< Fitowa 9 >
1 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka je wurin Fir’auna ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji Allah na Ibraniyawa ya ce, “Ka bar mutanena su tafi, domin su yi mini sujada.”
RAB Musa'ya şöyle dedi: “Firavunun yanına git ve ona de ki, ‘İbraniler'in Tanrısı RAB şöyle diyor: Halkımı salıver, bana tapsınlar.
2 In ka ƙi ka bar su su tafi, kana ta riƙonsu,
Salıvermeyi reddeder, onları tutmakta diretirsen,
3 hannun Ubangiji zai kawo muguwar annoba a kan dabbobinka a gona, a kan dawakanka, da jakuna da raƙuma, da kuma a kan shanunka da tumaki da awaki.
RAB'bin eli kırlardaki hayvanlarınızı –atları, eşekleri, develeri, sığırları, davarları– büyük kırıma uğratarak sizi cezalandıracak.
4 Amma Ubangiji zai raba tsakanin dabbobin Isra’ila da na Masar, saboda kada wata dabbar Isra’ilawa ta mutu.’”
RAB İsrailliler'le Mısırlılar'ın hayvanlarına farklı davranacak. İsrailliler'in hayvanlarından hiçbiri ölmeyecek.’”
5 Sai Ubangiji ya sa lokaci ya ce, “Gobe Ubangiji zai yi wannan a ƙasar.”
RAB zamanı da belirleyerek, “Yarın ülkede bunu yapacağım” dedi.
6 Kashegari Ubangiji ya yi haka. Dukan dabbobin Masarawa suka mutu, amma babu dabba guda ta Isra’ilawan da ta mutu.
Ertesi gün RAB dediğini yaptı: Mısırlılar'ın hayvanları büyük çapta öldü. Ama İsrailliler'in hayvanlarından hiçbiri ölmedi.
7 Fir’auna ya aiki mutane su bincika, sai suka tarar babu dabba guda ta Isra’ilawan da ta mutu. Duk da haka zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa bar mutanen su tafi ba.
Firavun adam gönderdi, İsrailliler'in bir tek hayvanının bile ölmediğini öğrendi. Öyleyken, inat etti ve halkı salıvermedi.
8 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna, “Ɗibi tokar matoya cike da tafin hannuwanku, Musa kuwa zai watsa tokar sama a gaban Fir’auna.
RAB Musa'yla Harun'a, “Yanınıza iki avuç dolusu ocak kurumu alın” dedi, “Musa kurumu firavunun önünde göğe doğru savursun.
9 Za tă zama ƙura bisa dukan ƙasar Masar, sai marurai masu zafi su fiffito bisa mutane da dabbobi a dukan ƙasar.”
Kurum bütün Mısır'ın üzerinde ince bir toza dönüşecek; ülkenin her yanındaki insanların, hayvanların bedenlerinde irinli çıbanlar çıkacak.”
10 Sai suka ɗibi tokar matoya, suka tsaya a gaban Fir’auna, Musa ya watsa ta a iska, sai marurai masu zafi suka fiffito bisa mutane da dabbobi.
Böylece Musa'yla Harun ocak kurumu alıp firavunun önünde durdular. Musa kurumu göğe doğru savurdu. İnsanlarda ve hayvanlarda irinli çıbanlar çıktı.
11 Bokaye suka kāsa tsayawa a gaban Musa saboda maruran da suke bisansu da a kan dukan Masarawa.
Büyücüler çıbandan ötürü Musa'nın karşısında duramaz oldular. Çünkü bütün Mısırlılar'da olduğu gibi onlarda da çıbanlar çıkmıştı.
12 Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, bai kuwa saurare Musa da Haruna ba kamar yadda Ubangiji ya riga ya ce wa Musa.
RAB firavunu inatçı yaptı, RAB'bin Musa'ya söylediği gibi, firavun Musa'yla Harun'u dinlemedi.
