< Fitowa 7 >
1 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Duba, na maishe ka kamar Allah ga Fir’auna, ɗan’uwanka Haruna kuma zai zama annabinka.
Et le Seigneur dit à Moïse: Voilà que je t’ai établi le Dieu de Pharaon, et Aaron ton frère sera ton prophète.
2 Za ka faɗi kome da na umarce ka, ɗan’uwanka Haruna kuwa zai faɗa wa Fir’auna, yă bar Isra’ilawa su fita daga ƙasarsa.
Toi, tu lui diras tout ce que je t’ordonne, et lui parlera à Pharaon, afin qu’il laisse les enfants d’Israël s’en aller de son pays.
3 Amma zan taurare zuciyar Fir’auna, kuma ko da na ninka mu’ujizai da kuma alamu a Masar,
Mais moi j’endurcirai son cœur, et je multiplierai mes signes et mes prodiges dans la terre d’Egypte.
4 ba zai saurare ku ba. Don haka zan miƙa hannuna a kan Masar, in murƙushe ta da bala’i iri-iri, bayan haka zan fitar da taron mutanen Isra’ila daga ƙasar Masar ta wurin hukuntaina masu girma.
Et il ne vous écoutera point: et je lancerai ma main sur l’Egypte, et je retirerai mon armée et mon peuple, les enfants d’Israël, de la terre d’Egypte par de très grands jugements.
5 Masarawa kuwa za su san cewa ni ne Ubangiji sa’ad da na miƙa hannuna a kan Masar, na kuma fitar da Isra’ilawa daga gare ta.”
Et les Egyptiens sauront que c’est moi le Seigneur qui aurai étendu ma main sur l’Egypte, et retiré les enfants d’Israël du milieu d’eux.
6 Musa da Haruna suka aikata yadda Ubangiji ya umarce su.
C’est pourquoi Moïse et Aaron firent comme avait ordonné le Seigneur: ainsi agirent-ils.
7 Musa yana da shekara tamanin da haihuwa, Haruna kuma yana da shekara tamanin da uku, sa’ad da suka yi magana da Fir’auna.
Or Moïse avait quatre-vingts ans et Aaron quatre-vingt-trois, quand ils parlèrent à Pharaon.
8 Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
Et le Seigneur dit à Moïse et à Aaron:
9 “Sa’ad da Fir’auna ya ce muku, ‘Aikata wani al’ajabi,’ sai ka ce wa Haruna, ‘Ɗauki sandanka ka jefa shi a ƙasa, a gaban Fir’auna,’ zai kuwa zama maciji.”
Quand Pharaon vous dira: Montrez des signes, tu diras à Aaron: Prends ta verge et jette-la devant Pharaon; et elle sera changée en serpent.
10 Sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir’auna, suka yi yadda Ubangiji ya umarce su. Haruna ya jefa sandansa ƙasa, a gaban Fir’auna da bayinsa, sai sandan ya zama maciji.
Moïse donc et Aaron, étant entrés auprès de Pharaon, firent comme avait ordonné le Seigneur: Aaron jeta la verge devant Pharaon et ses serviteurs, et elle fut changée en serpent.
11 Fir’auna kuwa ya kira masu hikima da masu sihiri, sai bokayen Masarawa ma suka yi irin abubuwan nan da bokancinsu.
Mais Pharaon appela les sages et les magiciens; et ils firent eux aussi pareillement par les enchantements égyptiens et par certains secrets.
12 Kowannensu ya jefa sandansa ƙasa, ya kuwa zama maciji. Amma sandan Haruna ya haɗiye sandunansu.
Ils jetèrent chacun leur verge, et elles furent changées en serpents; mais la verge d’Aaron dévora leurs verges.
13 Duk da haka zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa saurare su ba, kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
Et le cœur de Pharaon s’endurcit, et il n’écouta point Moïse et Aaron, comme avait ordonné le Seigneur.
14 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Zuciyar Fir’auna taurariya ce, ya ƙi yă bar mutanen su tafi.
Or le Seigneur dit à Moïse: Le cœur de Pharaon s’est endurci; il ne veut pas laisser aller le peuple.
15 Ka je wurin Fir’auna da safe, yayinda za shi kogi. Ka jira a bakin Nilu don ka sadu da shi, ka ɗauki sandan nan da ya canja zuwa maciji a hannunka.
