< Fitowa 8 >

1 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka je wurin Fir’auna, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka bar mutanena su tafi domin su yi mini sujada.
And the Lord said to Moses: Go in to Pharao, and thou shalt say to him: Thus saith the Lord: Let my people go to sacrifice to me.
2 In ka ƙi barinsu, zan hore ka da annoban kwaɗi a dukan ƙasarka.
But if thou wilt not let them go behold I will strike all thy coasts with frogs.
3 Nilu zai cika da kwaɗi. Za su haura zuwa cikin fadanka da kan gadonka, cikin gidajen bayinka da kan mutanenka, cikin kwanonin toye-toyenka da na cin abincinka.
And the river shall bring forth an abundance of frogs: which shall come up, and enter into thy house, and thy bedchamber, and upon thy bed, and in the houses of thy servants, and to thy people, and into thy ovens, and into the remains of thy meats;
4 Kwaɗin nan za su yi ta tsalle a kanka, da kan mutanenka, da kuma kan dukan bayinka.’”
And the frogs shall come in to thee and to thy people, and to all thy servants.
5 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ce wa Haruna, ‘Ka miƙa hannunka da sandanka bisa koguna da rafuffuka da kuma kududdufai, ka sa kwaɗi su fito su mamaye ƙasar Masar.’”
And the Lord said to Moses: Say to Aaron, Stretch forth thy hand upon the streams and upon the rivers and the pools, and bring forth frogs upon the land of Egypt.
6 Sai Haruna ya miƙa hannunsa bisa ruwan Masar, kwaɗi kuwa suka fito, suka mamaye ƙasar Masar.
And Aaron stretched forth his hand upon the waters of Egypt, and the frogs came up, and covered the land of Egypt.
7 Amma bokaye ma suka yi abubuwan nan ta wurin sihirinsu; suka sa kwaɗi suka fito suka mamaye ƙasar Masar.
And the magicians also by their enchantments did in like manner, and the brought forth frogs upon all the land of Egypt.
8 Fir’auna ya kira Musa da Haruna ya ce, “Yi addu’a ga Ubangiji yă ɗauke kwaɗi daga gare ni da mutanena, zan kuwa bar mutanenku su tafi su yi hadaya ga Ubangiji.”
But Pharao called Moses and Aaron and said to them: Pray ye to the Lord to take away the frogs from me and from my people; and I will let the people go to sacrifice to the Lord.
9 Musa ya ce wa Fir’auna, “Na ba ka dama ka ba da lokacin da zan yi addu’a dominka da kuma bayinka da mutanenka, gidajenku kuwa za su rabu da kwaɗi, amma ban da waɗanda suke cikin Nilu.”
And Moses said to Pharao: Set me a time when I shall pray for thee, and for thy servants, and for thy people, that the frogs may be driven away from thee and from thy house, and from thy servants, and from thy people: and may remain only in the river.
10 Fir’auna ya ce, “Gobe.” Musa ya amsa, “Za a yi kamar yadda ka faɗa, domin ka sani babu wani kamar Ubangiji, Allahnmu.
And he answered: Tomorrow. But he said: I will do according to thy word; that thou mayst know that there is none like to the Lord our God.
11 Kwaɗin za su bar ka da gidajenka, bayinka da mutanenka; za su kasance a Nilu ne kaɗai.”
And the frogs shall depart from thee, and from thy house, and from thy servants, and from thy people; and shall remain only in the river.
12 Bayan Musa da Haruna sun bar Fir’auna, Sai Musa ya yi kuka ga Ubangiji saboda kwaɗin da ya kawo a bisa Fir’auna.
And Moses and Aaron went forth from Pharao: and Moses cried to the Lord for the promise, which he had made to Pharao concerning the frogs.
13 Sai Ubangiji ya yi abin da Musa ya nema. Kwaɗin suka mutu a gidaje, da filaye, da kuma gonaki.
And the Lord did according to the word of Moses: and the frogs died out of the houses, and out of the villages, and out of the fields:
14 Aka jibga su tsibi-tsibi, ƙasar ta yi ɗoyi saboda su.
And they gathered them together into immense heaps, and the land was corrupted.
15 Amma da Fir’auna ya ga an sami sauƙi, sai ya taurare, ya ƙi yă saurari Musa da Haruna kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
And Pharao seeing that rest was given, hardened his own heart, and did not hear them, as the Lord had commanded.
16 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ce wa Haruna, ‘Miƙa hannunka ka bugi ƙurar ƙasa,’ dukan ƙurar ƙasar Masar kuwa za tă zama ƙwari masu cizo.”
And the Lord said to Moses: Say to Aaron, Stretch forth thy rod, and strike the dust of the earth: and may there be sciniphs in all the land of Egypt.
17 Suka yi haka, da Haruna ya miƙa hannunsa da sandan, ya bugi ƙurar ƙasa, sai ƙwari masu cizo suka fito a kan mutane da dabbobi. Dukan ƙurar, ko’ina a ƙasar Masar ta zama cinnaku.
And they did so. And Aaron stretched forth his hand, holding the rod: and he struck the dust of the earth, and there came sciniphs on men and on beasts: all the dust of the earth was turned into sciniphs through all the land of Egypt.
