< Fitowa 8 >

1 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka je wurin Fir’auna, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka bar mutanena su tafi domin su yi mini sujada.
Après cela l'Eternel dit à Moïse: va vers Pharaon, et lui dis: ainsi a dit l'Eternel: laisse aller mon peuple, afin qu'ils me servent.
2 In ka ƙi barinsu, zan hore ka da annoban kwaɗi a dukan ƙasarka.
Que si tu refuses de le laisser aller, voici, je m'en vais frapper de grenouilles toutes tes contrées.
3 Nilu zai cika da kwaɗi. Za su haura zuwa cikin fadanka da kan gadonka, cikin gidajen bayinka da kan mutanenka, cikin kwanonin toye-toyenka da na cin abincinka.
Et le fleuve fourmillera de grenouilles, qui monteront et entreront dans ta maison, et dans la chambre où tu couches, et sur ton lit, et dans la maison de tes serviteurs, et parmi tout ton peuple, dans tes fours, et dans tes maies.
4 Kwaɗin nan za su yi ta tsalle a kanka, da kan mutanenka, da kuma kan dukan bayinka.’”
Ainsi les grenouilles monteront sur toi, sur ton peuple, et sur tous tes serviteurs.
5 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ce wa Haruna, ‘Ka miƙa hannunka da sandanka bisa koguna da rafuffuka da kuma kududdufai, ka sa kwaɗi su fito su mamaye ƙasar Masar.’”
L'Eternel donc dit à Moïse: dis à Aaron: étends ta main avec ta verge sur les fleuves, sur les rivières, et sur les marais, et fais monter les grenouilles sur le pays d'Egypte.
6 Sai Haruna ya miƙa hannunsa bisa ruwan Masar, kwaɗi kuwa suka fito, suka mamaye ƙasar Masar.
Et Aaron étendit sa main sur les eaux de l'Egypte, et les grenouilles montèrent, et couvrirent le pays d'Egypte.
7 Amma bokaye ma suka yi abubuwan nan ta wurin sihirinsu; suka sa kwaɗi suka fito suka mamaye ƙasar Masar.
Mais les magiciens firent de même par leurs enchantements, et firent monter des grenouilles sur le pays d'Egypte.
8 Fir’auna ya kira Musa da Haruna ya ce, “Yi addu’a ga Ubangiji yă ɗauke kwaɗi daga gare ni da mutanena, zan kuwa bar mutanenku su tafi su yi hadaya ga Ubangiji.”
Alors Pharaon appela Moïse et Aaron, et leur dit: fléchissez l'Eternel par [vos] prières, afin qu'il retire les grenouilles de dessus moi et de dessus mon peuple; et je laisserai aller le peuple, afin qu'ils sacrifient à l'Eternel.
9 Musa ya ce wa Fir’auna, “Na ba ka dama ka ba da lokacin da zan yi addu’a dominka da kuma bayinka da mutanenka, gidajenku kuwa za su rabu da kwaɗi, amma ban da waɗanda suke cikin Nilu.”
Et Moïse dit à Pharaon: glorifie-toi sur moi. Pour quel temps fléchirai-je par mes prières [l'Eternel] pour toi et pour tes serviteurs, et pour ton peuple, afin qu'il chasse les grenouilles loin de toi, et de tes maisons? Il en demeurera seulement dans le fleuve.
10 Fir’auna ya ce, “Gobe.” Musa ya amsa, “Za a yi kamar yadda ka faɗa, domin ka sani babu wani kamar Ubangiji, Allahnmu.
Alors il répondit: pour demain. Et [Moïse] dit: [il sera fait] selon ta parole, afin que tu saches qu'il n'y a nul [Dieu] tel que l'Eternel notre Dieu.
11 Kwaɗin za su bar ka da gidajenka, bayinka da mutanenka; za su kasance a Nilu ne kaɗai.”
Les grenouilles donc se retireront de toi, et de tes maisons, et de tes serviteurs, et de ton peuple; il en demeurera seulement dans le fleuve.
