< Fitowa 1 >

1 Waɗannan su ne sunayen’ya’yan Isra’ila maza, waɗanda suka tafi Masar tare da Yaƙub; kowanne da iyalinsa.
NOW THESE are the names of the sons of Israel, who came into Egypt with Jacob; every man came with his household:
2 Ruben, Simeyon, Lawi da Yahuda;
Reuben, Simeon, Levi, and Judah;
3 Issakar, Zebulun da Benyamin;
Issachar, Zebulun, and Benjamin;
4 Dan da Naftali; Gad da Asher.
Dan and Naphtali, Gad and Asher.
5 Zuriyar Yaƙub duka sun kai mutum saba’in. Yusuf ya riga ya kasance a Masar.
And all the souls that came out of the loins of Jacob were seventy souls; and Joseph was in Egypt already.
6 Yanzu Yusuf da dukan’yan’uwansa da kuma dukan tsaran nan da suka tafi Masar, sun mutu,
And Joseph died, and all his brethren, and all that generation.
7 amma Isra’ilawa sun riɓaɓɓanya, suka kuma yi ta haihuwa sosai, suka yi yawan sosai, har ƙasar ta cika da su.
And the children of Israel were fruitful, and increased abundantly, and multiplied, and waxed exceeding mighty; and the land was filled with them.
8 Sai wani sabon sarki wanda bai san Yusuf ba, ya hau sarautar Masar.
Now there arose a new king over Egypt, who knew not Joseph.
9 Ya ce wa mutanensa, “Duba Isra’ilawa sun yi yawa, sun fi ƙarfinmu.
And he said unto his people: 'Behold, the people of the children of Israel are too many and too mighty for us;
10 Ku zo, mu yi dabara a kansu, in ba haka ba za su ƙaru fiye da haka, in kuwa yaƙi ya tashi tsakaninmu da abokan gāba, za su iya haɗa kai da abokan gāba, su yaƙe mu, su bar ƙasar.”
come, let us deal wisely with them, lest they multiply, and it come to pass, that, when there befalleth us any war, they also join themselves unto our enemies, and fight against us, and get them up out of the land.'
11 Saboda haka sai suka naɗa shugabannin gandu a kansu don su wahalshe su, su kuma bauta musu, suka sa su suka gina biranen Fitom da Rameses su zama biranen ajiya, domin Fir’auna.
Therefore they did set over them taskmasters to afflict them with their burdens. And they built for Pharaoh store-cities, Pithom and Raamses.
12 Amma duk da wannan ƙarin wulaƙancin da ake yi musu, su kuwa sai daɗa riɓaɓɓanya suke ta yi. Sai tsoron Isra’ilawa ya ƙaru a zuciyar Masarawa,
But the more they afflicted them, the more they multiplied and the more they spread abroad. And they were adread because of the children of Israel.
13 ganin haka sai Masarawa suka ƙara musu wahala.
And the Egyptians made the children of Israel to serve with rigour.
14 Suka baƙanta wa Isra’ilawa rai da bauta mai wuya, ta wurin sa su yin tubali da yumɓu, da kuma kowace irin bauta a gonaki. A cikin dukan ayyukansu, Masarawa ba su ji tausayinsu ba ko kaɗan.
And they made their lives bitter with hard service, in mortar and in brick, and in all manner of service in the field; in all their service, wherein they made them serve with rigour.
15 Sai Sarkin Masar ya gaya wa ungozomomin matan Ibraniyawa, wato, su Shofra da Fuwa ya ce,
And the king of Egypt spoke to the Hebrew midwives, of whom the name of the one was Shiphrah, and the name of the other Puah;
16 “Sa’ad da kuke taimakon matan Ibraniyawa lokacin haihuwa, in jaririn namiji ne ku kashe shi, amma in ta mace ce, ku bar ta da rai.”
and he said: 'When ye do the office of a midwife to the Hebrew women, ye shall look upon the birthstool: if it be a son, then ye shall kill him; but if it be a daughter, then she shall live.'
17 Amma ungozomomin nan masu tsoron Allah ne, ba su kuwa aikata abin da sarkin Masar ya gaya musu ba; suka bar jarirai maza su rayu.
But the midwives feared God, and did not as the king of Egypt commanded them, but saved the men-children alive.
18 Sai sarkin Masar ya kira ungozomomin, ya tambaye su ya ce, “Don me kuka yi haka? Don me kuka bar jarirai maza su rayu?”
And the king of Egypt called for the midwives, and said unto them: 'Why have ye done this thing, and have saved the men-children alive?'
19 Ungozoman suka amsa wa Fir’auna suka ce, “Ai, matan Ibraniyawa ba kamar matan Masarawa ba ne, gwarzaye ne, sukan haihu kafin ungozomomin su kai wurinsu.”
And the midwives said unto Pharaoh: 'Because the Hebrew women are not as the Egyptian women; for they are lively, and are delivered ere the midwife come unto them.'
20 Saboda haka Allah ya nuna alheri wa ungozomomin, Isra’ilawa kuwa suka yi yawa fiye da dā.
And God dealt well with the midwives; and the people multiplied, and waxed very mighty.
21 Saboda ungozomomin suna tsoron Allah, sai Allah ya ba su iyalan kansu.
And it came to pass, because the midwives feared God, that He made them houses.
22 Sai Fir’auna ya ba da umarni wa mutanensa ya ce, “Duk yaron da yake namijin da haka haifa, dole ku jefa shi cikin kogi, amma ku bar yara mata su rayu.”
And Pharaoh charged all his people, saying: 'Every son that is born ye shall cast into the river, and every daughter ye shall save alive.'

< Fitowa 1 >