< Fitowa 8 >

1 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka je wurin Fir’auna, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka bar mutanena su tafi domin su yi mini sujada.
Da sa Herren til Moses: Gå inn til Farao og si til ham: Så sier Herren: La mitt folk fare, så de kan tjene mig!
2 In ka ƙi barinsu, zan hore ka da annoban kwaɗi a dukan ƙasarka.
Dersom du nekter å la dem fare, da vil jeg plage hele ditt land med frosk.
3 Nilu zai cika da kwaɗi. Za su haura zuwa cikin fadanka da kan gadonka, cikin gidajen bayinka da kan mutanenka, cikin kwanonin toye-toyenka da na cin abincinka.
Og elven skal vrimle av frosk, og de skal krype op og komme inn i ditt hus og i ditt sengkammer og op i din seng og i dine tjeneres hus og på ditt folk og i dine bakerovner og i dine deigtrau.
4 Kwaɗin nan za su yi ta tsalle a kanka, da kan mutanenka, da kuma kan dukan bayinka.’”
Ja, på dig og på ditt folk og på alle dine tjenere skal froskene krype op.
5 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ce wa Haruna, ‘Ka miƙa hannunka da sandanka bisa koguna da rafuffuka da kuma kududdufai, ka sa kwaɗi su fito su mamaye ƙasar Masar.’”
Og Herren sa til Moses: Si til Aron: Rekk ut din hånd med din stav over elvene, over kanalene og over sjøene, og la froskene komme op over Egyptens land!
6 Sai Haruna ya miƙa hannunsa bisa ruwan Masar, kwaɗi kuwa suka fito, suka mamaye ƙasar Masar.
Og Aron rakte ut sin hånd over Egyptens vann, og froskene kom op og dekket hele Egyptens land.
7 Amma bokaye ma suka yi abubuwan nan ta wurin sihirinsu; suka sa kwaɗi suka fito suka mamaye ƙasar Masar.
Men tegnsutleggerne gjorde det samme med sine hemmelige kunster og lot froskene komme op over Egyptens land.
8 Fir’auna ya kira Musa da Haruna ya ce, “Yi addu’a ga Ubangiji yă ɗauke kwaɗi daga gare ni da mutanena, zan kuwa bar mutanenku su tafi su yi hadaya ga Ubangiji.”
Da kalte Farao Moses og Aron til sig og sa: Bed til Herren at han vil ta froskene bort fra mig og mitt folk! Da til jeg la folket fare, sa de kan ofre til Herren.
9 Musa ya ce wa Fir’auna, “Na ba ka dama ka ba da lokacin da zan yi addu’a dominka da kuma bayinka da mutanenka, gidajenku kuwa za su rabu da kwaɗi, amma ban da waɗanda suke cikin Nilu.”
Og Moses sa til Farao: Ha selv den ære å si når jeg skal bede for dig og dine tjenere og ditt folk at froskene må bli drevet bort fra dig og dine hus, så de bare blir tilbake i elven.
10 Fir’auna ya ce, “Gobe.” Musa ya amsa, “Za a yi kamar yadda ka faɗa, domin ka sani babu wani kamar Ubangiji, Allahnmu.
Han svarte: Imorgen. Da sa Moses: La det bli som du sier, forat du kan kjenne at det ikke er nogen som Herren vår Gud.
11 Kwaɗin za su bar ka da gidajenka, bayinka da mutanenka; za su kasance a Nilu ne kaɗai.”
Froskene skal vike fra dig og dine hus og fra dine tjenere og ditt folk; bare i elven skal de bli tilbake.
12 Bayan Musa da Haruna sun bar Fir’auna, Sai Musa ya yi kuka ga Ubangiji saboda kwaɗin da ya kawo a bisa Fir’auna.
Så gikk Moses og Aron ut igjen fra Farao, og Moses ropte til Herren for froskenes skyld som han hadde ført over Farao.
13 Sai Ubangiji ya yi abin da Musa ya nema. Kwaɗin suka mutu a gidaje, da filaye, da kuma gonaki.
Og Herren gjorde som Moses hadde sagt, og froskene som var i husene og gårdene og på markene, døde bort;
14 Aka jibga su tsibi-tsibi, ƙasar ta yi ɗoyi saboda su.
og de samlet dem i dyngevis, og landet blev fylt med stank.
15 Amma da Fir’auna ya ga an sami sauƙi, sai ya taurare, ya ƙi yă saurari Musa da Haruna kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
Men da Farao så at han hadde fått luft, gjorde han sitt hjerte hårdt og hørte ikke på dem, således som Herren hadde sagt.
16 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ce wa Haruna, ‘Miƙa hannunka ka bugi ƙurar ƙasa,’ dukan ƙurar ƙasar Masar kuwa za tă zama ƙwari masu cizo.”
Da sa Herren til Moses: Si til Aron: Rekk ut din stav og slå i støvet på jorden, så skal det bli til mygg i hele Egyptens land.
17 Suka yi haka, da Haruna ya miƙa hannunsa da sandan, ya bugi ƙurar ƙasa, sai ƙwari masu cizo suka fito a kan mutane da dabbobi. Dukan ƙurar, ko’ina a ƙasar Masar ta zama cinnaku.
Og de gjorde således; Aron rakte ut sin hånd med sin stav og slo i støvet på jorden, og myggene kom både på folk og fe; alt støvet på jorden blev til mygg i hele Egyptens land.
