< Fitowa 9 >

1 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka je wurin Fir’auna ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji Allah na Ibraniyawa ya ce, “Ka bar mutanena su tafi, domin su yi mini sujada.”
Derpå sagde HERREN til Moses: "Gå til Farao og sig til ham: Så siger HERREN, Hebræernes Gud: Lad mit Folk rejse, for at de kan dyrke mig!
2 In ka ƙi ka bar su su tafi, kana ta riƙonsu,
Men hvis du vægrer dig ved at lade dem rejse og bliver ved med at holde dem fast,
3 hannun Ubangiji zai kawo muguwar annoba a kan dabbobinka a gona, a kan dawakanka, da jakuna da raƙuma, da kuma a kan shanunka da tumaki da awaki.
se, da skal HERRENs Hånd komme over dit Kvæg på Marken, over Hestene, Æslerne og Kamelerne, Hornkvæget og Småkvæget med en såre forfærdelig Pest.
4 Amma Ubangiji zai raba tsakanin dabbobin Isra’ila da na Masar, saboda kada wata dabbar Isra’ilawa ta mutu.’”
Og HERREN skal sætte Skel mellem Israels Kvæget og Ægypterens Kvæg, så der ikke skal dø noget af, hvad der tilhører Israeliterne."
5 Sai Ubangiji ya sa lokaci ya ce, “Gobe Ubangiji zai yi wannan a ƙasar.”
Og HERREN satte en Tidsfrist, idet han sagde: "I Morgen skal HERREN lade dette ske i Landet."
6 Kashegari Ubangiji ya yi haka. Dukan dabbobin Masarawa suka mutu, amma babu dabba guda ta Isra’ilawan da ta mutu.
Den følgende Dag lod HERREN det så ske, og alt Ægypternes Kvæg døde, men af Israeliternes Kvæg døde ikke et eneste Dyr.
7 Fir’auna ya aiki mutane su bincika, sai suka tarar babu dabba guda ta Isra’ilawan da ta mutu. Duk da haka zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa bar mutanen su tafi ba.
Farao sendte da Bud, og se, ikke et eneste Dyr af Israeliternes Kvæg var dødt. Men Faraos Hjerte blev forhærdet, og han lod ikke Folket rejse.
8 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna, “Ɗibi tokar matoya cike da tafin hannuwanku, Musa kuwa zai watsa tokar sama a gaban Fir’auna.
Derpå sagde HERREN til Moses og Aron: "Tag begge eders Hænder fulde af Sod fra Smelteovnen, og Moses skal kaste det i Vejret i Faraos Påsyn!
9 Za tă zama ƙura bisa dukan ƙasar Masar, sai marurai masu zafi su fiffito bisa mutane da dabbobi a dukan ƙasar.”
Så skal det blive til en Støvsky over hele Ægypten og til Betændelse, der bryder ud i Bylder på Mennesker og Kvæg i hele Ægypten!"
10 Sai suka ɗibi tokar matoya, suka tsaya a gaban Fir’auna, Musa ya watsa ta a iska, sai marurai masu zafi suka fiffito bisa mutane da dabbobi.
Da tog de Sod fra Smelteovnen og trådte frem for Farao, og Moses kastede det i Vejret; og det blev til Betændelse, der brød ud i Bylder på Mennesker og Kvæg.
11 Bokaye suka kāsa tsayawa a gaban Musa saboda maruran da suke bisansu da a kan dukan Masarawa.
Og Koglerne kunde ikke holde Stand over for Moses på Grund af Betændelsen, thi Betændelsen angreb Koglerne såvel som alle de andre Ægyptere.
12 Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, bai kuwa saurare Musa da Haruna ba kamar yadda Ubangiji ya riga ya ce wa Musa.
Men HERREN forhærdede Faraos Hjerte, så han ikke hørte på dem, således som HERREN havde sagt til Moses.
