< Fitowa 9 >

1 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka je wurin Fir’auna ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji Allah na Ibraniyawa ya ce, “Ka bar mutanena su tafi, domin su yi mini sujada.”
UThixo wasesithi kuMosi, “Yana kuFaro uthi kuye, ‘Nanku okutshiwo nguThixo, uNkulunkulu wamaHebheru, ukuthi, “Yekela abantu bami bahambe, ukuze bayengikhonza.”
2 In ka ƙi ka bar su su tafi, kana ta riƙonsu,
Ungabalela ukuthi bahambe ube ulokhu ubabambile
3 hannun Ubangiji zai kawo muguwar annoba a kan dabbobinka a gona, a kan dawakanka, da jakuna da raƙuma, da kuma a kan shanunka da tumaki da awaki.
uThixo uzakwehlisela isifo esibi ezifuyweni zakho emadlelweni, amabhiza enu, obabhemi, amakamela, inkomo, izimvu lembuzi.
4 Amma Ubangiji zai raba tsakanin dabbobin Isra’ila da na Masar, saboda kada wata dabbar Isra’ilawa ta mutu.’”
Kodwa uThixo uzakwenza umahluko phakathi kwezifuyo zabako-Israyeli lezamaGibhithe ukuze kungafi lasinye isifuyo sabako-Israyeli.’”
5 Sai Ubangiji ya sa lokaci ya ce, “Gobe Ubangiji zai yi wannan a ƙasar.”
UThixo wamisa isikhathi esithile wathi, “uThixo uzakwenza lokhu kusasa elizweni leli.”
6 Kashegari Ubangiji ya yi haka. Dukan dabbobin Masarawa suka mutu, amma babu dabba guda ta Isra’ilawan da ta mutu.
Lakanye ngelanga elilandelayo uThixo wakwenza, zonke izifuyo zamaGibhithe zafa, kodwa akufanga ngitsho lasinye isifuyo sabako-Israyeli.
7 Fir’auna ya aiki mutane su bincika, sai suka tarar babu dabba guda ta Isra’ilawan da ta mutu. Duk da haka zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa bar mutanen su tafi ba.
UFaro wathuma amadoda ukuyahlola umonakalo afumana ukuthi kwakungafanga sifuyo lasinye sabako-Israyeli. Kodwa inhliziyo yakhe yala ilokhu ilukhuni, wabalela abantu ukuthi bahambe.
8 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna, “Ɗibi tokar matoya cike da tafin hannuwanku, Musa kuwa zai watsa tokar sama a gaban Fir’auna.
UThixo wasesithi kuMosi lo-Aroni, “Thathani umlotha omlutshwana eziko lifike kuFaro uMosi awuhazele emoyeni phambi kwakhe.
9 Za tă zama ƙura bisa dukan ƙasar Masar, sai marurai masu zafi su fiffito bisa mutane da dabbobi a dukan ƙasar.”
Uzakuba luthuli phezu kwelizwe lonke laseGibhithe, lapho-ke kuzaphihlika amathumba amabi ebantwini lasezinyamazaneni kulolonke ilizwe.”
10 Sai suka ɗibi tokar matoya, suka tsaya a gaban Fir’auna, Musa ya watsa ta a iska, sai marurai masu zafi suka fiffito bisa mutane da dabbobi.
Ngakho bathatha umlotha eziko baya kuFaro. UMosi wawuhazela emoyeni, abantu bonke lezinyamazana zonke kwamilwa ngamathumba aphihlikayo.
11 Bokaye suka kāsa tsayawa a gaban Musa saboda maruran da suke bisansu da a kan dukan Masarawa.
Izangoma zehluleka ukumisana loMosi ngenxa yamathumba ayezibulala kanye lamaGibhithe wonke.
12 Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, bai kuwa saurare Musa da Haruna ba kamar yadda Ubangiji ya riga ya ce wa Musa.
Kodwa uThixo wenza yaba lukhuni inhliziyo kaFaro wala ukulalela uMosi lo-Aroni njengoba uThixo wayevele etshilo kuMosi.
