< Fitowa 8 >

1 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka je wurin Fir’auna, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka bar mutanena su tafi domin su yi mini sujada.
And Jehovah spoke to Moses, Go in to Pharaoh, and say to him, Thus says Jehovah, Let my people go, that they may serve me.
2 In ka ƙi barinsu, zan hore ka da annoban kwaɗi a dukan ƙasarka.
And if thou refuse to let them go, behold, I will smite all thy borders with frogs.
3 Nilu zai cika da kwaɗi. Za su haura zuwa cikin fadanka da kan gadonka, cikin gidajen bayinka da kan mutanenka, cikin kwanonin toye-toyenka da na cin abincinka.
And the river shall swarm with frogs, which shall go up and come into thy house, and into thy bedchamber, and upon thy bed, and into the house of thy servants, and upon thy people, and into thine ovens, and into thy kneading-troughs.
4 Kwaɗin nan za su yi ta tsalle a kanka, da kan mutanenka, da kuma kan dukan bayinka.’”
And the frogs shall come up both upon thee, and upon thy people, and upon all thy servants.
5 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ce wa Haruna, ‘Ka miƙa hannunka da sandanka bisa koguna da rafuffuka da kuma kududdufai, ka sa kwaɗi su fito su mamaye ƙasar Masar.’”
And Jehovah said to Moses, Say to Aaron, Stretch forth thy hand with thy rod over the rivers, over the streams, and over the pools, and cause frogs to come up upon the land of Egypt.
6 Sai Haruna ya miƙa hannunsa bisa ruwan Masar, kwaɗi kuwa suka fito, suka mamaye ƙasar Masar.
And Aaron stretched out his hand over the waters of Egypt, and the frogs came up, and covered the land of Egypt.
7 Amma bokaye ma suka yi abubuwan nan ta wurin sihirinsu; suka sa kwaɗi suka fito suka mamaye ƙasar Masar.
And the magicians did in like manner with their enchantments, and brought up frogs upon the land of Egypt.
8 Fir’auna ya kira Musa da Haruna ya ce, “Yi addu’a ga Ubangiji yă ɗauke kwaɗi daga gare ni da mutanena, zan kuwa bar mutanenku su tafi su yi hadaya ga Ubangiji.”
Then Pharaoh called for Moses and Aaron, and said, Entreat Jehovah, that he take away the frogs from me, and from my people, and I will let the people go, that they may sacrifice to Jehovah.
9 Musa ya ce wa Fir’auna, “Na ba ka dama ka ba da lokacin da zan yi addu’a dominka da kuma bayinka da mutanenka, gidajenku kuwa za su rabu da kwaɗi, amma ban da waɗanda suke cikin Nilu.”
And Moses said to Pharaoh, Have this honor over me: When shall I entreat for thee, and for thy servants, and for thy people, that the frogs be destroyed from thee and thy houses, and remain in the river only?
10 Fir’auna ya ce, “Gobe.” Musa ya amsa, “Za a yi kamar yadda ka faɗa, domin ka sani babu wani kamar Ubangiji, Allahnmu.
And he said, Tomorrow. And he said, Be it according to thy word, that thou may know that there is none like Jehovah our God.
11 Kwaɗin za su bar ka da gidajenka, bayinka da mutanenka; za su kasance a Nilu ne kaɗai.”
And the frogs shall depart from thee, and from thy houses, and from thy servants, and from thy people, they shall remain in the river only.
12 Bayan Musa da Haruna sun bar Fir’auna, Sai Musa ya yi kuka ga Ubangiji saboda kwaɗin da ya kawo a bisa Fir’auna.
And Moses and Aaron went out from Pharaoh. And Moses cried to Jehovah concerning the frogs which he had brought upon Pharaoh.
13 Sai Ubangiji ya yi abin da Musa ya nema. Kwaɗin suka mutu a gidaje, da filaye, da kuma gonaki.
And Jehovah did according to the word of Moses. And the frogs died out of the houses, out of the courts, and out of the fields.
14 Aka jibga su tsibi-tsibi, ƙasar ta yi ɗoyi saboda su.
And they gathered them together in heaps, and the land stank.
15 Amma da Fir’auna ya ga an sami sauƙi, sai ya taurare, ya ƙi yă saurari Musa da Haruna kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
But when Pharaoh saw that there was relief, he hardened his heart, and did not hearken to them, as Jehovah had spoken.
16 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ce wa Haruna, ‘Miƙa hannunka ka bugi ƙurar ƙasa,’ dukan ƙurar ƙasar Masar kuwa za tă zama ƙwari masu cizo.”
And Jehovah said to Moses, Say to Aaron, Stretch out thy rod, and smite the dust of the earth, that it may become lice throughout all the land of Egypt.
17 Suka yi haka, da Haruna ya miƙa hannunsa da sandan, ya bugi ƙurar ƙasa, sai ƙwari masu cizo suka fito a kan mutane da dabbobi. Dukan ƙurar, ko’ina a ƙasar Masar ta zama cinnaku.
And they did so. And Aaron stretched out his hand with his rod, and smote the dust of the earth. And there were lice upon man, and upon beast; all the dust of the earth became lice throughout all the land of Egypt.