13 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Tashi da sassafe, ka sadu da Fir’auna, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Ibraniyawa ya ce, Ka bar mutanena su tafi don su yi mini sujada,
Derpå sagde HERREN til Moses: "Træd i Morgen tidlig frem for Farao og sig til ham: Så siger HERREN, Hebræernes Gud: Lad mit Folk rejse, for at de kan dyrke mig!
14 ko kuwa a wannan lokaci zan aika da cikakkiyar annoba mai ƙarfi a kanka da a kan fadawanka da mutanenka, domin ka san cewa ba kama da ni a dukan duniya.
Thi denne Gang vil jeg sende alle mine Plager mod dig selv og mod dine Tjenere og dit Folk, for at du kan kende, at der er ingen som jeg på hele Jorden.
15 Gama da ni kaina na miƙa hannuna na buge ka da jama’arka da annoba, ai, da an hallaka ku a duniya ƙaƙaf.
Thi ellers havde jeg nu udrakt min Hånd for at ramme dig og dit Folk med Pest, så du blev udryddet fra Jordens Overflade;
16 Amma na bar ka ka rayu domin in nuna maka ikona, domin kuma sunana yă zama abin darajantawa a dukan duniya.
dog derfor har jeg ladet dig blive i Live for at vise dig min Magt, og for at mit Navn kan blive forkyndt på hele Jorden.
17 Har yanzu kana gāba da mutanena, ba ka kuma bar su su tafi ba.
Endnu stiller du dig i Vejen for mit Folk og vil ikke lade det rejse.
18 Saboda haka, gobe war haka, zan sa a yi ƙanƙara mai tsananin gaske, irin wadda Masar ba tă taɓa gani ba tun kahuwarta, har yă zuwa yanzu.
Se, jeg lader i Morgen ved denne Tid et frygteligt Haglvejr bryde løs, hvis Lige ikke har været i Ægypten, fra den Dag det blev til og indtil nu.
19 Yanzu, ka ba da umarni a dawo da shanunku da kuma kome da kuke da shi wanda yake a gona zuwa gida, gama ƙanƙarar za tă kashe kowane mutum ko dabba wadda take a gona wadda ba a kawo cikin gida ba, sa’ad da ta fāɗo.’”
Derfor må du sørge for at bringe dit Kvæg og alt, hvad du har på Marken, i Sikkerhed! Thi alle Mennesker og Dyr, der befinder sig på Marken og ikke er kommet under Tag, skal rammes af Haglen og omkomme."
20 Waɗansu daga cikin dattawan Fir’auna suka cika da tsoro saboda abin da Ubangiji ya faɗa, nan da nan suka shigo da dabbobinsu da bayinsu da sauri daga gona zuwa cikin gida.
De blandt Faraos Tjenere, der frygtede HERRENs Ord, bragte nu deres Trælle og Kvæg under Tag;
21 Amma waɗanda ba su kula da maganar Ubangiji ba, suka bar bayinsu da dabbobi a gona.
men de, der ikke lagde sig HERRENs Ord på Hjerte, lod deres Trælle og Kvæg blive ude på Marken.
22 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka sama don a yi ƙanƙara a bisa dukan Masar, a bisa mutane da dabbobi, da bisa dukan abubuwan da suke girma a gonakin Masar.”
Da sagde HERREN til Moses: "Ræk din Hånd op mod Himmelen, så skal der falde Hagl i hele Ægypten på Mennesker og Dyr og på alle Markens Urter i Ægypten!"