13 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Tashi da sassafe, ka sadu da Fir’auna, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Ibraniyawa ya ce, Ka bar mutanena su tafi don su yi mini sujada,
UThixo wasesithi kuMosi, “Vuka ekuseni kakhulu uye kuFaro, uthi kuye, ‘Nanku okutshiwo nguThixo, uNkulunkulu wamaHebheru, uthi, yekela abantu bami bahambe ukuze bayengikhonza.
14 ko kuwa a wannan lokaci zan aika da cikakkiyar annoba mai ƙarfi a kanka da a kan fadawanka da mutanenka, domin ka san cewa ba kama da ni a dukan duniya.
Kungenjalo kulesisikhathi ngizakwehlisa ubunzima bezinhlupho zami obulesihluku phezu kwakho, phezu kwezinceku zakho labantu bakho ukuze lazi ukuthi kakho omunye onjengami emhlabeni wonke.
15 Gama da ni kaina na miƙa hannuna na buge ka da jama’arka da annoba, ai, da an hallaka ku a duniya ƙaƙaf.
Kunje nje ngabe sengiselulile isandla sami ngakutshaya kanye labantu bakho ngesifo ebesizakucitsha emhlabeni.
16 Amma na bar ka ka rayu domin in nuna maka ikona, domin kuma sunana yă zama abin darajantawa a dukan duniya.
Kodwa ngikuphephisile ngayonale injongo yokuthi ngikubonise amandla ami, lokuthi ibizo lami lifakazwe kuwo wonke umhlaba.
17 Har yanzu kana gāba da mutanena, ba ka kuma bar su su tafi ba.
Ulokhu utshingela abantu bami ubalela ukuthi bahambe.
18 Saboda haka, gobe war haka, zan sa a yi ƙanƙara mai tsananin gaske, irin wadda Masar ba tă taɓa gani ba tun kahuwarta, har yă zuwa yanzu.
Ngalokho-ke ngalesisikhathi kusasa ngizakwehlisa isiqhotho esingakaze sehlele eGibhithe lilokhu lababala laba khona ilizwe leli.
19 Yanzu, ka ba da umarni a dawo da shanunku da kuma kome da kuke da shi wanda yake a gona zuwa gida, gama ƙanƙarar za tă kashe kowane mutum ko dabba wadda take a gona wadda ba a kawo cikin gida ba, sa’ad da ta fāɗo.’”
Wohle nje uthumezele ilizwi lokuthi izifuyo zakho lakho konke olakho emadlelweni kubuyiswe kuvalelwe esibayeni esivikelweyo ngoba isiqhotho leso sizatshaya umuntu wonke lesifuyo sonke esingabuthwanga nxa silokhu sisegangeni, konke kuzakufa.’”
20 Waɗansu daga cikin dattawan Fir’auna suka cika da tsoro saboda abin da Ubangiji ya faɗa, nan da nan suka shigo da dabbobinsu da bayinsu da sauri daga gona zuwa cikin gida.
Lezozikhulu zikaFaro ezalesabayo ilizwi likaThixo zaphanga zangenisa izigqili zazo lezifuyo ngaphakathi.
21 Amma waɗanda ba su kula da maganar Ubangiji ba, suka bar bayinsu da dabbobi a gona.
Labo abangalinanzanga ilizwi likaThixo izigqili zabo lezifuyo zabo bakuyekela kusegangeni.
22 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka sama don a yi ƙanƙara a bisa dukan Masar, a bisa mutane da dabbobi, da bisa dukan abubuwan da suke girma a gonakin Masar.”
UThixo wasesithi kuMosi, “Yelula isandla sakho siye phezulu ukuze kune isiqhotho kulolonke iGibhithe, phezu kwabantu lezinyamazana laphezu kwakho konke okukhulayo emasimini aseGibhithe.”
23 Da Musa ya miƙa sandansa sama, sai Ubangiji ya aiko da tsawa da ƙanƙara, da walƙiya har ƙasa. Ta haka Ubangiji ya yi ruwan ƙanƙara a bisa ƙasar Masar;
UMosi wonela ukukhomba ngentonga yakhe phezulu, uThixo wehlisa umdumo lesiqhotho, umbane wabaneka phansi emhlabathini. Ngakho uThixo wanisa isiqhotho elizweni laseGibhithe.
