< Fitowa 8 >
1 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka je wurin Fir’auna, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka bar mutanena su tafi domin su yi mini sujada.
Gospod je spregovoril Mojzesu: »Pojdi k faraonu in mu reci: ›Tako govori Gospod: ›Odpusti moje ljudstvo, da mi bodo lahko služili.‹‹
2 In ka ƙi barinsu, zan hore ka da annoban kwaɗi a dukan ƙasarka.
Če pa odkloniš, da jih odpustiš, glej, bom vse tvoje meje udaril z žabami.
3 Nilu zai cika da kwaɗi. Za su haura zuwa cikin fadanka da kan gadonka, cikin gidajen bayinka da kan mutanenka, cikin kwanonin toye-toyenka da na cin abincinka.
Reke bodo rodile žab v obilju, ki bodo šle gor in prišle v tvojo hišo, v tvojo spalnico, na tvojo posteljo, v hiše tvojih služabnikov, na tvoje ljudstvo, v tvoje peči in v tvoje nečke.
4 Kwaɗin nan za su yi ta tsalle a kanka, da kan mutanenka, da kuma kan dukan bayinka.’”
Žabe bodo prišle tako nate, kakor na tvoje ljudstvo in na vse tvoje služabnike.«
5 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ce wa Haruna, ‘Ka miƙa hannunka da sandanka bisa koguna da rafuffuka da kuma kududdufai, ka sa kwaɗi su fito su mamaye ƙasar Masar.’”
Gospod je spregovoril Mojzesu: »Reci Aronu: ›Iztegni svojo roko s svojo palico nad vodotoke, nad reke in nad ribnike ter povzroči žabam, da pridejo nad egiptovsko deželo.‹«
6 Sai Haruna ya miƙa hannunsa bisa ruwan Masar, kwaɗi kuwa suka fito, suka mamaye ƙasar Masar.
Aron je iztegnil svojo roko nad egiptovske vode in žabe so prišle gor ter pokrile egiptovsko deželo.
7 Amma bokaye ma suka yi abubuwan nan ta wurin sihirinsu; suka sa kwaɗi suka fito suka mamaye ƙasar Masar.
Čarovniki so tako storili s svojimi izrekanji urokov in nad egiptovsko deželo privedli žabe.
8 Fir’auna ya kira Musa da Haruna ya ce, “Yi addu’a ga Ubangiji yă ɗauke kwaɗi daga gare ni da mutanena, zan kuwa bar mutanenku su tafi su yi hadaya ga Ubangiji.”
Potem je faraon dal poklicati Mojzesa in Arona ter rekel: »Rotita Gospoda, da lahko odstrani žabe od mene in od mojega ljudstva; jaz pa bom pustil ljudstvu oditi, da bodo lahko žrtvovali Gospodu.«
9 Musa ya ce wa Fir’auna, “Na ba ka dama ka ba da lokacin da zan yi addu’a dominka da kuma bayinka da mutanenka, gidajenku kuwa za su rabu da kwaɗi, amma ban da waɗanda suke cikin Nilu.”
Mojzes je rekel faraonu: »Slava nad menoj. Kdaj naj rotim zate in za tvoje služabnike in za tvoje ljudstvo, da uniči žabe pred teboj in tvojimi hišami, da bodo lahko preostale samo v reki?«
10 Fir’auna ya ce, “Gobe.” Musa ya amsa, “Za a yi kamar yadda ka faɗa, domin ka sani babu wani kamar Ubangiji, Allahnmu.
Rekel je: »Jutri.« Rekel je: » To bodi glede na tvojo besedo, da lahko spoznaš, da ni nikogar podobnega Gospodu, našemu Bogu.
