< Fitowa 8 >

1 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka je wurin Fir’auna, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka bar mutanena su tafi domin su yi mini sujada.
Le Seigneur dit aussi a Moïse: Entre auprès de Pharaon, et tu lui diras: Voici ce que dit le Seigneur: Laisse aller mon peuple, afin qu’il me sacrifie:
2 In ka ƙi barinsu, zan hore ka da annoban kwaɗi a dukan ƙasarka.
Mais si tu ne veux pas le laisser aller, voici que moi je frapperai tout ton pays de grenouilles.
3 Nilu zai cika da kwaɗi. Za su haura zuwa cikin fadanka da kan gadonka, cikin gidajen bayinka da kan mutanenka, cikin kwanonin toye-toyenka da na cin abincinka.
Car le fleuve fera jaillir des grenouilles, qui monteront, et entreront dans ta maison et dans la chambre où est ton lit, et sur ton lit. et dans les maisons de tes serviteurs, et au milieu de ton peuple, et dans tes fours, et sur les restes de tes aliments.
4 Kwaɗin nan za su yi ta tsalle a kanka, da kan mutanenka, da kuma kan dukan bayinka.’”
Ainsi c’est chez toi, et chez ton peuple et chez tous tes serviteurs qu’entreront les grenouilles.
5 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ce wa Haruna, ‘Ka miƙa hannunka da sandanka bisa koguna da rafuffuka da kuma kududdufai, ka sa kwaɗi su fito su mamaye ƙasar Masar.’”
Le Seigneur dit donc à Moïse: Dis à Aaron: Etends ta main sur les fleuves, et sur les ruisseaux et les marais, et fais venir les grenouilles sur la terre d’Egypte.
6 Sai Haruna ya miƙa hannunsa bisa ruwan Masar, kwaɗi kuwa suka fito, suka mamaye ƙasar Masar.
Et Aaron étendit sa main sur les eaux d’Egypte, et les grenouilles montèrent et couvrirent la terre d’Egypte.
7 Amma bokaye ma suka yi abubuwan nan ta wurin sihirinsu; suka sa kwaɗi suka fito suka mamaye ƙasar Masar.
Mais les magiciens aussi firent pareillement par leurs enchantements, et ils firent venir les grenouilles sur la terre d’Egypte.
8 Fir’auna ya kira Musa da Haruna ya ce, “Yi addu’a ga Ubangiji yă ɗauke kwaɗi daga gare ni da mutanena, zan kuwa bar mutanenku su tafi su yi hadaya ga Ubangiji.”
Or Pharaon appela Moïse et Aaron et leur dit: Priez le Seigneur qu’il éloigne les grenouilles de moi et de mon peuple, et je laisserai aller le peuple, afin qu’il sacrifie au Seigneur.
9 Musa ya ce wa Fir’auna, “Na ba ka dama ka ba da lokacin da zan yi addu’a dominka da kuma bayinka da mutanenka, gidajenku kuwa za su rabu da kwaɗi, amma ban da waɗanda suke cikin Nilu.”
Et Moïse répondit à Pharaon: Indique-moi quand je devrai prier pour toi, et pour tes serviteurs et pour ton peuple, afin que les grenouilles soient chassées loin de toi et de ta maison, et de tes serviteurs et de ton peuple, et qu’elles demeurent seulement dans le fleuve.
10 Fir’auna ya ce, “Gobe.” Musa ya amsa, “Za a yi kamar yadda ka faɗa, domin ka sani babu wani kamar Ubangiji, Allahnmu.
Celui-ci répondit: Demain. Or Moïse: Je ferai, dit-il, selon ta parole, afin que tu saches qu’il n’y en a point comme le Seigneur notre Dieu.
11 Kwaɗin za su bar ka da gidajenka, bayinka da mutanenka; za su kasance a Nilu ne kaɗai.”
Et les grenouilles s’éloigneront de toi et de ta maison, et de tes serviteurs et de ton peuple, et elles demeureront seulement dans le fleuve.