18 Sa’ad da bokayen Fir’auna suka yi ƙoƙari yin sihiri iri na rufe ido domin su fito da kwari, sai suka kāsa. Ƙwari masu cizo kuwa suka rufe mutane da dabbobi.
Tegnsutleggerne gjorde likeså med sine hemmelige kunster; de søkte å få mygg frem, men kunde ikke. Og myggene blev sittende på folk og på fe.
19 Sai bokaye suka ce wa Fir’auna, “Wannan fa da hannun Allah a ciki.” Amma zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa saurara ba, kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
Da sa tegnsutleggerne til Farao: Dette er Guds finger. Men Faraos hjerte var og blev forherdet, og han hørte ikke på dem, således som Herren hadde sagt.
20 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka tashi da sassafe ka sadu da Fir’auna a lokacin da za shi kogi, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, bari mutanena su tafi, don su yi mini sujada.
Da sa Herren til Moses: Stå tidlig op imorgen, og still dig frem for Farao når han går ned til elven, og si til ham: Så sier Herren: La mitt folk fare, så de kan tjene mig!
21 In ba ka bar mutanena suka tafi ba, zan turo da tarin ƙuda a kanka da bayinka, a kan mutanenka da cikin gidajenka. Gidajen Masarawa za su cika da ƙudaje, har ma da ƙasa inda za su taka.
For dersom du ikke lar mitt folk fare, da sender jeg fluesvermer over dig og dine tjenere og ditt folk og dine hus, og egypternes hus skal fylles av fluesvermene, ja endog jorden de står på.
22 “‘Amma zan keɓe yankin Goshen, inda mutanena suke don kada ƙudaje su taɓa wurin, domin ka sani cewa Ni, Ubangiji, ina cikin wannan ƙasa.
Men på den dag vil jeg undta Gosen, hvor mitt folk bor, så det ikke skal være fluesvermer der; da skal du kjenne at jeg, Herren, er midt i landet.
23 Zan sa iyaka tsakanin jama’ata da jama’arka. Gobe ne wannan mu’ujiza za tă auku.’”
For jeg vil frelse mitt folk og gjøre forskjell på mitt folk og ditt folk; imorgen skal dette tegn skje.
24 Ubangiji kuwa ya yi haka. Tarin ƙuda suka zubo a fadar Fir’auna da cikin gidajen bayinsa, da ko’ina a Masar, ƙasar kuwa ta lalace saboda ƙudaje.
Og Herren gjorde som han hadde sagt, og det kom svære fluesvermer i Faraos hus og i hans tjeneres hus; i hele Egypten blev landet herjet av fluesvermer.
25 Sai Fir’auna ya kira Musa da Haruna ya ce, “Ku tafi, ku miƙa hadaya ga Allahnku, a nan a cikin ƙasar.”
Da kalte Farao Moses og Aron til sig og sa: Gå og ofre til eders Gud her i landet!
26 Amma Musa ya ce, “Wannan ba zai yiwu ba. Hadayun da mukan miƙa wa Ubangiji, Allahnmu haram ne ga Masarawa. In kuwa muka miƙa hadayun da suke haram a idanunsu, ba za su jajjefe mu ba?
Men Moses sa: Det er ikke rådelig å gjøre så; for det vi ofrer til Herren vår Gud, er en vederstyggelighet for egypterne; om vi nu ofret for egypternes øine det som er en vederstyggelighet for dem, vilde de da ikke stene oss?
27 Dole mu yi tafiya kwana uku cikin hamada domin miƙa hadayu ga Ubangiji Allahnmu, yadda ya umarce mu.”
Tre dagsreiser vil vi gå ut i ørkenen og ofre til Herren vår Gud, således som han byder oss.
28 Fir’auna ya ce, “Zan bar ku ku tafi, don ku miƙa hadayu ga Ubangiji Allahnku, a cikin hamada, amma ba za ku tafi da nisa ba. Yanzu ku yi mini addu’a.”
Da sa Farao: Jeg vil la eder fare, så I kan ofre til Herren eders Gud i ørkenen; men I må ikke dra langt bort. Bed for mig!
29 Musa ya amsa, “Da zarar na bar ka, zan yi addu’a ga Ubangiji, gobe kuwa ƙudaje za su bar Fir’auna da fadawansa da kuma mutanensa. Sai dai a tabbata Fir’auna bai sāke yin ruɗi ta wurin ƙin barin mutane su tafi su miƙa hadayu ga Ubangiji ba.”
Moses svarte: Se, jeg går nu ut og vil bede til Herren, og imorgen skal fluesvermene vike bort fra Farao, fra hans tjenere og fra hans folk; bare nu Farao ikke mere vil bruke svik, men la folket fare, så de kan ofre til Herren.
30 Sa’an nan Musa ya rabu da Fir’auna, ya kuma yi addu’a ga Ubangiji,
Så gikk Moses ut fra Farao og bad til Herren.
31 Ubangiji kuwa ya yi abin da Musa ya roƙa. Ƙudaje suka rabu da Fir’auna da fadawansa da kuma mutanensa; ba ƙudan da ya rage.
Og Herren gjorde som Moses bad, og lot fluesvermene vike bort fra Farao, fra hans tjenere og fra hans folk; det blev ikke én igjen.
32 Amma a wannan lokaci ma, Fir’auna ya taurare zuciyarsa, bai kuma bar mutanen suka tafi ba.
Men Farao forherdet sitt hjerte også denne gang; han lot ikke folket fare.

< Fitowa 8 >