< Fitowa 8 >
1 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka je wurin Fir’auna, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka bar mutanena su tafi domin su yi mini sujada.
ALAILA, i mai la o Iehova ia Mose, O hele oe io Parao la, a e i aku ia ia, Ke i mai nei o Iehova penei, E hookuu mai oe i ko'u poe Kanaka, i hookauwa mai lakou na'u.
2 In ka ƙi barinsu, zan hore ka da annoban kwaɗi a dukan ƙasarka.
A ina paha e hookuu ole mai oe, aia hoi, e hoino no wau i kou mau mokuna a pau i na rana;
3 Nilu zai cika da kwaɗi. Za su haura zuwa cikin fadanka da kan gadonka, cikin gidajen bayinka da kan mutanenka, cikin kwanonin toye-toyenka da na cin abincinka.
A e hoopuka nui mai ka muliwai i na rana, a e hele mai lakou iloko o kou hale, a me kou keena moe, a maluna o kou hikiee, a iloko o ka hale o kau poe kauwa, a maluna o kou poe kanaka, a maloko o kou mau imu, a maloko hoi o kou mau pa wili ai.
4 Kwaɗin nan za su yi ta tsalle a kanka, da kan mutanenka, da kuma kan dukan bayinka.’”
A e hele mai auanei na rana maluna ou, a maluna o kou poe kanaka, a maluna o kau poe kauwa a pau.
5 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ce wa Haruna, ‘Ka miƙa hannunka da sandanka bisa koguna da rafuffuka da kuma kududdufai, ka sa kwaɗi su fito su mamaye ƙasar Masar.’”
I mai la o Iehova ia Mose, E i aku oe ia Aarona, E o aku kou lima me kou kookoo maluna o na kahawai, a me na muliwai, a me na loko, i hiki mai na rana maluna o ka aina o Aigupita.
6 Sai Haruna ya miƙa hannunsa bisa ruwan Masar, kwaɗi kuwa suka fito, suka mamaye ƙasar Masar.
O aku la no ko Aarona lima maluna o ka wai o Aigupita, a hiki mai la na rana, a hoouhi paapu ae la i ka aina o Aigupita.
7 Amma bokaye ma suka yi abubuwan nan ta wurin sihirinsu; suka sa kwaɗi suka fito suka mamaye ƙasar Masar.
Hana iho la no pela na magoi i ka lakou mea e kilokilo ai, i hoohiki mai ai i na rana ma ka aina o Aigupita.
8 Fir’auna ya kira Musa da Haruna ya ce, “Yi addu’a ga Ubangiji yă ɗauke kwaɗi daga gare ni da mutanena, zan kuwa bar mutanenku su tafi su yi hadaya ga Ubangiji.”
Alaila, hea mai la o Parao ia Mose a me Aarona, i mai la, E pule aku olua ia Iehova, i lawe aku ia i na rana mai o'u aku nei, a mai ko'u poe kanaka aku, a e hookuu no wau i na kanaka, i kaumaha ai lakou na Iehova.
9 Musa ya ce wa Fir’auna, “Na ba ka dama ka ba da lokacin da zan yi addu’a dominka da kuma bayinka da mutanenka, gidajenku kuwa za su rabu da kwaɗi, amma ban da waɗanda suke cikin Nilu.”
I aku la o Mose ia Parao, E kauoha pono mai oe ia'u, i ka manawa hea ka'u e pule aku ai nou, a no kau poe kauwa hoi, a no kou poe kanaka, i laweia aku na rana mai ou aku la, a mai kou kauhale aku, a koe ma ka muliwai wale no?
10 Fir’auna ya ce, “Gobe.” Musa ya amsa, “Za a yi kamar yadda ka faɗa, domin ka sani babu wani kamar Ubangiji, Allahnmu.
Olelo mai la kela, Apopo. I aku la ia, E like me kau olelo, pela no auanei ia, i ike pono ai oe, aohe mea e ae e like me Iehova ko makou Akua.
11 Kwaɗin za su bar ka da gidajenka, bayinka da mutanenka; za su kasance a Nilu ne kaɗai.”
A e haalele mai no na rana ia oe, a me kou hale, a me kau poe kauwa, a me kou poe kanaka, a e koe ma ka muliwai wale no.