24 ƙanƙara ta fāɗo, walƙiya kuma tana ta wulƙawa. Wannan ce ƙanƙara mafi munin da aka taɓa yi, a dukan ƙasar Masar, tun tarihin kahuwarta na zaman al’umma.
Isiqhotho satshaya umbane wabaneka yonke indawo. Sasingakaze sibe khona isiphepho esinjalo sekulokhu isizwe saseGibhithe saba khona.
25 Ko’ina a Masar ƙanƙara ta bugi duk abin da yake a gonaki, mutane da dabbobi, ta bugi duk ganyaye da suke a gonaki, ta kuma ragargaza kowane itace.
Isiqhotho satshaya saqothula yonke into egangeni, abantu lezinyamazana; sabhuqa konke okukhulayo emasimini, saphundla izihlahla zonke eGibhithe.
26 Wuri guda kaɗai da ba a yi ruwan ƙanƙara ba, shi ne yankin Goshen, inda Isra’ilawa suke.
Indawo eyasilayo yiGosheni lapho okwakulabako-Israyeli khona.
27 Sai Fir’auna ya aika a kira Musa da Haruna. Ya ce musu, “A wannan karo na yi zunubi. Ubangiji, shi ne da gaskiya, ni da mutane mu ke da kuskure.
UFaro wasebiza uMosi lo-Aroni. Wathi kubo, “Okwamanje ngenze isono. UThixo ulungile, kukanti mina labantu bami siyizoni.
28 Ku roƙi Ubangiji, yă tsai da tsawar da ƙanƙarar. Ni kuwa na yi alkawari zan bar ku ku tafi, ba za ku ƙara tsayawa a nan ba.”
Khulekani kuThixo, ngoba ukukhwaza kwezulu lesiqhotho sekwanele. Ngizaliyekela lihambe; akusadingeki ukuthi lihlale.”
29 Musa ya amsa, “To, da kyau, da zarar na fita daga birnin, zan yi addu’a ga Ubangiji, tsawar za tă tsaya, ƙanƙarar kuma za tă daina, don ku sani cewa duniya ta Ubangiji ce.
UMosi waphendula wathi. “Nxa sengiphumile edolobheni ngizavula izandla zami ngikhuleke kuThixo. Ukuduma kuzakhawula kungabe kusaba lesiqhotho, ukuze wazi ukuthi umhlaba ngokaThixo.
30 Amma na san cewa kai da fadawanka, har wa yau ba ku ji tsoron Ubangiji Allah ba tukuna.”
Kodwa ngiyazi ukuthi wena lezikhulu zakho lilokhu lingamesabi uThixo uNkulunkulu.”
31 (Rama da sha’ir suka lalace, gama sha’ir ya riga ya nuna, rama kuwa tana fid da kai.
(Amabele lebhali kwabhuqwa nya ngoba amabele ayeselezikhwebu lophoko selumumethe.
32 Alkama da gero kam, ba a hallaka su ba, gama lokacin nunansu bai yi ba tukuna.)
Ingqoloyi lenyawuthi khona kakuthintwanga ngoba kuvuthwa muva.)
33 Sai Musa ya tashi daga gaban Fir’auna, ya fita daga birni. Da ya miƙa hannuwansa ta wajen Ubangiji, sai tsawa da ƙanƙara suka tsaya, kwararowar ruwa kuma ta ɗauke.
UMosi wasesuka kuFaro waphuma edolobheni. Welulela izandla zakhe kuThixo; ukuduma kwezulu lesiqhotho kwakhawula, izulu alabe lisana emhlabeni.
34 Da Fir’auna ya ga cewa ruwa da ƙanƙara da tsawa sun daina, sai ya sāke yin zunubi. Shi da fadawansa, suka taurare zukatansu.
Kwathi uFaro ebona ukuthi izulu lesiqhotho lokukhwaza kwezulu kwasekukhawule waphinda wenza isono: Yena lezikhulu zakhe benza inhliziyo zabo zaba lukhuni.
35 Ta haka zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa bar Isra’ilawa suka tafi ba, kamar yadda Ubangiji ya riga ya faɗa ta wurin Musa.
Ngakho inhliziyo kaFaro yaba lukhuni akaze avumela abako-Israyeli ukuthi bahambe njengoba uThixo wayetshilo ngoMosi.

< Fitowa 9 >