12 Bayan Musa da Haruna sun bar Fir’auna, Sai Musa ya yi kuka ga Ubangiji saboda kwaɗin da ya kawo a bisa Fir’auna.
Alors Moïse et Aaron sortirent d'avec Pharaon; et Moïse cria à l'Eternel au sujet des grenouilles qu'il avait fait venir sur Pharaon.
13 Sai Ubangiji ya yi abin da Musa ya nema. Kwaɗin suka mutu a gidaje, da filaye, da kuma gonaki.
Et l'Eternel fit selon la parole de Moïse. Ainsi les grenouilles moururent; et il n'y en eut plus dans les maisons, ni dans les villages, ni à la campagne.
14 Aka jibga su tsibi-tsibi, ƙasar ta yi ɗoyi saboda su.
Et on les amassa par monceaux, et la terre en fut infectée.
15 Amma da Fir’auna ya ga an sami sauƙi, sai ya taurare, ya ƙi yă saurari Musa da Haruna kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
Mais Pharaon voyant qu'il avait du relâche, endurcit son cœur, et ne les écouta point, selon que l'Eternel [en] avait parlé.
16 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ce wa Haruna, ‘Miƙa hannunka ka bugi ƙurar ƙasa,’ dukan ƙurar ƙasar Masar kuwa za tă zama ƙwari masu cizo.”
Et l'Eternel dit à Moïse: dis à Aaron: étends ta verge, et frappe la poussière de la terre, et elle deviendra des poux par tout le pays d'Egypte.
17 Suka yi haka, da Haruna ya miƙa hannunsa da sandan, ya bugi ƙurar ƙasa, sai ƙwari masu cizo suka fito a kan mutane da dabbobi. Dukan ƙurar, ko’ina a ƙasar Masar ta zama cinnaku.
Et ils firent ainsi. Et Aaron étendit sa main avec sa verge, et frappa la poussière de la terre, et elle devint des poux, sur les hommes, et sur les bêtes; toute la poussière du pays devint des poux en tout le pays d'Egypte.
18 Sa’ad da bokayen Fir’auna suka yi ƙoƙari yin sihiri iri na rufe ido domin su fito da kwari, sai suka kāsa. Ƙwari masu cizo kuwa suka rufe mutane da dabbobi.
Et les magiciens voulurent faire de même par leurs enchantements, pour produire des poux, mais ils ne purent. Les poux furent donc tant sur les hommes que sur les bêtes.
19 Sai bokaye suka ce wa Fir’auna, “Wannan fa da hannun Allah a ciki.” Amma zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa saurara ba, kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
Alors les magiciens dirent à Pharaon: c'est ici le doigt de Dieu. Toutefois le cœur de Pharaon s'endurcit et il ne les écouta point, selon que l'Eternel [en] avait parlé.
20 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka tashi da sassafe ka sadu da Fir’auna a lokacin da za shi kogi, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, bari mutanena su tafi, don su yi mini sujada.
Puis l'Eternel dit à Moïse: lève-toi de bon matin, et te présente devant Pharaon; voici, il sortira vers l'eau, et tu lui diras: ainsi a dit l'Eternel: laisse aller mon peuple, afin qu'ils me servent.
21 In ba ka bar mutanena suka tafi ba, zan turo da tarin ƙuda a kanka da bayinka, a kan mutanenka da cikin gidajenka. Gidajen Masarawa za su cika da ƙudaje, har ma da ƙasa inda za su taka.
Car si tu ne laisses pas aller mon peuple, voici, je m'en vais envoyer contre toi, contre tes serviteurs, contre ton peuple, et contre tes maisons, un mélange d'insectes; et les maisons des Egyptiens seront remplies de ce mélange, et la terre aussi sur laquelle ils seront.
22 “‘Amma zan keɓe yankin Goshen, inda mutanena suke don kada ƙudaje su taɓa wurin, domin ka sani cewa Ni, Ubangiji, ina cikin wannan ƙasa.
