< Fitowa 9 >

1 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka je wurin Fir’auna ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji Allah na Ibraniyawa ya ce, “Ka bar mutanena su tafi, domin su yi mini sujada.”
Og Herren sa til Moses: Gå inn til Farao og si til ham: Så sier Herren, hebreernes Gud: La mitt folk fare, så de kan tjene mig!
2 In ka ƙi ka bar su su tafi, kana ta riƙonsu,
For dersom du nekter å la dem fare og fremdeles holder på dem,
3 hannun Ubangiji zai kawo muguwar annoba a kan dabbobinka a gona, a kan dawakanka, da jakuna da raƙuma, da kuma a kan shanunka da tumaki da awaki.
da skal Herrens hånd komme over ditt fe på marken, over hestene, over asenene, over kamelene, over storfeet og over småfeet med en forferdelig pest.
4 Amma Ubangiji zai raba tsakanin dabbobin Isra’ila da na Masar, saboda kada wata dabbar Isra’ilawa ta mutu.’”
Men Herren skal gjøre forskjell på Israels fe og egypternes fe, og det skal ikke dø noget av alt det som hører Israels barn til.
5 Sai Ubangiji ya sa lokaci ya ce, “Gobe Ubangiji zai yi wannan a ƙasar.”
Og Herren fastsatte tiden og sa: Imorgen vil Herren la dette skje i landet.
6 Kashegari Ubangiji ya yi haka. Dukan dabbobin Masarawa suka mutu, amma babu dabba guda ta Isra’ilawan da ta mutu.
Dagen efter gjorde Herren som han hadde sagt, og alt egypternes fe døde, men av Israels barns fe døde ikke ett liv.
7 Fir’auna ya aiki mutane su bincika, sai suka tarar babu dabba guda ta Isra’ilawan da ta mutu. Duk da haka zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa bar mutanen su tafi ba.
Og Farao sendte bud, og da var det ikke død et eneste liv av Israels fe; men Faraos hjerte blev hårdt, og han lot ikke folket fare.
8 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna, “Ɗibi tokar matoya cike da tafin hannuwanku, Musa kuwa zai watsa tokar sama a gaban Fir’auna.
Da sa Herren til Moses og Aron: Ta hendene fulle av aske fra ovnen, og Moses skal kaste den op i været så Farao ser på det,
9 Za tă zama ƙura bisa dukan ƙasar Masar, sai marurai masu zafi su fiffito bisa mutane da dabbobi a dukan ƙasar.”
og den skal bli til støv utover hele Egyptens land, og den skal bli til bylder som bryter ut med blemmer, både på folk og fe i hele Egyptens land.
10 Sai suka ɗibi tokar matoya, suka tsaya a gaban Fir’auna, Musa ya watsa ta a iska, sai marurai masu zafi suka fiffito bisa mutane da dabbobi.
Så tok de asken fra ovnen og trådte frem for Farao, og Moses kastet den op i været; og det blev bylder som brøt ut med blemmer, både på folk og fe.
11 Bokaye suka kāsa tsayawa a gaban Musa saboda maruran da suke bisansu da a kan dukan Masarawa.
Og tegnsutleggerne kunde ikke holde stand mot Moses for byldenes skyld; for det var kommet bylder på tegnsutleggerne og på alle egypterne.
12 Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, bai kuwa saurare Musa da Haruna ba kamar yadda Ubangiji ya riga ya ce wa Musa.
Men Herren forherdet Faraos hjerte, så han ikke hørte på dem, således som Herren hadde sagt til Moses
13 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Tashi da sassafe, ka sadu da Fir’auna, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Ibraniyawa ya ce, Ka bar mutanena su tafi don su yi mini sujada,
Da sa Herren til Moses: Stå tidlig op imorgen, og tred frem for Farao og si til ham: Så sier Herren, hebreernes Gud: La mitt folk fare, så de kan tjene mig!
14 ko kuwa a wannan lokaci zan aika da cikakkiyar annoba mai ƙarfi a kanka da a kan fadawanka da mutanenka, domin ka san cewa ba kama da ni a dukan duniya.
For denne gang vil jeg sende alle mine plager over dig selv og over dine tjenere og ditt folk, forat du skal kjenne at ingen er som jeg på hele jorden.
15 Gama da ni kaina na miƙa hannuna na buge ka da jama’arka da annoba, ai, da an hallaka ku a duniya ƙaƙaf.
For nu hadde jeg allerede rakt ut min hånd og vilde slått dig og ditt folk med pesten, så du var blitt utslettet av jorden;
16 Amma na bar ka ka rayu domin in nuna maka ikona, domin kuma sunana yă zama abin darajantawa a dukan duniya.
men derfor lot jeg dig bli i live at jeg kunde vise dig min makt, og mitt navn kunde bli kunngjort over hele jorden.
17 Har yanzu kana gāba da mutanena, ba ka kuma bar su su tafi ba.
Ennu stiller du dig i veien for mitt folk og vil ikke la dem fare.
18 Saboda haka, gobe war haka, zan sa a yi ƙanƙara mai tsananin gaske, irin wadda Masar ba tă taɓa gani ba tun kahuwarta, har yă zuwa yanzu.
Se, jeg vil på denne tid imorgen sende et forferdelig haglvær, som det aldri har vært make til i Egypten, like fra den dag det blev til, og til nu.
19 Yanzu, ka ba da umarni a dawo da shanunku da kuma kome da kuke da shi wanda yake a gona zuwa gida, gama ƙanƙarar za tă kashe kowane mutum ko dabba wadda take a gona wadda ba a kawo cikin gida ba, sa’ad da ta fāɗo.’”
