< Fitowa 7 >
1 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Duba, na maishe ka kamar Allah ga Fir’auna, ɗan’uwanka Haruna kuma zai zama annabinka.
And the Lord seide to Moises, Lo! Y haue maad thee the god of Farao; and Aaron, thi brother, schal be thi prophete.
2 Za ka faɗi kome da na umarce ka, ɗan’uwanka Haruna kuwa zai faɗa wa Fir’auna, yă bar Isra’ilawa su fita daga ƙasarsa.
Thou schalt speke to Aaron alle thingis whiche Y comaunde to thee, and he schal speke to Farao, that he delyuere the sones of Israel fro his hond.
3 Amma zan taurare zuciyar Fir’auna, kuma ko da na ninka mu’ujizai da kuma alamu a Masar,
But Y schal make hard his herte, and Y schal multiplie my signes and merueils in the lond of Egipt, and he schal not here you;
4 ba zai saurare ku ba. Don haka zan miƙa hannuna a kan Masar, in murƙushe ta da bala’i iri-iri, bayan haka zan fitar da taron mutanen Isra’ila daga ƙasar Masar ta wurin hukuntaina masu girma.
and Y schal sende myn hond on Egipt, and Y schal lede out myn oost, and my puple, the sones of Israel, fro the lond of Egipt bi mooste domes;
5 Masarawa kuwa za su san cewa ni ne Ubangiji sa’ad da na miƙa hannuna a kan Masar, na kuma fitar da Isra’ilawa daga gare ta.”
and Egipcians schulen wite, that Y am the Lord, which haue holde forth myn hond on Egipt, and haue led out of the myddis of hem the sones of Israel.
6 Musa da Haruna suka aikata yadda Ubangiji ya umarce su.
And so Moises dide and Aaron; as the Lord comaundide, so thei diden.
7 Musa yana da shekara tamanin da haihuwa, Haruna kuma yana da shekara tamanin da uku, sa’ad da suka yi magana da Fir’auna.
Forsothe Moyses was of fourescoor yeer, and Aaron was of fourescoor yeer and thre, whanne thei spaken to Farao.
8 Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
And the Lord seide to Moises and to Aaron,
9 “Sa’ad da Fir’auna ya ce muku, ‘Aikata wani al’ajabi,’ sai ka ce wa Haruna, ‘Ɗauki sandanka ka jefa shi a ƙasa, a gaban Fir’auna,’ zai kuwa zama maciji.”
Whanne Farao schal seie to you, Schewe ye signes to vs, thou schalt seie to Aaron, Take thi yerde, and caste forth it before Farao, and be it turned into a serpent.
10 Sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir’auna, suka yi yadda Ubangiji ya umarce su. Haruna ya jefa sandansa ƙasa, a gaban Fir’auna da bayinsa, sai sandan ya zama maciji.
And so Moises and Aaron entriden to Farao, and diden as the Lord comaundide; and Aaron took the yeerde, and castide forth bifore Farao and hise seruauntis, which yerde was turned in to a serpent.
11 Fir’auna kuwa ya kira masu hikima da masu sihiri, sai bokayen Masarawa ma suka yi irin abubuwan nan da bokancinsu.
Forsothe Farao clepide wise men, and witchis, and thei also diden bi enchauntementis of Egipt, and bi summe priuy thingis in lijk maner;
12 Kowannensu ya jefa sandansa ƙasa, ya kuwa zama maciji. Amma sandan Haruna ya haɗiye sandunansu.
and alle castiden forth her yerdis, whiche weren turned in to dragouns; but the yerde of Aaron deuouride `the yerdis of hem.
13 Duk da haka zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa saurare su ba, kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
And the herte of Farao was maad hard, and he herde not hem, as the Lord comaundide.
14 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Zuciyar Fir’auna taurariya ce, ya ƙi yă bar mutanen su tafi.
