< Ezekiyel 10 >
1 Na duba, sai na ga kamannin kursiyin saffaya a kan sararin da yake a bisa kawunan kerubobi.
Then looking, I saw that on the arch which was over the head of the winged ones there was seen over them what seemed like a sapphire stone, having the form of a king's seat.
2 Sai Ubangiji ya ce wa mutumin da yake saye da lilin, “Ka shiga cikin da’irorin da suke ƙarƙashin kerubobi. Ka cika hannuwanka da garwashin wuta wanda yake tsakanin kerubobin ka kuma watsar da su a kan birnin.” Yayinda nake dubawa, sai ya shiga.
And he said to the man clothed in linen, Go in between the wheels, under the winged ones, and get your two hands full of burning coals from between the winged ones and send them in a shower over the town. And he went in before my eyes.
3 Kerubobin kuwa suna tsaye a gefen kudu na haikali sa’ad da mutumin ya shiga, sai girgije ya cika filin da yake can ciki.
Now the winged ones were stationed on the right side of the house when the man went in; and the inner square was full of the cloud.
4 Sai ɗaukakar Ubangiji ya tashi daga bisa kerubobi ya tafi zuwa madogarar ƙofar haikali. Girgijen ya cika haikali, filin kuwa ya cika da hasken ɗaukakar Ubangiji.
And the glory of the Lord went up from the winged ones and came to rest over the doorstep of the house; and the house was full of the cloud and the open square was full of the shining of the Lord's glory.
5 Sai aka ji ƙarar fikafikan kerubobin har a filin waje, kamar muryar Allah Maɗaukaki sa’ad da ya yi magana.
And the sound of the wings of the winged ones was clear even in the outer square, like the voice of the Ruler of all.
6 Sa’ad da Ubangiji ya umarci mutumin da yake saye da lilin cewa, “Ka ɗibi wuta daga cikin tsakanin da’irorin, daga tsakanin kerubobin,” sai mutumin ya shiga ya tsaya kusa da da’irar.
And when he gave orders to the man clothed in linen, saying, Take fire from between the wheels, from between the winged ones, then he went in and took his place at the side of a wheel.
7 Sa’an nan ɗaya daga cikin kerubobin ya miƙa hannu zuwa wurin wutar da take tsakaninsu. Ya ɗebo wutar daga ciki ya zuba a hannuwan mutumin da yake saye da lilin, shi kuwa ya karɓa ya fita.
And stretching out his hand to the fire which was between the winged ones, he took some of it and went out.
8 (A ƙarƙashin fikafikan kerubobin ana iya ganin abin da ya yi kamar hannuwan mutum.)
And I saw the form of a man's hands among the winged ones under their wings.
9 Na duba, sai na ga kusa da kerubobin akwai da’irori huɗu, kowanne kusa da kerub guda; da’irorin suna ƙyalli kamar wani dutse mai daraja.
And looking, I saw four wheels by the side of the winged ones, one wheel by the side of a winged one and another wheel by the side of another: and the wheels were like the colour of a beryl stone to the eye.
10 Game da kamanninsu kuwa, huɗu a cikinsu sun yi kama da juna; kowanne ya yi kamar da da’ira a cikin da’ira.
In form the four of them were all the same, they seemed like a wheel inside a wheel.
11 Yayinda suke tafiya, sukan tafi kowane gefe huɗun da kerubobin suka nufa; da’irorin ba sa juyawa yayinda kerubobin suke tafiya. Kerubobin suka tafi kowane gefen da kan ya nufa, ba tare da juyawa ba sa’ad da suke tafiya.
When they were moving, they went on their four sides without turning; they went after the head in the direction in which it was looking; they went without turning.
12 Jikunansu gaba ɗaya, har da bayansu, hannuwansu da fikafikansu, sun cika gaba ɗaya da idanu, kamar yadda suke a da’irori huɗun.
And the edges of the four wheels were full of eyes round about.
13 Na ji ana kiran da’irorin “da’irorin guguwa.”
As for the wheels, they were named in my hearing, the circling wheels.
14 Kowane daga kerubobin yana da fuskoki huɗu. Fuska ɗaya na kerub ne, na biyun fuskar mutum ne, na ukun fuskar zaki ne, na huɗun kuwa fuskar gaggafa ce.
And every one had four faces: the first face was the face of a winged one, and the second was the face of a man, and the third the face of a lion, and the fourth the face of an eagle.
15 Sai kerubobin suka tashi sama. Waɗannan ne halittu masu ran da na gani kusa da Kogin Kebar.
And the winged ones went up on high: this is the living being which I saw by the river Chebar.
16 Sa’ad da kerubobin suka motsa, sai da’irorin da suke kusa da su su motsa; kuma sa’ad da kerubobin suka buɗe fikafikansu don su tashi daga ƙasa, da’irorin ba sa barin wurarensu.
And when the winged ones went, the wheels went by their side: and when their wings were lifted to take them up from the earth, the wheels were not turned from their side.
17 Sa’ad da kerubobin suka tsaya cik, su ma sukan tsaya cik; kuma sa’ad da kerubobin suka tashi, sai su ma su tashi tare da su, domin ruhun rayayyun halittun yana a cikinsu.
When they were at rest in their place, these were at rest; when they were lifted up, these went up with them: for the spirit of life was in them.
18 Sai ɗaukakar Ubangiji ya tashi daga bisa madogarar ƙofar haikali ya kuma tsaya a bisa kerubobi.
Then the glory of the Lord went out from the doorstep of the house, and came to rest over the winged ones.
19 Yayinda nake duba, kerubobin suka buɗe fikafikansu suka kuma tashi daga ƙasa, yayinda suka tafi kuwa, da’irorin suka tafi tare da su. Suka tsaya a mashigin ƙofar gabas na gidan Ubangiji, ɗaukakar Allah na Isra’ila kuwa yana a kansu.
And the winged ones, lifting up their wings, went up from the earth before my eyes, with the wheels by their side: and they came to rest at the east doorway of the Lord's house; and the glory of the God of Israel was over them on high.
20 Waɗannan ne rayayyun halittun da na gani a ƙarƙashin Allah na Isra’ila kusa da Kogin Kebar, na kuma gane cewa su kerubobi ne.
This is the living being which I saw under the God of Israel by the river Chebar; and it was clear to me that they were the winged ones.
21 Kowanne yana da fuskoki huɗu da fikafikai huɗu, a ƙarƙashin kuwa akwai wani abin da ya yi kamar hannuwan mutum.
Every one had four faces and every one had four wings; and hands like a man's hands were under their wings.
22 Fuskokinsu suna da kamanni ɗaya da waɗanda na gani kusa da Kogin Kebar. Kowanne ya tafi kai tsaye sosai.
As for the form of their faces, they were the faces whose form I saw by the river Chebar; when they went, every one of them went straight forward.