12 Bayan Musa da Haruna sun bar Fir’auna, Sai Musa ya yi kuka ga Ubangiji saboda kwaɗin da ya kawo a bisa Fir’auna.
Hele aku la o Mose laua o Aarona mai o Parao aku la: uwe aku la o Mose ia Iehova no na rana ana i lawe mai ai maluna o Parao.
13 Sai Ubangiji ya yi abin da Musa ya nema. Kwaɗin suka mutu a gidaje, da filaye, da kuma gonaki.
Hana iho la o Iehova e like me ka Mose olelo ana, a make iho la na rana ma na hale, a ma na pahale a ma na kula.
14 Aka jibga su tsibi-tsibi, ƙasar ta yi ɗoyi saboda su.
Hoiliili ae la lakou i na rana ma na puu: a pilau iho la ka aina.
15 Amma da Fir’auna ya ga an sami sauƙi, sai ya taurare, ya ƙi yă saurari Musa da Haruna kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
A ike iho la o Parao, he maha, hoopaakiki iho la ia i kona naau, aole i hoolohe mai i ka laua; e like me ka Iehova i olelo mai ai.
16 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ce wa Haruna, ‘Miƙa hannunka ka bugi ƙurar ƙasa,’ dukan ƙurar ƙasar Masar kuwa za tă zama ƙwari masu cizo.”
Olelo mai la o Iehova ia Mose, E i aku oe ia Aarona, e o aku oe i kou kookoo, a e hahau i ka lepo o ka aina, i lilo ia i makika ma ka aina a pau o Aigupita.
17 Suka yi haka, da Haruna ya miƙa hannunsa da sandan, ya bugi ƙurar ƙasa, sai ƙwari masu cizo suka fito a kan mutane da dabbobi. Dukan ƙurar, ko’ina a ƙasar Masar ta zama cinnaku.
Hana iho la laua pela; o aku la no ko Aarona lima me kona kookoo, hahau iho la i ka lepo o ka aina, a lilo ae la ia i makika ma na kanaka, a ma na holoholona; lilo no na hunalepo a pau o ka aina i makika ma ka aina a pau o Aigupita.
18 Sa’ad da bokayen Fir’auna suka yi ƙoƙari yin sihiri iri na rufe ido domin su fito da kwari, sai suka kāsa. Ƙwari masu cizo kuwa suka rufe mutane da dabbobi.
Hana iho la no pela na magoi, me ko lakou mea kilokilo, i hiki mai ai ka makika, aole nae i hiki ia lakou. He makika no nae maluna o na kanaka, a maluna o na holoholona.
19 Sai bokaye suka ce wa Fir’auna, “Wannan fa da hannun Allah a ciki.” Amma zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa saurara ba, kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
Alaila olelo ae la na magoi ia Parao, Eia no ka lima o ke Akua. Ua hoopaakikiia no nae ko Parao naau; aole ia i hoolohe i ka laua, e like me ka Iehova i olelo mai ai.
20 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka tashi da sassafe ka sadu da Fir’auna a lokacin da za shi kogi, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, bari mutanena su tafi, don su yi mini sujada.
Olelo mai la o Iehova ia Mose, A kakahiaka nui, e ala ae oe, a e ku imua i ke alo o Parao, aia hoi, e hele mai no ia iwaho i ka wai, a e i aku oe ia ia, Ke olelo mai nei o Iehova penei, E hookuu oe i ko'u poe kanaka, i hookauwa mai lakou na'u.
21 In ba ka bar mutanena suka tafi ba, zan turo da tarin ƙuda a kanka da bayinka, a kan mutanenka da cikin gidajenka. Gidajen Masarawa za su cika da ƙudaje, har ma da ƙasa inda za su taka.
Aka hoi, ina aole oe e hookuu mai i ko'u poe kanaka, aia hoi, e hoouna aku no au i na nalonahu maluna ou, a maluna o kau poe kauwa, a maluna o kou poe kanaka, a maloko o kou mau hale; a e piha na hale o ko Aigupita i na nalonahu, a me ka aina hoi kahi a lakou e noho ai.
22 “‘Amma zan keɓe yankin Goshen, inda mutanena suke don kada ƙudaje su taɓa wurin, domin ka sani cewa Ni, Ubangiji, ina cikin wannan ƙasa.