Va vers lui dès le matin; voilà qu’il sortira pour aller vers l’eau; et tu te présenteras à sa rencontre sur la rive du fleuve: et la verge qui a été changée en serpent, tu la prendras en ta main,
16 Sa’an nan ka ce masa, ‘Ubangiji, Allah na Ibraniyawa, ya aiko ni in faɗa maka, Ka bar mutanena su tafi domin su yi mini sujada a hamada. Amma har yanzu ba ka yi biyayya ba.
Et tu diras à Pharaon: Le Seigneur Dieu des Hébreux m’a envoyé vers toi, disant: Laisse aller mon peuple afin qu’il me sacrifie dans le désert, et jusqu’à présent tu n’as pas voulu écouter.
17 Ga abin da Ubangiji ya ce, da wannan za ka san cewa ni ne Ubangiji. Da sandan da yake hannuna zan bugi ruwan Nilu, zai kuma zama jini.
Voici donc ce que dit le Seigneur: En ceci tu sauras que je suis le Seigneur: voici que je frapperai de la verge qui est en ma main l’eau du fleuve, et elle sera changée en sang.
18 Kifi a ciki Nilu za su mutu, ruwan kuma zai yi ɗoyi; Masarawa ba za su iya shan ruwansa ba.’”
Les poissons même qui sont dans le fleuve mourront; et les eaux se corrompront, et les Egyptiens qui boiront de l’eau du fleuve, souffriront beaucoup.
19 Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ce wa Haruna, ‘Ka ɗauki sandanka, ka miƙa hannunka kan ruwan Masar, kan kogunansu da rafuffukansu da kududdufansu da kuma dukan tafkunansu, za su zama jini.’ Jini zai kasance ko’ina a Masar, har ma a cikin abubuwan ajiyar ruwansu da aka yi da itace da kuma dutse.”
Le Seigneur dit aussi à Moïse: Dis à Aaron: Prends ta verge, et étends ta main sur les eaux de l’Egypte, et sur leurs fleuves, et sur les ruisseaux et les marais, et sur tous les lacs des eaux, afin qu’ils soient changés en sang, et qu’il y ait ainsi du sang dans toute la terre d’Egypte, tant dans les vases de bois que dans les vases de pierre.
20 Musa da Haruna suka yi yadda Ubangiji ya umarta. Ya ɗaga sandansa a gaban Fir’auna da bayinsa, ya bugi ruwan Nilu, dukan ruwan kuwa ya zama jini.
Et Moïse et Aaron firent comme l’avait ordonné le Seigneur; et Aaron levant sa verge, frappa l’eau du fleuve devant Pharaon et ses serviteurs, et elle fut changée en sang.
21 Kifin da suke cikin Nilu suka mutu, kogin kuwa ya yi wari sosai yadda Masarawa ba su iya shan ruwan ba. Jini ya bazu ko’ina a Masar.
Et les poissons qui étaient dans le fleuve moururent; le fleuve se corrompit, et les Egyptiens ne pouvaient boire de l’eau du fleuve: et il y eut du sang dans toute la terre d’Egypte.
22 Amma bokayen Masar ma suka yi abubuwan nan da sihirinsu, sai zuciyar Fir’auna ta taurare; bai saurari Musa da Haruna ba, kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
Les magiciens d’Egypte firent pareillement par leurs enchantements, et le cœur de Pharaon s’endurcit, et il n’écouta pas Moïse et Aaron, comme avait ordonné le Seigneur.
23 A maimakon yă saurara, sai ya juya ya koma fadarsa, bai ma damu da abin da aka yi ba.
Il se retira et il entra en sa maison, et ne prit pas la chose à cœur encore cette fois.
24 Sai dukan Masarawa suka yi ta tonon gefen Nilu don su sami ruwan sha, domin ba su iya shan ruwan kogin ba.
Or tous les Egyptiens creusèrent autour du fleuve pour trouver de l’eau à boire; car ils ne pouvaient boire de l’eau du fleuve.
25 Kwana bakwai suka wuce bayan da Ubangiji ya bugi kogin.
Et il se passa sept jours entiers, après que le Seigneur eut frappé le fleuve.