18 Sa’ad da bokayen Fir’auna suka yi ƙoƙari yin sihiri iri na rufe ido domin su fito da kwari, sai suka kāsa. Ƙwari masu cizo kuwa suka rufe mutane da dabbobi.
And the magicians with their enchantments practiced in like manner, to bring forth sciniphs, and they could not and there were sciniphs as well on men as on beasts.
19 Sai bokaye suka ce wa Fir’auna, “Wannan fa da hannun Allah a ciki.” Amma zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa saurara ba, kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
And the magicians said to Pharao This is the finger of God. And Pharao heart was hardened, and he hearkened not unto them, as the Lord had commanded.
20 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka tashi da sassafe ka sadu da Fir’auna a lokacin da za shi kogi, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, bari mutanena su tafi, don su yi mini sujada.
The Lord also said to Moses: Arise early, and stand before Pharao: for he will go forth to the waters: and thou shalt say to him: Thus saith the Lord: Let my people go to sacrifice to me.
21 In ba ka bar mutanena suka tafi ba, zan turo da tarin ƙuda a kanka da bayinka, a kan mutanenka da cikin gidajenka. Gidajen Masarawa za su cika da ƙudaje, har ma da ƙasa inda za su taka.
But if thou wilt not let them go, behold I will send in upon thee, and upon thy servants, and upon thy houses all kind of flies: and the houses of the Egyptians shall be filled with flies of divers kinds, and the whole land wherein they shall be.
22 “‘Amma zan keɓe yankin Goshen, inda mutanena suke don kada ƙudaje su taɓa wurin, domin ka sani cewa Ni, Ubangiji, ina cikin wannan ƙasa.
And I will make the land of Gessen wherein my people is, wonderful in that lay, so that flies shall not be there: and thou shalt know that I am the Lord in the midst of the earth.
23 Zan sa iyaka tsakanin jama’ata da jama’arka. Gobe ne wannan mu’ujiza za tă auku.’”
And I will put a division between my people and thy people: tomorrow shall this sign be.
24 Ubangiji kuwa ya yi haka. Tarin ƙuda suka zubo a fadar Fir’auna da cikin gidajen bayinsa, da ko’ina a Masar, ƙasar kuwa ta lalace saboda ƙudaje.
And the Lord did so. And there came a very grievous swarm of flies into he houses of Pharao and of his servants, and into all the land of Egypt: and the land was corrupted by this kind of flies.
25 Sai Fir’auna ya kira Musa da Haruna ya ce, “Ku tafi, ku miƙa hadaya ga Allahnku, a nan a cikin ƙasar.”
And Pharao called Moses and Aaron, and said to them: Go, and sacrifice to your God in this land.
26 Amma Musa ya ce, “Wannan ba zai yiwu ba. Hadayun da mukan miƙa wa Ubangiji, Allahnmu haram ne ga Masarawa. In kuwa muka miƙa hadayun da suke haram a idanunsu, ba za su jajjefe mu ba?
And Moses said: It cannot be so: for we shall sacrifice the abominations of the Egyptians to the Lord our God: now if we kill those things which the Egyptians worship, in their presence, they will stone us.
27 Dole mu yi tafiya kwana uku cikin hamada domin miƙa hadayu ga Ubangiji Allahnmu, yadda ya umarce mu.”
We will go three days’ journey into the wilderness: and we will sacrifice to the Lord our God, as he hath commanded us.
28 Fir’auna ya ce, “Zan bar ku ku tafi, don ku miƙa hadayu ga Ubangiji Allahnku, a cikin hamada, amma ba za ku tafi da nisa ba. Yanzu ku yi mini addu’a.”
And Pharao said: I will let you go to sacrifice to the Lord your God in the wilderness: but go no farther: pray for me.
29 Musa ya amsa, “Da zarar na bar ka, zan yi addu’a ga Ubangiji, gobe kuwa ƙudaje za su bar Fir’auna da fadawansa da kuma mutanensa. Sai dai a tabbata Fir’auna bai sāke yin ruɗi ta wurin ƙin barin mutane su tafi su miƙa hadayu ga Ubangiji ba.”
And Moses said: I will go out from thee, and will pray to the Lord: and the flies shall depart from Pharao, and from his servants, and from his people tomorrow: but do not deceive any more, in not letting the people go to sacrifice to the Lord.
30 Sa’an nan Musa ya rabu da Fir’auna, ya kuma yi addu’a ga Ubangiji,
So Moses went out from Pharao, and prayed to the Lord.
31 Ubangiji kuwa ya yi abin da Musa ya roƙa. Ƙudaje suka rabu da Fir’auna da fadawansa da kuma mutanensa; ba ƙudan da ya rage.
And he did according to his word: and he took away the flies from Pharao, and from his servants, and from his people: there was not left so much as one.
32 Amma a wannan lokaci ma, Fir’auna ya taurare zuciyarsa, bai kuma bar mutanen suka tafi ba.
And Pharao’s heart was hardened, so that neither this time would he let the people go.

< Fitowa 8 >