Ia la hoi, e hookaawale auanei au i ka aina o Gosena, i kahi e noho nei ko'u poe kanaka, i hiki ole ai ka nalonahu ilaila; i mea e ike ai oe, owau no Iehova mawaena o ka honua.
23 Zan sa iyaka tsakanin jama’ata da jama’arka. Gobe ne wannan mu’ujiza za tă auku.’”
A e kaa no au i pale mawaena o ko'u poe kanaka a me kou poe kanaka. Apopo e hiki mai keia mea.
24 Ubangiji kuwa ya yi haka. Tarin ƙuda suka zubo a fadar Fir’auna da cikin gidajen bayinsa, da ko’ina a Masar, ƙasar kuwa ta lalace saboda ƙudaje.
Hana iho la no o Iehova pela: a hiki mai la na nalonahu he nui loa maloko o ka hale o Parao, a me na hale o kana poe kauwa, a ma ka aina a pau o Aigupita: ua oki loa ka aina i na nalonahu.
25 Sai Fir’auna ya kira Musa da Haruna ya ce, “Ku tafi, ku miƙa hadaya ga Allahnku, a nan a cikin ƙasar.”
Hea mai la o Parao ia Mose a me Aarona, i mai la, E hele oukou, a e kaumaha aku i ko oukou Akua maloko o ka aina nei.
26 Amma Musa ya ce, “Wannan ba zai yiwu ba. Hadayun da mukan miƙa wa Ubangiji, Allahnmu haram ne ga Masarawa. In kuwa muka miƙa hadayun da suke haram a idanunsu, ba za su jajjefe mu ba?
I aku la o Mose, Aole pono ke hana pela; no ka mea, e kaumaha auanei makou na Iehova ko makou Akua i ka mea hoopailua a ko Aigupita nei: a ina e kaumaha aku makou i ka mea hoopailua a ko Aigupita nei imua o ko lakou maka, aole anei lakou e hailuku mai ia makou i ka pohaku?
27 Dole mu yi tafiya kwana uku cikin hamada domin miƙa hadayu ga Ubangiji Allahnmu, yadda ya umarce mu.”
E hele no makou i ekolu la hele iloko o ka waonahele, a e kaumaha aku na Iehova ko makou Akua, e like me kana e kauoha mai ai ia makou.
28 Fir’auna ya ce, “Zan bar ku ku tafi, don ku miƙa hadayu ga Ubangiji Allahnku, a cikin hamada, amma ba za ku tafi da nisa ba. Yanzu ku yi mini addu’a.”
I mai la o Parao, E hookuu aku no wau ia oukou, i kaumaha aku ai oukou na Iehova ko oukou Akua, ma ka waonahele: aka, mai hele aku oukou i kahi mamao. E pule aku olua no'u.
29 Musa ya amsa, “Da zarar na bar ka, zan yi addu’a ga Ubangiji, gobe kuwa ƙudaje za su bar Fir’auna da fadawansa da kuma mutanensa. Sai dai a tabbata Fir’auna bai sāke yin ruɗi ta wurin ƙin barin mutane su tafi su miƙa hadayu ga Ubangiji ba.”
I aku la o Mose, Aia hoi, ke hele aku nei au mai ou aku nei, a e nonoi aku au ia Iehova e lawe aku ia i na nalonahu mai o Parao aku, a mai kana poe kauwa aku, a mai kona poe kanaka aku; aia apopo. Aka, mai hoopunipuni hou mai o Parao. i ka hookuu ole i na kanaka e kaumaha aku na Iehova.
30 Sa’an nan Musa ya rabu da Fir’auna, ya kuma yi addu’a ga Ubangiji,
Hele aku la o Mose mai o Parao aku, a nonoi aku la ia Iehova.
31 Ubangiji kuwa ya yi abin da Musa ya roƙa. Ƙudaje suka rabu da Fir’auna da fadawansa da kuma mutanensa; ba ƙudan da ya rage.
Hana mai la o Iehova e like me ka olelo a Mose, a lawe aku la ia i na nalonahu mai o Parao aku, a mai kana poe kauwa aku, a mai kona poe kanaka aku; aole hookahi i koe.
32 Amma a wannan lokaci ma, Fir’auna ya taurare zuciyarsa, bai kuma bar mutanen suka tafi ba.
Hoopaakiki hou iho la o Parao i kona naau ia manawa no hoi, aole i hookuu aku i na kanaka.