Så send da folk og berg din buskap og alt det du har på marken! Alt folk og alt fe som er ute på marken og ikke har kommet sig i hus, på dem skal haglet falle, og de skal dø.
20 Waɗansu daga cikin dattawan Fir’auna suka cika da tsoro saboda abin da Ubangiji ya faɗa, nan da nan suka shigo da dabbobinsu da bayinsu da sauri daga gona zuwa cikin gida.
De av Faraos tjenere som fryktet Herrens ord, berget da sine folk og sin buskap i hus;
21 Amma waɗanda ba su kula da maganar Ubangiji ba, suka bar bayinsu da dabbobi a gona.
men de som ikke gav akt på Herrens ord, lot sine folk og sin buskap bli ute på marken.
22 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka sama don a yi ƙanƙara a bisa dukan Masar, a bisa mutane da dabbobi, da bisa dukan abubuwan da suke girma a gonakin Masar.”
Da sa Herren til Moses: Rekk din hånd op mot himmelen, og det skal komme hagl i hele Egyptens land, både over folk og fe og over alle markens urter i Egyptens land.
23 Da Musa ya miƙa sandansa sama, sai Ubangiji ya aiko da tsawa da ƙanƙara, da walƙiya har ƙasa. Ta haka Ubangiji ya yi ruwan ƙanƙara a bisa ƙasar Masar;
Og Moses rakte sin stav op mot himmelen, og Herren lot komme torden og hagl, og det fôr ild ned på jorden, og Herren lot falle hagl over Egyptens land.
24 ƙanƙara ta fāɗo, walƙiya kuma tana ta wulƙawa. Wannan ce ƙanƙara mafi munin da aka taɓa yi, a dukan ƙasar Masar, tun tarihin kahuwarta na zaman al’umma.
Det kom hagl, og midt i haglskuren lyn i lyn, et uvær så svært at det aldri hadde vært maken i hele Egyptens land fra den tid folk hadde bosatt sig der.
25 Ko’ina a Masar ƙanƙara ta bugi duk abin da yake a gonaki, mutane da dabbobi, ta bugi duk ganyaye da suke a gonaki, ta kuma ragargaza kowane itace.
Og i hele Egyptens land slo haglet ned alt det som var på marken, både folk og fe; og alle markens urter slo haglet ned, og alle markens trær brøt det sønder.
26 Wuri guda kaɗai da ba a yi ruwan ƙanƙara ba, shi ne yankin Goshen, inda Isra’ilawa suke.
Bare i Gosens land, hvor Israels barn bodde, falt det ikke hagl.
27 Sai Fir’auna ya aika a kira Musa da Haruna. Ya ce musu, “A wannan karo na yi zunubi. Ubangiji, shi ne da gaskiya, ni da mutane mu ke da kuskure.
Da sendte Farao bud efter Moses og Aron og sa til dem: Denne gang har jeg syndet; Herren er den som har rett, og jeg og mitt folk har urett.
28 Ku roƙi Ubangiji, yă tsai da tsawar da ƙanƙarar. Ni kuwa na yi alkawari zan bar ku ku tafi, ba za ku ƙara tsayawa a nan ba.”
Bed til Herren at det nu må være nok av hans torden og hagl! Så vil jeg la eder fare, og I skal ikke bie lenger.
29 Musa ya amsa, “To, da kyau, da zarar na fita daga birnin, zan yi addu’a ga Ubangiji, tsawar za tă tsaya, ƙanƙarar kuma za tă daina, don ku sani cewa duniya ta Ubangiji ce.
Moses svarte ham: Så snart jeg kommer ut av byen, vil jeg utbrede mine hender til Herren; så skal tordenen holde op og haglet ikke falle mere, forat du skal kjenne at jorden hører Herren til.
30 Amma na san cewa kai da fadawanka, har wa yau ba ku ji tsoron Ubangiji Allah ba tukuna.”
Men om dig og dine tjenere vet jeg at I ennu ikke frykter for Gud Herren.
31 (Rama da sha’ir suka lalace, gama sha’ir ya riga ya nuna, rama kuwa tana fid da kai.
Lin og bygg var slått ned; for bygget stod i aks og linet i knopp;
32 Alkama da gero kam, ba a hallaka su ba, gama lokacin nunansu bai yi ba tukuna.)
men hvete og spelt var ikke slått ned, for de kommer senere.
33 Sai Musa ya tashi daga gaban Fir’auna, ya fita daga birni. Da ya miƙa hannuwansa ta wajen Ubangiji, sai tsawa da ƙanƙara suka tsaya, kwararowar ruwa kuma ta ɗauke.
Og Moses gikk bort fra Farao og ut av byen og utbredte sine hender til Herren; da holdt tordenen og haglet op, og regnet strømmet ikke mere ned på jorden.
34 Da Fir’auna ya ga cewa ruwa da ƙanƙara da tsawa sun daina, sai ya sāke yin zunubi. Shi da fadawansa, suka taurare zukatansu.
Men da Farao så at regnet og haglet og tordenen hadde holdt op, blev han ved å synde, og han forherdet sitt hjerte, både han og hans tjenere.
35 Ta haka zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa bar Isra’ilawa suka tafi ba, kamar yadda Ubangiji ya riga ya faɗa ta wurin Musa.
Faraos hjerte var og blev forherdet, og han lot ikke Israels barn fare, således som Herren hadde sagt ved Moses.

< Fitowa 9 >