13 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Tashi da sassafe, ka sadu da Fir’auna, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Ibraniyawa ya ce, Ka bar mutanena su tafi don su yi mini sujada,
RAB Musa'ya şöyle dedi: “Sabah erkenden kalkıp firavunun huzuruna çık, de ki, ‘İbraniler'in Tanrısı RAB şöyle diyor: Halkımı salıver, bana tapsınlar.
14 ko kuwa a wannan lokaci zan aika da cikakkiyar annoba mai ƙarfi a kanka da a kan fadawanka da mutanenka, domin ka san cewa ba kama da ni a dukan duniya.
Yoksa bu kez senin, görevlilerinin, halkının üzerine bütün belalarımı yağdıracağım. Öyle ki, bu dünyada benim gibisi olmadığını öğrenesin.
15 Gama da ni kaina na miƙa hannuna na buge ka da jama’arka da annoba, ai, da an hallaka ku a duniya ƙaƙaf.
Çünkü elimi kaldırıp seni ve halkını salgın hastalıkla vurmuş olsaydım, yeryüzünden silinmiş olurdun.
16 Amma na bar ka ka rayu domin in nuna maka ikona, domin kuma sunana yă zama abin darajantawa a dukan duniya.
Gücümü sana göstermek, adımı bütün dünyaya tanıtmak için seni ayakta tuttum.
17 Har yanzu kana gāba da mutanena, ba ka kuma bar su su tafi ba.
Hâlâ halkımı salıvermiyor, onlara üstünlük taslıyorsun.
18 Saboda haka, gobe war haka, zan sa a yi ƙanƙara mai tsananin gaske, irin wadda Masar ba tă taɓa gani ba tun kahuwarta, har yă zuwa yanzu.
Bu yüzden, yarın bu saatlerde Mısır'a tarihinde görülmemiş ağır bir dolu yağdıracağım.
19 Yanzu, ka ba da umarni a dawo da shanunku da kuma kome da kuke da shi wanda yake a gona zuwa gida, gama ƙanƙarar za tă kashe kowane mutum ko dabba wadda take a gona wadda ba a kawo cikin gida ba, sa’ad da ta fāɗo.’”
Şimdi buyruk ver, hayvanların ve kırda neyin varsa hepsi sığınaklara konsun. Dolu yağınca, eve getirilmeyen, kırda kalan bütün insanlarla hayvanlar ölecek.’”
20 Waɗansu daga cikin dattawan Fir’auna suka cika da tsoro saboda abin da Ubangiji ya faɗa, nan da nan suka shigo da dabbobinsu da bayinsu da sauri daga gona zuwa cikin gida.
Firavunun görevlileri arasında RAB'bin uyarısından korkanlar köleleriyle hayvanlarını çabucak evlerine getirdiler.
21 Amma waɗanda ba su kula da maganar Ubangiji ba, suka bar bayinsu da dabbobi a gona.
RAB'bin uyarısını önemsemeyenler ise köleleriyle hayvanlarını tarlada bıraktı.
22 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka sama don a yi ƙanƙara a bisa dukan Masar, a bisa mutane da dabbobi, da bisa dukan abubuwan da suke girma a gonakin Masar.”
RAB Musa'ya, “Elini göğe doğru uzat” dedi, “Mısır'ın her yerine, insanların, hayvanların, kırdaki bütün bitkilerin üzerine dolu yağsın.”
23 Da Musa ya miƙa sandansa sama, sai Ubangiji ya aiko da tsawa da ƙanƙara, da walƙiya har ƙasa. Ta haka Ubangiji ya yi ruwan ƙanƙara a bisa ƙasar Masar;
Musa değneğini göğe doğru uzatınca RAB gök gürlemeleri ve dolu gönderdi. Yıldırım düştü. RAB Mısır'a dolu yağdırdı.