Mais je distinguerai en ce jour-là le pays de Goscen, où se tient mon peuple, tellement qu'il n'y aura nul mélange d'insectes, afin que tu saches que je [suis] l'Eternel au milieu de la terre.
23 Zan sa iyaka tsakanin jama’ata da jama’arka. Gobe ne wannan mu’ujiza za tă auku.’”
Et je mettrai de la différence entre ton peuple et mon peuple; demain ce signe-là se fera.
24 Ubangiji kuwa ya yi haka. Tarin ƙuda suka zubo a fadar Fir’auna da cikin gidajen bayinsa, da ko’ina a Masar, ƙasar kuwa ta lalace saboda ƙudaje.
Et l'Eternel [le] fit ainsi; et un grand mélange d'insectes entra dans la maison de Pharaon, et dans chaque maison de ses serviteurs, et dans tout le pays d'Egypte, [de sorte que] la terre fut gâtée par ce mélange.
25 Sai Fir’auna ya kira Musa da Haruna ya ce, “Ku tafi, ku miƙa hadaya ga Allahnku, a nan a cikin ƙasar.”
Et Pharaon appela Moïse et Aaron, et [leur] dit: allez, sacrifiez à votre Dieu dans ce pays.
26 Amma Musa ya ce, “Wannan ba zai yiwu ba. Hadayun da mukan miƙa wa Ubangiji, Allahnmu haram ne ga Masarawa. In kuwa muka miƙa hadayun da suke haram a idanunsu, ba za su jajjefe mu ba?
Mais Moïse dit: il n'est pas à propos de faire ainsi; car nous sacrifierions à l'Eternel notre Dieu l'abomination des Egyptiens. Voici, si nous sacrifions l'abomination des Égyptiens devant leurs yeux, ne nous lapideraient-ils pas?
27 Dole mu yi tafiya kwana uku cikin hamada domin miƙa hadayu ga Ubangiji Allahnmu, yadda ya umarce mu.”
Nous irons le chemin de trois jours au désert, et nous sacrifierons à l'Eternel notre Dieu, comme il nous dira.
28 Fir’auna ya ce, “Zan bar ku ku tafi, don ku miƙa hadayu ga Ubangiji Allahnku, a cikin hamada, amma ba za ku tafi da nisa ba. Yanzu ku yi mini addu’a.”
Alors Pharaon dit: je vous laisserai aller pour sacrifier dans le désert à l'Eternel votre Dieu; toutefois vous ne vous éloignerez nullement en vous en allant. Fléchissez [l'Eternel] pour moi par vos prières.
29 Musa ya amsa, “Da zarar na bar ka, zan yi addu’a ga Ubangiji, gobe kuwa ƙudaje za su bar Fir’auna da fadawansa da kuma mutanensa. Sai dai a tabbata Fir’auna bai sāke yin ruɗi ta wurin ƙin barin mutane su tafi su miƙa hadayu ga Ubangiji ba.”
Et Moïse dit: voici, je sors d'avec toi, et je fléchirai par prières l'Eternel, afin que le mélange d'insectes se retire demain de Pharaon, de ses serviteurs, et de son peuple. Mais que Pharaon ne continue point à se moquer, en ne laissant point aller le peuple pour sacrifier à l'Eternel.
30 Sa’an nan Musa ya rabu da Fir’auna, ya kuma yi addu’a ga Ubangiji,
Alors Moïse sortit d'avec Pharaon, et fléchit l'Eternel par prières.
31 Ubangiji kuwa ya yi abin da Musa ya roƙa. Ƙudaje suka rabu da Fir’auna da fadawansa da kuma mutanensa; ba ƙudan da ya rage.
Et l'Eternel fit selon la parole de Moïse; et le mélange d'insectes se retira de Pharaon, et de ses serviteurs, et de son peuple; il ne resta pas un seul [insecte].
32 Amma a wannan lokaci ma, Fir’auna ya taurare zuciyarsa, bai kuma bar mutanen suka tafi ba.
Mais Pharaon endurcit son cœur encore cette fois, et ne laissa point aller le peuple.

< Fitowa 8 >