< Fitowa 1 >

1 Waɗannan su ne sunayen’ya’yan Isra’ila maza, waɗanda suka tafi Masar tare da Yaƙub; kowanne da iyalinsa.
These are the names of the sons of Israel, who went into Egypt with Jacob. They entered, each one with his house:
2 Ruben, Simeyon, Lawi da Yahuda;
Reuben, Simeon, Levi, Judah,
3 Issakar, Zebulun da Benyamin;
Issachar, Zebulun, and Benjamin,
4 Dan da Naftali; Gad da Asher.
Dan and Naphtali, Gad and Asher.
5 Zuriyar Yaƙub duka sun kai mutum saba’in. Yusuf ya riga ya kasance a Masar.
Therefore, all the souls of those who went forth from Jacob’s thigh were seventy. Now Joseph was in Egypt.
6 Yanzu Yusuf da dukan’yan’uwansa da kuma dukan tsaran nan da suka tafi Masar, sun mutu,
When he had died, along with all of his brothers and all of that generation,
7 amma Isra’ilawa sun riɓaɓɓanya, suka kuma yi ta haihuwa sosai, suka yi yawan sosai, har ƙasar ta cika da su.
the sons of Israel increased, and they multiplied like seedlings. And having been strengthened exceedingly, they filled the land.
8 Sai wani sabon sarki wanda bai san Yusuf ba, ya hau sarautar Masar.
Meanwhile, there arose a new king over Egypt, who was ignorant of Joseph.
9 Ya ce wa mutanensa, “Duba Isra’ilawa sun yi yawa, sun fi ƙarfinmu.
And he said to his people: “Behold, the people of the sons of Israel are many, and they are stronger than we are.
10 Ku zo, mu yi dabara a kansu, in ba haka ba za su ƙaru fiye da haka, in kuwa yaƙi ya tashi tsakaninmu da abokan gāba, za su iya haɗa kai da abokan gāba, su yaƙe mu, su bar ƙasar.”
Come, let us wisely oppress them, lest they multiply; and if any war should advance against us, they may be added to our enemies, and having fought against us, they might depart from the land.”
11 Saboda haka sai suka naɗa shugabannin gandu a kansu don su wahalshe su, su kuma bauta musu, suka sa su suka gina biranen Fitom da Rameses su zama biranen ajiya, domin Fir’auna.
And so he set over them masters of the works, in order to afflict them with burdens. And they built for Pharaoh the cities of the tabernacles: Pithom and Raamses.
12 Amma duk da wannan ƙarin wulaƙancin da ake yi musu, su kuwa sai daɗa riɓaɓɓanya suke ta yi. Sai tsoron Isra’ilawa ya ƙaru a zuciyar Masarawa,
And the more they oppressed them, so much more did they multiply and increase.
13 ganin haka sai Masarawa suka ƙara musu wahala.
And the Egyptians hated the sons of Israel, and they afflicted them and mocked them.
14 Suka baƙanta wa Isra’ilawa rai da bauta mai wuya, ta wurin sa su yin tubali da yumɓu, da kuma kowace irin bauta a gonaki. A cikin dukan ayyukansu, Masarawa ba su ji tausayinsu ba ko kaɗan.
And they led their life directly into bitterness, with hard work in clay and brick, and with all kinds of servitude, so that they were being overwhelmed with the works of the land.
15 Sai Sarkin Masar ya gaya wa ungozomomin matan Ibraniyawa, wato, su Shofra da Fuwa ya ce,
Then the king of Egypt spoke to the midwives of the Hebrews, (one of whom one was called Shiphrah, another Puah)
16 “Sa’ad da kuke taimakon matan Ibraniyawa lokacin haihuwa, in jaririn namiji ne ku kashe shi, amma in ta mace ce, ku bar ta da rai.”
instructing them: “When you will act as a midwife to the Hebrew women, and the time of delivery has arrived: if it is male, put it to death; if it is female, retain it.”
17 Amma ungozomomin nan masu tsoron Allah ne, ba su kuwa aikata abin da sarkin Masar ya gaya musu ba; suka bar jarirai maza su rayu.
But the midwives feared God, and so they did not act according to the precept of the king of Egypt, but they kept the males safe.
18 Sai sarkin Masar ya kira ungozomomin, ya tambaye su ya ce, “Don me kuka yi haka? Don me kuka bar jarirai maza su rayu?”
And summoning them, the king said, “What did you intend to do, so that you would save the boys?”
19 Ungozoman suka amsa wa Fir’auna suka ce, “Ai, matan Ibraniyawa ba kamar matan Masarawa ba ne, gwarzaye ne, sukan haihu kafin ungozomomin su kai wurinsu.”
They responded: “The Hebrew women are not like the Egyptian women. For they themselves have the wisdom of a midwife, and so they give birth before we can come to them.”
20 Saboda haka Allah ya nuna alheri wa ungozomomin, Isra’ilawa kuwa suka yi yawa fiye da dā.
Therefore, God acted favorably toward the midwives. And the people increased, and they were strengthened exceedingly.
21 Saboda ungozomomin suna tsoron Allah, sai Allah ya ba su iyalan kansu.
And because the midwives feared God, he built houses for them.
22 Sai Fir’auna ya ba da umarni wa mutanensa ya ce, “Duk yaron da yake namijin da haka haifa, dole ku jefa shi cikin kogi, amma ku bar yara mata su rayu.”
Therefore, Pharaoh instructed all his people, saying: “Whatever will be born of the male sex, cast it into the river; whatever will be born of the female sex, retain it.”

< Fitowa 1 >