18 Sa’ad da bokayen Fir’auna suka yi ƙoƙari yin sihiri iri na rufe ido domin su fito da kwari, sai suka kāsa. Ƙwari masu cizo kuwa suka rufe mutane da dabbobi.
And the magicians did so with their enchantments to bring forth lice, but they could not. And there were lice upon man, and upon beast.
19 Sai bokaye suka ce wa Fir’auna, “Wannan fa da hannun Allah a ciki.” Amma zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa saurara ba, kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
Then the magicians said to Pharaoh, This is the finger of God. And Pharaoh's heart was hardened, and he did not hearken to them, as Jehovah had spoken.
20 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka tashi da sassafe ka sadu da Fir’auna a lokacin da za shi kogi, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, bari mutanena su tafi, don su yi mini sujada.
And Jehovah said to Moses, Rise up early in the morning, and stand before Pharaoh. Lo, he comes forth to the water. And say to him, Thus says Jehovah, Let my people go, that they may serve me.
21 In ba ka bar mutanena suka tafi ba, zan turo da tarin ƙuda a kanka da bayinka, a kan mutanenka da cikin gidajenka. Gidajen Masarawa za su cika da ƙudaje, har ma da ƙasa inda za su taka.
Else, if thou will not let my people go, behold, I will send swarms of flies upon thee, and upon they servants, and upon thy people, and into thy houses. And the houses of the Egyptians shall be full of swarms of flies, and also the ground on which they are.
22 “‘Amma zan keɓe yankin Goshen, inda mutanena suke don kada ƙudaje su taɓa wurin, domin ka sani cewa Ni, Ubangiji, ina cikin wannan ƙasa.
And in that day I will set apart the land of Goshen, in which my people dwell, that no swarms of flies shall be there, to the end thou may know that I am Jehovah in the midst of the earth.
23 Zan sa iyaka tsakanin jama’ata da jama’arka. Gobe ne wannan mu’ujiza za tă auku.’”
And I will put a division between my people and thy people. This sign shall be by tomorrow.
24 Ubangiji kuwa ya yi haka. Tarin ƙuda suka zubo a fadar Fir’auna da cikin gidajen bayinsa, da ko’ina a Masar, ƙasar kuwa ta lalace saboda ƙudaje.
And Jehovah did so, and there came grievous swarms of flies into the house of Pharaoh, and into his servants' houses. And in all the land of Egypt the land was corrupted because of the swarms of flies.
25 Sai Fir’auna ya kira Musa da Haruna ya ce, “Ku tafi, ku miƙa hadaya ga Allahnku, a nan a cikin ƙasar.”
And Pharaoh called for Moses and for Aaron, and said, Go ye, sacrifice to your God in the land.
26 Amma Musa ya ce, “Wannan ba zai yiwu ba. Hadayun da mukan miƙa wa Ubangiji, Allahnmu haram ne ga Masarawa. In kuwa muka miƙa hadayun da suke haram a idanunsu, ba za su jajjefe mu ba?
And Moses said, It is not right to do so, for we shall sacrifice the abomination of the Egyptians to Jehovah our God. Lo, shall we sacrifice the abomination of the Egyptians before their eyes, and will they not stone us?
27 Dole mu yi tafiya kwana uku cikin hamada domin miƙa hadayu ga Ubangiji Allahnmu, yadda ya umarce mu.”
We will go three days' journey into the wilderness, and sacrifice to Jehovah our God, as he shall command us.
28 Fir’auna ya ce, “Zan bar ku ku tafi, don ku miƙa hadayu ga Ubangiji Allahnku, a cikin hamada, amma ba za ku tafi da nisa ba. Yanzu ku yi mini addu’a.”
And Pharaoh said, I will let you go, that ye may sacrifice to Jehovah your God in the wilderness, only ye shall not go very far away. Entreat for me.
29 Musa ya amsa, “Da zarar na bar ka, zan yi addu’a ga Ubangiji, gobe kuwa ƙudaje za su bar Fir’auna da fadawansa da kuma mutanensa. Sai dai a tabbata Fir’auna bai sāke yin ruɗi ta wurin ƙin barin mutane su tafi su miƙa hadayu ga Ubangiji ba.”
And Moses said, Behold, I go out from thee, and I will entreat Jehovah that the swarms of flies may depart from Pharaoh, from his servants, and from his people, tomorrow. Only let not Pharaoh deal deceitfully any more in not letting the people go to sacrifice to Jehovah.
30 Sa’an nan Musa ya rabu da Fir’auna, ya kuma yi addu’a ga Ubangiji,
And Moses went out from Pharaoh, and entreated Jehovah.
31 Ubangiji kuwa ya yi abin da Musa ya roƙa. Ƙudaje suka rabu da Fir’auna da fadawansa da kuma mutanensa; ba ƙudan da ya rage.
And Jehovah did according to the word of Moses, and he removed the swarms of flies from Pharaoh, from his servants, and from his people; there remained not one.
32 Amma a wannan lokaci ma, Fir’auna ya taurare zuciyarsa, bai kuma bar mutanen suka tafi ba.
And Pharaoh hardened his heart this time also, and he did not let the people go.

< Fitowa 8 >