12 Bayan Musa da Haruna sun bar Fir’auna, Sai Musa ya yi kuka ga Ubangiji saboda kwaɗin da ya kawo a bisa Fir’auna.
Alors Moïse et Aaron sortirent de devant Pharaon; et Moïse cria au Seigneur, à cause de la promesse qu’il avait faite à Pharaon touchant les grenouilles.
13 Sai Ubangiji ya yi abin da Musa ya nema. Kwaɗin suka mutu a gidaje, da filaye, da kuma gonaki.
Et le Seigneur fit selon la parole de Moïse; et les grenouilles des maisons, et des villages et des champs, moururent.
14 Aka jibga su tsibi-tsibi, ƙasar ta yi ɗoyi saboda su.
Et on les entassa en immenses monceaux, et la terre en fut infectée.
15 Amma da Fir’auna ya ga an sami sauƙi, sai ya taurare, ya ƙi yă saurari Musa da Haruna kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
Or Pharaon, voyant qu’il lui avait été donné du relâche, endurcit son cœur, et il n’écouta pas Moïse et Aaron, comme avait ordonné le Seigneur.
16 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ce wa Haruna, ‘Miƙa hannunka ka bugi ƙurar ƙasa,’ dukan ƙurar ƙasar Masar kuwa za tă zama ƙwari masu cizo.”
Alors le Seigneur dit à Moïse: Dis à Aaron: Etends ta verge et frappe la poussière de la terre, et qu’il y ait des moucherons dans toute la terre d’Egypte.
17 Suka yi haka, da Haruna ya miƙa hannunsa da sandan, ya bugi ƙurar ƙasa, sai ƙwari masu cizo suka fito a kan mutane da dabbobi. Dukan ƙurar, ko’ina a ƙasar Masar ta zama cinnaku.
Et ils firent ainsi. Aaron étendit donc sa main, tenant sa verge; et il frappa la poussière de la terre, et les moucherons s’attachèrent aux hommes et aux bêtes; toute la poussière de la terre fut changée en moucherons par toute la terre d’Egypte.
18 Sa’ad da bokayen Fir’auna suka yi ƙoƙari yin sihiri iri na rufe ido domin su fito da kwari, sai suka kāsa. Ƙwari masu cizo kuwa suka rufe mutane da dabbobi.
Et les magiciens firent pareillement par leurs enchantements, pour produire les moucherons, mais ils ne le purent; et les moucherons restaient attachés aux hommes et aux bêtes.
19 Sai bokaye suka ce wa Fir’auna, “Wannan fa da hannun Allah a ciki.” Amma zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa saurara ba, kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
Alors les magiciens dirent à Pharaon: C’est le doigt de Dieu; et le cœur de Pharaon s’endurcit, et il n’écouta pas Moïse et Aaron, comme avait ordonné le Seigneur.
20 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka tashi da sassafe ka sadu da Fir’auna a lokacin da za shi kogi, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, bari mutanena su tafi, don su yi mini sujada.
Le Seigneur dit aussi à Moïse: Lève-toi au point du jour, et présente-toi devant Pharaon; car il sortira pour aller vers l’eau, et tu lui diras: Voici ce que dit le Seigneur: Laisse aller mon peuple, afin qu’il me sacrifie.
21 In ba ka bar mutanena suka tafi ba, zan turo da tarin ƙuda a kanka da bayinka, a kan mutanenka da cikin gidajenka. Gidajen Masarawa za su cika da ƙudaje, har ma da ƙasa inda za su taka.
Que si tu ne le laisses pas aller, voici que je vais envoyer sur toi et sur tes serviteurs, et sur ton peuple et en tes maisons, toute sorte de mouches; et les maisons des Egyptiens seront remplies de mouches de diverses espèces, et toute la terre en laquelle ils seront.
22 “‘Amma zan keɓe yankin Goshen, inda mutanena suke don kada ƙudaje su taɓa wurin, domin ka sani cewa Ni, Ubangiji, ina cikin wannan ƙasa.