23 Da Musa ya miƙa sandansa sama, sai Ubangiji ya aiko da tsawa da ƙanƙara, da walƙiya har ƙasa. Ta haka Ubangiji ya yi ruwan ƙanƙara a bisa ƙasar Masar;
Da rakte Moses sin Stav op mod Himmelen, og HERREN sendte Torden og Hagl; Ild for ned mod Jorden, og HERREN lod Hagl falde over Ægypten;
24 ƙanƙara ta fāɗo, walƙiya kuma tana ta wulƙawa. Wannan ce ƙanƙara mafi munin da aka taɓa yi, a dukan ƙasar Masar, tun tarihin kahuwarta na zaman al’umma.
og der kom et Haglvejr, med Ildsluer flammende mellem Haglen, så voldsomt, at dets Lige aldrig havde været nogetsteds i Ægypten, siden det blev befolket;
25 Ko’ina a Masar ƙanƙara ta bugi duk abin da yake a gonaki, mutane da dabbobi, ta bugi duk ganyaye da suke a gonaki, ta kuma ragargaza kowane itace.
og i hele Ægypten slog Haglen alt ned, hvad der var på Marken, både Mennesker og Kvæg, og alle Markens Urter slog Haglen ned, og alle Markens Træer knækkede den;
26 Wuri guda kaɗai da ba a yi ruwan ƙanƙara ba, shi ne yankin Goshen, inda Isra’ilawa suke.
kun i Gosen, hvor Israeliterne boede, faldt der ikke Hagl.
27 Sai Fir’auna ya aika a kira Musa da Haruna. Ya ce musu, “A wannan karo na yi zunubi. Ubangiji, shi ne da gaskiya, ni da mutane mu ke da kuskure.
Da sendte Farao Bud efter Moses og Aron og sagde til dem: "Denne Gang har jeg syndet; HERREN har Ret, og jeg og mit Folk har Uret;
28 Ku roƙi Ubangiji, yă tsai da tsawar da ƙanƙarar. Ni kuwa na yi alkawari zan bar ku ku tafi, ba za ku ƙara tsayawa a nan ba.”
gå i Forbøn hos HERREN, at det nu må være nok med Guds Torden og Haglvejret, så vil jeg lade eder rejse, og I skal ikke blive længer!"
29 Musa ya amsa, “To, da kyau, da zarar na fita daga birnin, zan yi addu’a ga Ubangiji, tsawar za tă tsaya, ƙanƙarar kuma za tă daina, don ku sani cewa duniya ta Ubangiji ce.
Moses svarede ham: "Så snart jeg kommer ud af Byen, skal jeg udbrede mine Hænder mod HERREN; så skal Tordenen høre op, og Haglen skal ikke falde mere, for at du kan kende, at Jorden tilhører HERREN."
30 Amma na san cewa kai da fadawanka, har wa yau ba ku ji tsoron Ubangiji Allah ba tukuna.”
Dog, jeg ved, at du og dine Tjenere endnu ikke frygter for Gud HERREN."
31 (Rama da sha’ir suka lalace, gama sha’ir ya riga ya nuna, rama kuwa tana fid da kai.
Hørren og Byggen blev slået ned, thi Byggen stod i Aks, og Hørren i Blomst;
32 Alkama da gero kam, ba a hallaka su ba, gama lokacin nunansu bai yi ba tukuna.)
derimod blev Hveden og Spelten ikke slået ned, thi de modnes senere.
33 Sai Musa ya tashi daga gaban Fir’auna, ya fita daga birni. Da ya miƙa hannuwansa ta wajen Ubangiji, sai tsawa da ƙanƙara suka tsaya, kwararowar ruwa kuma ta ɗauke.
Da Moses var gået bort fra Farao og var kommet ud af Byen, udbredte han sine Hænder mod HERREN, og da hørte Tordenen og Haglen op, og Regnen strømmede ikke mere ned.
34 Da Fir’auna ya ga cewa ruwa da ƙanƙara da tsawa sun daina, sai ya sāke yin zunubi. Shi da fadawansa, suka taurare zukatansu.
Men da Farao så, at Regnen, Haglen og Tordenen var hørt op, fremturede han i sin Synd, og han og hans Tjenere forhærdede deres Hjerte.
35 Ta haka zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa bar Isra’ilawa suka tafi ba, kamar yadda Ubangiji ya riga ya faɗa ta wurin Musa.
Faraos Hjerte blev forhærdet, så at han ikke lod Israeliterne rejse, således som HERREN havde sagt ved Moses.

< Fitowa 9 >