< Fitowa 9 >

1 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka je wurin Fir’auna ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji Allah na Ibraniyawa ya ce, “Ka bar mutanena su tafi, domin su yi mini sujada.”
Og Herren sagde til Mose: Gak til Farao, og du skal sige til ham: Saa siger Herren, Hebræernes Gud: Lad mit Folk fare, at de kunne tjene mig.
2 In ka ƙi ka bar su su tafi, kana ta riƙonsu,
Thi dersom du vægrer dig ved at lade dem fare, og du fremdeles holder paa dem,
3 hannun Ubangiji zai kawo muguwar annoba a kan dabbobinka a gona, a kan dawakanka, da jakuna da raƙuma, da kuma a kan shanunka da tumaki da awaki.
se, da skal Herrens Haand komme over dit Kvæg, som er paa Marken, over Heste, over Asener, over Kameler, over Øksne og over smaat Kvæg, en saare svar Pest.
4 Amma Ubangiji zai raba tsakanin dabbobin Isra’ila da na Masar, saboda kada wata dabbar Isra’ilawa ta mutu.’”
Og Herren skal gøre Skilsmisse imellem Israels Kvæg og imellem Ægypternes Kvæg, og der skal intet dø af alt det, Israels Børn have.
5 Sai Ubangiji ya sa lokaci ya ce, “Gobe Ubangiji zai yi wannan a ƙasar.”
Og Herren satte en bestemt Tid og sagde: I Morgen skal Herren gøre denne Gerning i Landet.
6 Kashegari Ubangiji ya yi haka. Dukan dabbobin Masarawa suka mutu, amma babu dabba guda ta Isra’ilawan da ta mutu.
Og Herren gjorde denne Gerning den næste Dag, og alt Ægypternes Kvæg døde; men der døde ikke eet Stykke af Israels Børns Kvæg.
7 Fir’auna ya aiki mutane su bincika, sai suka tarar babu dabba guda ta Isra’ilawan da ta mutu. Duk da haka zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa bar mutanen su tafi ba.
Og Farao sendte Bud, og se, end ikke eet Stykke var død af Israels Kvæg; men Faraos Hjerte forhærdedes, og han lod ikke Folket fare.
8 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna, “Ɗibi tokar matoya cike da tafin hannuwanku, Musa kuwa zai watsa tokar sama a gaban Fir’auna.
Da sagde Herren til Mose og til Aron: Tager eders Næver fulde af Aske fra Ovnen, og Mose skal slaa den ud mod Himmelen for Faraos Øjne.
9 Za tă zama ƙura bisa dukan ƙasar Masar, sai marurai masu zafi su fiffito bisa mutane da dabbobi a dukan ƙasar.”
Og den skal vorde til Støv over alt Ægyptens Land, og det skal vorde til Bylder, som skal bryde ud med Blegner, paa Folket og paa Kvæget i alt Ægyptens Land.
10 Sai suka ɗibi tokar matoya, suka tsaya a gaban Fir’auna, Musa ya watsa ta a iska, sai marurai masu zafi suka fiffito bisa mutane da dabbobi.
Saa toge de Aske fra Ovnen og stode for Farao, og Mose slog den ud mod Himmelen; og der blev Bylder, som brød ud med Blegner, paa Folket og paa Kvæget.
11 Bokaye suka kāsa tsayawa a gaban Musa saboda maruran da suke bisansu da a kan dukan Masarawa.
Og Koglerne kunde ikke bestaa for Mose, formedelst Bylderne; thi der var Bylder paa Koglerne og paa alle Ægyptere.
12 Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, bai kuwa saurare Musa da Haruna ba kamar yadda Ubangiji ya riga ya ce wa Musa.
Men Herren forhærdede Faraos Hjerte, saa at han ikke hørte dem, som Herren havde sagt til Mose.