Mais je rendrai merveilleuse en ce jour-là la terre de Gessen, en laquelle est mon peuple, de manière à ce qu’il n’y ait point là de mouches, et que tu saches que moi le Seigneur, je suis au milieu de cette terre.
23 Zan sa iyaka tsakanin jama’ata da jama’arka. Gobe ne wannan mu’ujiza za tă auku.’”
C’est ainsi que je mettrai une distinction entre mon peuple et ton peuple: demain aura lieu ce prodige.
24 Ubangiji kuwa ya yi haka. Tarin ƙuda suka zubo a fadar Fir’auna da cikin gidajen bayinsa, da ko’ina a Masar, ƙasar kuwa ta lalace saboda ƙudaje.
Et le Seigneur fit ainsi. Il vint des mouches très dangereuses dans les maisons de Pharaon et de ses serviteurs, et dans toute la terre d’Egypte: ainsi la terre fut infectée par les mouches de cette sorte.
25 Sai Fir’auna ya kira Musa da Haruna ya ce, “Ku tafi, ku miƙa hadaya ga Allahnku, a nan a cikin ƙasar.”
Alors Pharaon appela Moïse et Aaron, et leur dit: Allez et sacrifiez à votre Dieu en cette terre-ci.
26 Amma Musa ya ce, “Wannan ba zai yiwu ba. Hadayun da mukan miƙa wa Ubangiji, Allahnmu haram ne ga Masarawa. In kuwa muka miƙa hadayun da suke haram a idanunsu, ba za su jajjefe mu ba?
Mais Moïse répondit: Cela ne peut se faire ainsi; car les sacrifices que nous offrirons au Seigneur notre Dieu sont des abominations pour les Egyptiens; que si nous tuons devant eux les animaux qu’adorent les Egyptiens, ils nous lapideront.
27 Dole mu yi tafiya kwana uku cikin hamada domin miƙa hadayu ga Ubangiji Allahnmu, yadda ya umarce mu.”
Nous ferons le chemin de trois journées dans le désert, et nous sacrifierons au Seigneur notre Dieu, comme il nous l’a ordonné.
28 Fir’auna ya ce, “Zan bar ku ku tafi, don ku miƙa hadayu ga Ubangiji Allahnku, a cikin hamada, amma ba za ku tafi da nisa ba. Yanzu ku yi mini addu’a.”
Et Pharaon reprit: Moi. je vous laisserai aller, afin que vous sacrifiiez au Seigneur votre Dieu dans le désert: cependant n’allez pas plus loin, priez pour moi.
29 Musa ya amsa, “Da zarar na bar ka, zan yi addu’a ga Ubangiji, gobe kuwa ƙudaje za su bar Fir’auna da fadawansa da kuma mutanensa. Sai dai a tabbata Fir’auna bai sāke yin ruɗi ta wurin ƙin barin mutane su tafi su miƙa hadayu ga Ubangiji ba.”
Moïse répondit: Sorti d’avec toi, je prierai le Seigneur, et demain les mouches s’éloigneront de Pharaon, et de ses serviteurs et de son peuple; cependant ne me trompe plus désormais, en ne laissant pas aller le peuple sacrifier au Seigneur.
30 Sa’an nan Musa ya rabu da Fir’auna, ya kuma yi addu’a ga Ubangiji,
Moïse donc, sortit de la présence de Pharaon, pria le Seigneur;
31 Ubangiji kuwa ya yi abin da Musa ya roƙa. Ƙudaje suka rabu da Fir’auna da fadawansa da kuma mutanensa; ba ƙudan da ya rage.
Qui fit selon sa parole, et il enleva les mouches de Pharaon, et de ses serviteurs et de son peuple: il n’en resta pas même une seule.
32 Amma a wannan lokaci ma, Fir’auna ya taurare zuciyarsa, bai kuma bar mutanen suka tafi ba.
Mais le cœur de Pharaon s’endurcit: en sorte que, pas même cette fois, il ne laissa aller le peuple.

< Fitowa 8 >