24 ƙanƙara ta fāɗo, walƙiya kuma tana ta wulƙawa. Wannan ce ƙanƙara mafi munin da aka taɓa yi, a dukan ƙasar Masar, tun tarihin kahuwarta na zaman al’umma.
Şiddetli dolu yağıyor, sürekli şimşek çakıyordu. Mısır Mısır olalı böylesi bir dolu görmemişti.
25 Ko’ina a Masar ƙanƙara ta bugi duk abin da yake a gonaki, mutane da dabbobi, ta bugi duk ganyaye da suke a gonaki, ta kuma ragargaza kowane itace.
Dolu Mısır'da insandan hayvana dek kırdaki her şeyi, bütün bitkileri mahvetti, bütün ağaçları kırdı.
26 Wuri guda kaɗai da ba a yi ruwan ƙanƙara ba, shi ne yankin Goshen, inda Isra’ilawa suke.
Yalnız İsrailliler'in yaşadığı Goşen bölgesine dolu düşmedi.
27 Sai Fir’auna ya aika a kira Musa da Haruna. Ya ce musu, “A wannan karo na yi zunubi. Ubangiji, shi ne da gaskiya, ni da mutane mu ke da kuskure.
Firavun Musa'yla Harun'u çağırtarak, “Bu kez günah işledim” dedi, “RAB haklı, ben ve halkım haksızız.
28 Ku roƙi Ubangiji, yă tsai da tsawar da ƙanƙarar. Ni kuwa na yi alkawari zan bar ku ku tafi, ba za ku ƙara tsayawa a nan ba.”
RAB'be dua edin, yeter bu gök gürlemeleri ve dolu. Sizi salıvereceğim, artık burada kalmayacaksınız.”
29 Musa ya amsa, “To, da kyau, da zarar na fita daga birnin, zan yi addu’a ga Ubangiji, tsawar za tă tsaya, ƙanƙarar kuma za tă daina, don ku sani cewa duniya ta Ubangiji ce.
Musa, “Kentten çıkınca, ellerimi RAB'be uzatacağım” dedi, “Gök gürlemeleri duracak, artık dolu yağmayacak. Böylece dünyanın RAB'be ait olduğunu bileceksin.
30 Amma na san cewa kai da fadawanka, har wa yau ba ku ji tsoron Ubangiji Allah ba tukuna.”
Ama biliyorum, sen ve görevlilerin RAB Tanrı'dan hâlâ korkmuyorsunuz.”
31 (Rama da sha’ir suka lalace, gama sha’ir ya riga ya nuna, rama kuwa tana fid da kai.
Keten ve arpa mahvolmuştu; çünkü arpa başak vermiş, keten çiçek açmıştı.
32 Alkama da gero kam, ba a hallaka su ba, gama lokacin nunansu bai yi ba tukuna.)
Ama buğday ve kızıl buğday henüz bitmediği için zarar görmemişti.
33 Sai Musa ya tashi daga gaban Fir’auna, ya fita daga birni. Da ya miƙa hannuwansa ta wajen Ubangiji, sai tsawa da ƙanƙara suka tsaya, kwararowar ruwa kuma ta ɗauke.
Musa firavunun yanından ayrılıp kentten çıktı. Ellerini RAB'be uzattı. Gök gürlemesi ve dolu durdu, yağmur dindi.
34 Da Fir’auna ya ga cewa ruwa da ƙanƙara da tsawa sun daina, sai ya sāke yin zunubi. Shi da fadawansa, suka taurare zukatansu.
Firavun yağmurun, dolunun, gök gürlemesinin kesildiğini görünce, yine günah işledi. Hem kendisi, hem görevlileri inat ettiler.
35 Ta haka zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa bar Isra’ilawa suka tafi ba, kamar yadda Ubangiji ya riga ya faɗa ta wurin Musa.
RAB'bin Musa aracılığıyla söylediği gibi, firavun inat ederek İsrailliler'i salıvermedi.