya, sukan tafi kowane gefe huɗun da kerubobin suka nufa; da’irorin ba sa juyawa yayinda kerubobin suke tafiya. Kerubobin suka tafi kowane gefen da kan ya nufa, ba tare da juyawa ba sa’ad da suke tafiya.
En avançant, elles allaient sur leurs quatre côtés, et ne se retournaient pas dans leur marche; car vers le lieu où se tournait la tête elles allaient, et elles ne se retournaient pas dans leur marche.
12 Jikunansu gaba ɗaya, har da bayansu, hannuwansu da fikafikansu, sun cika gaba ɗaya da idanu, kamar yadda suke a da’irori huɗun.
Et tout le corps des Chérubins, leur dos, leurs mains et leurs ailes, ainsi que les roues, étaient remplies d’yeux tout autour; tous les quatre avaient leurs roues.
13 Na ji ana kiran da’irorin “da’irorin guguwa.”
Quant aux roues, on les appelait « agiles. »
14 Kowane daga kerubobin yana da fuskoki huɗu. Fuska ɗaya na kerub ne, na biyun fuskar mutum ne, na ukun fuskar zaki ne, na huɗun kuwa fuskar gaggafa ce.
Chacun des Chérubins avait quatre faces: la face du premier était la face de chérubin; la face du second était une face d’homme; celle du troisième, une face de taureau, et celle du quatrième, une face d’aigle.
15 Sai kerubobin suka tashi sama. Waɗannan ne halittu masu ran da na gani kusa da Kogin Kebar.
Et les chérubins s’élevèrent; c’était l’être vivant que j’avais vu au fleuve Chobar.
16 Sa’ad da kerubobin suka motsa, sai da’irorin da suke kusa da su su motsa; kuma sa’ad da kerubobin suka buɗe fikafikansu don su tashi daga ƙasa, da’irorin ba sa barin wurarensu.
Quand les Chérubins allaient, les roues allaient aussi à côté d’eux; et quand les Chérubins dressaient leurs ailes pour s’élever de terre, les roues ne se détournaient pas, elles non plus, d’à côté d’eux.
17 Sa’ad da kerubobin suka tsaya cik, su ma sukan tsaya cik; kuma sa’ad da kerubobin suka tashi, sai su ma su tashi tare da su, domin ruhun rayayyun halittun yana a cikinsu.
Quand ils s’arrêtaient, elles s’arrêtaient; quand ils s’élevaient, elles s’élevaient avec eux; car l’Esprit de l’être vivant était en elles.
18 Sai ɗaukakar Ubangiji ya tashi daga bisa madogarar ƙofar haikali ya kuma tsaya a bisa kerubobi.
La gloire de Yahweh se retira de dessus le seuil de la maison et s’arrêta sur les Chérubins.
19 Yayinda nake duba, kerubobin suka buɗe fikafikansu suka kuma tashi daga ƙasa, yayinda suka tafi kuwa, da’irorin suka tafi tare da su. Suka tsaya a mashigin ƙofar gabas na gidan Ubangiji, ɗaukakar Allah na Isra’ila kuwa yana a kansu.
Les Chérubins dressèrent leurs ailes et s’élevèrent de terre à mes yeux, quand ils partirent et les roues avec eux. Ils s’arrêtèrent à l’entrée de la porte orientale de la maison de Yahweh; et la gloire du Dieu d’Israël reposait sur eux par-dessus.
20 Waɗannan ne rayayyun halittun da na gani a ƙarƙashin Allah na Isra’ila kusa da Kogin Kebar, na kuma gane cewa su kerubobi ne.
C’était l’être vivant que j’avais vu au-dessous du Dieu d’Israël, au fleuve Chobar; et je sus que c’étaient des Chérubins.
21 Kowanne yana da fuskoki huɗu da fikafikai huɗu, a ƙarƙashin kuwa akwai wani abin da ya yi kamar hannuwan mutum.
Chacun avait quatre faces et chacun avait quatre ailes, et une ressemblance de mains d’hommes était sous leurs ailes.
22 Fuskokinsu suna da kamanni ɗaya da waɗanda na gani kusa da Kogin Kebar. Kowanne ya tafi kai tsaye sosai.
Et quant à la ressemblance de leurs faces, c’étaient les faces que j’avais vues près du fleuve Chobar; c’était le même aspect, c’étaient eux-mêmes. Chacun allait droit devant soi.