Forsothe the Lord seide to Moyses, The herte of Farao is maad greuouse, he nyle delyuere the puple;
15 Ka je wurin Fir’auna da safe, yayinda za shi kogi. Ka jira a bakin Nilu don ka sadu da shi, ka ɗauki sandan nan da ya canja zuwa maciji a hannunka.
go thou to hym eerli; lo! he schal go out to the watris, and thou schalt stonde in the comyng of hym on the brynke of the flood; and thou schalt take in thin honde the yerde, that was turned into a dragoun,
16 Sa’an nan ka ce masa, ‘Ubangiji, Allah na Ibraniyawa, ya aiko ni in faɗa maka, Ka bar mutanena su tafi domin su yi mini sujada a hamada. Amma har yanzu ba ka yi biyayya ba.
and thou schalt seie to hym, The Lord God of Ebrews sente me to thee, and seide, Delyuere thou my puple, that it make sacrifice to me in desert; til to present time thou noldist here.
17 Ga abin da Ubangiji ya ce, da wannan za ka san cewa ni ne Ubangiji. Da sandan da yake hannuna zan bugi ruwan Nilu, zai kuma zama jini.
Therfor the Lord seith these thingis, In this thou schalt wite, that Y am the Lord; lo! Y schal smyte with the yerde, which is in myn hond, the watir of the flood, and it schal be turned in to blood;
18 Kifi a ciki Nilu za su mutu, ruwan kuma zai yi ɗoyi; Masarawa ba za su iya shan ruwansa ba.’”
and the fischis that ben in the flood schulen die; and the watris schulen wexe rotun, and Egipcians drynkynge the watir of the flood schulen be turmentid.
19 Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ce wa Haruna, ‘Ka ɗauki sandanka, ka miƙa hannunka kan ruwan Masar, kan kogunansu da rafuffukansu da kududdufansu da kuma dukan tafkunansu, za su zama jini.’ Jini zai kasance ko’ina a Masar, har ma a cikin abubuwan ajiyar ruwansu da aka yi da itace da kuma dutse.”
Also the Lord seide to Moises, Seie thou to Aaron, Take thi yerde, and holde forth thin hond on the watris of Egipt, and on the flodis of hem, and on the stremys `of hem, and on the mareis, and alle lakis of watris, that tho be turned in to blood; and blood be in al the lond of Egipt, as wel in vessils of tree as of stoon.
20 Musa da Haruna suka yi yadda Ubangiji ya umarta. Ya ɗaga sandansa a gaban Fir’auna da bayinsa, ya bugi ruwan Nilu, dukan ruwan kuwa ya zama jini.
And Moises and Aaron diden so, as the Lord comaundide; and Aaron reiside the yerde, and smoot the watir of the flood bifore Farao and hise seruauntis, which watir was turned in to blood;
21 Kifin da suke cikin Nilu suka mutu, kogin kuwa ya yi wari sosai yadda Masarawa ba su iya shan ruwan ba. Jini ya bazu ko’ina a Masar.
and fischis, that weren in the flood, dieden; and the flood was rotun, and Egipcians myyten not drynke the water of the flood; and blood was in al the lond of Egipt.
22 Amma bokayen Masar ma suka yi abubuwan nan da sihirinsu, sai zuciyar Fir’auna ta taurare; bai saurari Musa da Haruna ba, kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
And the witchis of Egipcians diden in lijk maner by her enchauntementis; and the herte of Farao was maad hard, and he herde not hem, as the Lord comaundide.
23 A maimakon yă saurara, sai ya juya ya koma fadarsa, bai ma damu da abin da aka yi ba.
And he turnede awei hym silf, and entride in to his hows, nethir he took it to herte, yhe, in this tyme.
24 Sai dukan Masarawa suka yi ta tonon gefen Nilu don su sami ruwan sha, domin ba su iya shan ruwan kogin ba.
Forsothe alle Egipcians diggiden watir `bi the cumpas of the flood, to drinke; for thei myyten not drynke of the `watir of the flood.
25 Kwana bakwai suka wuce bayan da Ubangiji ya bugi kogin.
And seuene daies weren fillid, aftir that the Lord smoot the flood.