11 Kwaɗin za su bar ka da gidajenka, bayinka da mutanenka; za su kasance a Nilu ne kaɗai.”
Žabe bodo odšle od tebe in od tvojih hiš in od tvojih služabnikov in od tvojega ljudstva. Preostale bodo samo še v reki.«
12 Bayan Musa da Haruna sun bar Fir’auna, Sai Musa ya yi kuka ga Ubangiji saboda kwaɗin da ya kawo a bisa Fir’auna.
Mojzes in Aron sta odšla izpred faraona. Mojzes je klical h Gospodu zaradi žab, ki jih je privedel zoper faraona.
13 Sai Ubangiji ya yi abin da Musa ya nema. Kwaɗin suka mutu a gidaje, da filaye, da kuma gonaki.
Gospod je storil glede na Mojzesovo besedo in žabe so poginile po hišah, po vaseh in po poljih.
14 Aka jibga su tsibi-tsibi, ƙasar ta yi ɗoyi saboda su.
Zbrali so jih skupaj na kupe in dežela se je usmradila.
15 Amma da Fir’auna ya ga an sami sauƙi, sai ya taurare, ya ƙi yă saurari Musa da Haruna kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
Toda ko je faraon videl, da je bil predah, je zakrknil svoje srce in jima ni prisluhnil, kakor je rekel Gospod.
16 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ce wa Haruna, ‘Miƙa hannunka ka bugi ƙurar ƙasa,’ dukan ƙurar ƙasar Masar kuwa za tă zama ƙwari masu cizo.”
Gospod je rekel Mojzesu: »Reci Aronu: ›Iztegni svojo palico in udari prah dežele, da [iz] tega lahko nastanejo uši po vsej egiptovski deželi.‹«
17 Suka yi haka, da Haruna ya miƙa hannunsa da sandan, ya bugi ƙurar ƙasa, sai ƙwari masu cizo suka fito a kan mutane da dabbobi. Dukan ƙurar, ko’ina a ƙasar Masar ta zama cinnaku.
Storila sta tako, kajti Aron je iztegnil svojo roko s svojo palico in udaril prah dežele in [iz] tega so nastale uši na človeku in na živali. [Iz] vsega prahu dežele so nastale uši po vsej egiptovski deželi.
18 Sa’ad da bokayen Fir’auna suka yi ƙoƙari yin sihiri iri na rufe ido domin su fito da kwari, sai suka kāsa. Ƙwari masu cizo kuwa suka rufe mutane da dabbobi.
Čarovniki so tako storili s svojimi izrekanji urokov, da odstranijo uši, toda niso mogli, tako so bile uši na človeku in na živali.
19 Sai bokaye suka ce wa Fir’auna, “Wannan fa da hannun Allah a ciki.” Amma zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa saurara ba, kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
Potem so čarovniki rekli faraonu: »To je Božji prst.« Faraonovo srce pa je bilo zakrknjeno in jim ni prisluhnil, kakor je rekel Gospod.
20 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka tashi da sassafe ka sadu da Fir’auna a lokacin da za shi kogi, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, bari mutanena su tafi, don su yi mini sujada.
Gospod je rekel Mojzesu: »Vstani zgodaj zjutraj in stopi pred faraona. Glej, ta prihaja k vodi in mu reci: ›Tako govori Gospod: ›Pusti moje ljudstvo oditi, da mi bodo lahko služili.
21 In ba ka bar mutanena suka tafi ba, zan turo da tarin ƙuda a kanka da bayinka, a kan mutanenka da cikin gidajenka. Gidajen Masarawa za su cika da ƙudaje, har ma da ƙasa inda za su taka.
Ali pa, če ne boš hotel pustiti mojemu ljudstvu oditi, glej, bom poslal roje muh nate, na tvoje služabnike, na tvoje ljudstvo in v tvoje hiše. Hiše Egipčanov bodo polne rojev muh in tudi zemlja, na kateri so.
22 “‘Amma zan keɓe yankin Goshen, inda mutanena suke don kada ƙudaje su taɓa wurin, domin ka sani cewa Ni, Ubangiji, ina cikin wannan ƙasa.