13 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Tashi da sassafe, ka sadu da Fir’auna, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Ibraniyawa ya ce, Ka bar mutanena su tafi don su yi mini sujada,
Da sagde Herren til Mose: Staa aarle op om Morgenen og stil dig for Farao og sig til ham: Saa siger Herren, Hebræernes Gud: Lad mit Folk fare, at de kunne tjene mig.
14 ko kuwa a wannan lokaci zan aika da cikakkiyar annoba mai ƙarfi a kanka da a kan fadawanka da mutanenka, domin ka san cewa ba kama da ni a dukan duniya.
Thi denne Gang vil jeg sende alle mine Plager, saa det gaar dig til Hjerte, baade paa dine Tjenere og paa dit Folk, at du skal fornemme, at der er ingen som jeg paa al Jorden.
15 Gama da ni kaina na miƙa hannuna na buge ka da jama’arka da annoba, ai, da an hallaka ku a duniya ƙaƙaf.
Thi havde jeg allerede udrakt min Haand og slaget dig og dit Folk med Pest, da havde du været udslettet af Jorden;
16 Amma na bar ka ka rayu domin in nuna maka ikona, domin kuma sunana yă zama abin darajantawa a dukan duniya.
men sandelig derfor har jeg ladet dig blive staaende, for at lade dig se min Magt, og for at mit Navn skal kundgøres i alle Lande.
17 Har yanzu kana gāba da mutanena, ba ka kuma bar su su tafi ba.
Ophøjer du dig endnu over mit Folk, saa at du ikke vil lade dem fare?
18 Saboda haka, gobe war haka, zan sa a yi ƙanƙara mai tsananin gaske, irin wadda Masar ba tă taɓa gani ba tun kahuwarta, har yă zuwa yanzu.
Se, jeg vil i Morgen paa denne Tid lade regne en saare svar Hagel, hvis Lige var aldrig før i Ægypten fra den Dag, det blev grundfæstet og hidindtil.
19 Yanzu, ka ba da umarni a dawo da shanunku da kuma kome da kuke da shi wanda yake a gona zuwa gida, gama ƙanƙarar za tă kashe kowane mutum ko dabba wadda take a gona wadda ba a kawo cikin gida ba, sa’ad da ta fāɗo.’”
Saa send nu hen, saml dit Kvæg og alt det, du har paa Marken; thi alle Mennesker og alt Kvæg, som findes paa Marken og ikke ere samlede i Hus, og som Hagelen slaar ned paa, skulle dø.
20 Waɗansu daga cikin dattawan Fir’auna suka cika da tsoro saboda abin da Ubangiji ya faɗa, nan da nan suka shigo da dabbobinsu da bayinsu da sauri daga gona zuwa cikin gida.
Hvo som da frygtede Herrens Ord blandt Faraos Tjenere, han lod sine Tjenere og sit Kvæg fly til Husene;
21 Amma waɗanda ba su kula da maganar Ubangiji ba, suka bar bayinsu da dabbobi a gona.
men hvo som ikke lagde Herrens Ord paa sit Hjerte, lod sine Tjenere og sit Kvæg blive paa Marken.
22 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka sama don a yi ƙanƙara a bisa dukan Masar, a bisa mutane da dabbobi, da bisa dukan abubuwan da suke girma a gonakin Masar.”
Da sagde Herren til Mose: Ræk din Haand op mod Himmelen, og der skal vorde Hagel over hele Ægyptens Land, over Mennesker og over Kvæg og over alle Urter paa Marken i Ægyptens Land.
23 Da Musa ya miƙa sandansa sama, sai Ubangiji ya aiko da tsawa da ƙanƙara, da walƙiya har ƙasa. Ta haka Ubangiji ya yi ruwan ƙanƙara a bisa ƙasar Masar;
Og Mose rakte sin Stav op mod Himmelen, og Herren lod tordne og hagle, og der for Ild ned paa Jorden; og Herren lod regne Hagel over Ægyptens Land.
24 ƙanƙara ta fāɗo, walƙiya kuma tana ta wulƙawa. Wannan ce ƙanƙara mafi munin da aka taɓa yi, a dukan ƙasar Masar, tun tarihin kahuwarta na zaman al’umma.
Og der blev Hagel og Ild, som slyngede sig midt i Hagelen, saare svar, saadan som ikke havde været i hele Ægyptens Land, fra den Tid det havde været et Folks Land.
25 Ko’ina a Masar ƙanƙara ta bugi duk abin da yake a gonaki, mutane da dabbobi, ta bugi duk ganyaye da suke a gonaki, ta kuma ragargaza kowane itace.
Og Hagelen nedslog i hele Ægyptens Land det, som var paa Marken, baade Mennesker og Kvæg; og alle Urter paa Marken slog Hagelen og knækkede alle Træer paa Marken.
26 Wuri guda kaɗai da ba a yi ruwan ƙanƙara ba, shi ne yankin Goshen, inda Isra’ilawa suke.
Alene i Gosen Land, hvor Israels Børn vare, faldt der ikke Hagel.
27 Sai Fir’auna ya aika a kira Musa da Haruna. Ya ce musu, “A wannan karo na yi zunubi. Ubangiji, shi ne da gaskiya, ni da mutane mu ke da kuskure.
Da sendte Farao hen og lod kalde ad Mose og Aron og sagde til dem: Jeg har syndet denne Gang; Herren er den retfærdige, men jeg og mit Folk ere de ugudelige.
28 Ku roƙi Ubangiji, yă tsai da tsawar da ƙanƙarar. Ni kuwa na yi alkawari zan bar ku ku tafi, ba za ku ƙara tsayawa a nan ba.”
Beder til Herren, at det maa være nok med den Guds Torden og Hagel, saa vil jeg lade eder fare, at I ikke skulle bie længere.
29 Musa ya amsa, “To, da kyau, da zarar na fita daga birnin, zan yi addu’a ga Ubangiji, tsawar za tă tsaya, ƙanƙarar kuma za tă daina, don ku sani cewa duniya ta Ubangiji ce.
Og Mose sagde til ham: Naar jeg kommer ud af Staden, da vil jeg udbrede mine Hænder til Herren, saa skal Tordenen høre op, og Hagelen skal ikke falde mere, at du skal fornemme, at Jorden hører Herren til.
30 Amma na san cewa kai da fadawanka, har wa yau ba ku ji tsoron Ubangiji Allah ba tukuna.”
Dog om dig og dine Tjenere ved jeg, at I endnu ikke frygte for den Herre Guds Ansigt.
31 (Rama da sha’ir suka lalace, gama sha’ir ya riga ya nuna, rama kuwa tana fid da kai.
Da blev baade Hør og Byg nedslaget; thi Bygget var skudt i Aks og Hørren i Knevler.
32 Alkama da gero kam, ba a hallaka su ba, gama lokacin nunansu bai yi ba tukuna.)
Men Hveden og Spelten bleve ikke nedslagne; thi de vare endnu ikke skredne.
33 Sai Musa ya tashi daga gaban Fir’auna, ya fita daga birni. Da ya miƙa hannuwansa ta wajen Ubangiji, sai tsawa da ƙanƙara suka tsaya, kwararowar ruwa kuma ta ɗauke.
Og Mose gik fra Farao ud af Staden og udbredte sine Hænder til Herren; saa lod det af at tordne og hagle, og Regnen blev ikke mere udøst paa Jorden.
34 Da Fir’auna ya ga cewa ruwa da ƙanƙara da tsawa sun daina, sai ya sāke yin zunubi. Shi da fadawansa, suka taurare zukatansu.
Der Farao saa, at det holdt op at regne og hagle og tordne, da syndede han endda; og han forhærdede sit Hjerte, han og hans Tjenere.
35 Ta haka zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa bar Isra’ilawa suka tafi ba, kamar yadda Ubangiji ya riga ya faɗa ta wurin Musa.
Saa blev Faraos Hjerte forhærdet, og han lod ikke Israels Børn fare, som Herren havde sagt ved Mose.

< Fitowa 9 >