Na ta dan bom oddvojil gošensko deželo, v kateri prebiva moje ljudstvo, da tam ne bo rojev muh; z namenom, da lahko spoznaš, da sem jaz Gospod v sredi zemlje.
23 Zan sa iyaka tsakanin jama’ata da jama’arka. Gobe ne wannan mu’ujiza za tă auku.’”
Jaz bom položil ločnico med svojim ljudstvom in tvojim ljudstvom. Jutri bo to znamenje.‹«
24 Ubangiji kuwa ya yi haka. Tarin ƙuda suka zubo a fadar Fir’auna da cikin gidajen bayinsa, da ko’ina a Masar, ƙasar kuwa ta lalace saboda ƙudaje.
In Gospod je storil tako. Prišel je nadležen roj muh v faraonovo hišo, v hiše njegovih služabnikov in v vso egiptovsko deželo. Dežela je bila okužena zaradi roja muh.
25 Sai Fir’auna ya kira Musa da Haruna ya ce, “Ku tafi, ku miƙa hadaya ga Allahnku, a nan a cikin ƙasar.”
Faraon je dal poklicati Mojzesa in Arona ter rekel: »Pojdite, žrtvujte vašemu Bogu v deželi.«
26 Amma Musa ya ce, “Wannan ba zai yiwu ba. Hadayun da mukan miƙa wa Ubangiji, Allahnmu haram ne ga Masarawa. In kuwa muka miƙa hadayun da suke haram a idanunsu, ba za su jajjefe mu ba?
Mojzes pa je rekel: »Ni primerno tako storiti, kajti ogabnost Egipčanom bomo žrtvovali Gospodu, našemu Bogu. Glej, pred njihovimi očmi bomo žrtvovali gnusobo Egipčanov in mar nas ne bodo kamnali?
27 Dole mu yi tafiya kwana uku cikin hamada domin miƙa hadayu ga Ubangiji Allahnmu, yadda ya umarce mu.”
Šli bomo tri dni potovanja v divjino in žrtvovali Gospodu, našemu Bogu, kakor nam bo zapovedal.«
28 Fir’auna ya ce, “Zan bar ku ku tafi, don ku miƙa hadayu ga Ubangiji Allahnku, a cikin hamada, amma ba za ku tafi da nisa ba. Yanzu ku yi mini addu’a.”
Faraon pa je rekel: »Pustil vam bom oditi, da boste lahko žrtvovali Gospodu, svojemu Bogu, v divjini; samo ne boste odšli zelo daleč proč. Rotite zame.«
29 Musa ya amsa, “Da zarar na bar ka, zan yi addu’a ga Ubangiji, gobe kuwa ƙudaje za su bar Fir’auna da fadawansa da kuma mutanensa. Sai dai a tabbata Fir’auna bai sāke yin ruɗi ta wurin ƙin barin mutane su tafi su miƙa hadayu ga Ubangiji ba.”
Mojzes je rekel: »Glej, ven grem od tebe in rotil bom Gospoda, da roji muh lahko jutri odidejo od faraona, od njegovih služabnikov in od njegovega ljudstva, toda faraon naj ne postopa več varljivo z nedovoljevanjem ljudstvu, da gre žrtvovat Gospodu.«
30 Sa’an nan Musa ya rabu da Fir’auna, ya kuma yi addu’a ga Ubangiji,
Mojzes je odšel izpred faraona in rotil Gospoda.
31 Ubangiji kuwa ya yi abin da Musa ya roƙa. Ƙudaje suka rabu da Fir’auna da fadawansa da kuma mutanensa; ba ƙudan da ya rage.
Gospod je storil glede na Mojzesovo besedo in roje muh odstranil od faraona, od njegovih služabnikov in od njegovega ljudstva. Niti ena ni preostala.
32 Amma a wannan lokaci ma, Fir’auna ya taurare zuciyarsa, bai kuma bar mutanen suka tafi ba.
Faraon pa je tudi tokrat zakrknil svoje srce niti ni hotel odpustiti ljudstva.