< Fitowa 7 >
1 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Duba, na maishe ka kamar Allah ga Fir’auna, ɗan’uwanka Haruna kuma zai zama annabinka.
And the LORD said to Moses, See, I have made you a god to Pharaoh: and Aaron your brother shall be your prophet.
2 Za ka faɗi kome da na umarce ka, ɗan’uwanka Haruna kuwa zai faɗa wa Fir’auna, yă bar Isra’ilawa su fita daga ƙasarsa.
You shall speak all that I command you: and Aaron your brother shall speak to Pharaoh, that he send the children of Israel out of his land.
3 Amma zan taurare zuciyar Fir’auna, kuma ko da na ninka mu’ujizai da kuma alamu a Masar,
And I will harden Pharaoh’s heart, and multiply my signs and my wonders in the land of Egypt.
4 ba zai saurare ku ba. Don haka zan miƙa hannuna a kan Masar, in murƙushe ta da bala’i iri-iri, bayan haka zan fitar da taron mutanen Isra’ila daga ƙasar Masar ta wurin hukuntaina masu girma.
But Pharaoh shall not listen to you, that I may lay my hand on Egypt, and bring forth my armies, and my people the children of Israel, out of the land of Egypt by great judgments.
5 Masarawa kuwa za su san cewa ni ne Ubangiji sa’ad da na miƙa hannuna a kan Masar, na kuma fitar da Isra’ilawa daga gare ta.”
And the Egyptians shall know that I am the LORD, when I stretch forth my hand on Egypt, and bring out the children of Israel from among them.
6 Musa da Haruna suka aikata yadda Ubangiji ya umarce su.
And Moses and Aaron did as the LORD commanded them, so did they.
7 Musa yana da shekara tamanin da haihuwa, Haruna kuma yana da shekara tamanin da uku, sa’ad da suka yi magana da Fir’auna.
And Moses was fourscore years old, and Aaron fourscore and three years old, when they spoke to Pharaoh.
8 Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
And the LORD spoke to Moses and to Aaron, saying,
9 “Sa’ad da Fir’auna ya ce muku, ‘Aikata wani al’ajabi,’ sai ka ce wa Haruna, ‘Ɗauki sandanka ka jefa shi a ƙasa, a gaban Fir’auna,’ zai kuwa zama maciji.”
When Pharaoh shall speak to you, saying, Show a miracle for you: then you shall say to Aaron, Take your rod, and cast it before Pharaoh, and it shall become a serpent.
10 Sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir’auna, suka yi yadda Ubangiji ya umarce su. Haruna ya jefa sandansa ƙasa, a gaban Fir’auna da bayinsa, sai sandan ya zama maciji.
And Moses and Aaron went in to Pharaoh, and they did so as the LORD had commanded: and Aaron cast down his rod before Pharaoh, and before his servants, and it became a serpent.
11 Fir’auna kuwa ya kira masu hikima da masu sihiri, sai bokayen Masarawa ma suka yi irin abubuwan nan da bokancinsu.
Then Pharaoh also called the wise men and the sorcerers: now the magicians of Egypt, they also did in like manner with their enchantments.
12 Kowannensu ya jefa sandansa ƙasa, ya kuwa zama maciji. Amma sandan Haruna ya haɗiye sandunansu.
For they cast down every man his rod, and they became serpents: but Aaron’s rod swallowed up their rods.
13 Duk da haka zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa saurare su ba, kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
And he hardened Pharaoh’s heart, that he listened not to them; as the LORD had said.
14 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Zuciyar Fir’auna taurariya ce, ya ƙi yă bar mutanen su tafi.
And the LORD said to Moses, Pharaoh’s heart is hardened, he refuses to let the people go.
15 Ka je wurin Fir’auna da safe, yayinda za shi kogi. Ka jira a bakin Nilu don ka sadu da shi, ka ɗauki sandan nan da ya canja zuwa maciji a hannunka.
Get you to Pharaoh in the morning; see, he goes out to the water; and you shall stand by the river’s brink against he come; and the rod which was turned to a serpent shall you take in your hand.
16 Sa’an nan ka ce masa, ‘Ubangiji, Allah na Ibraniyawa, ya aiko ni in faɗa maka, Ka bar mutanena su tafi domin su yi mini sujada a hamada. Amma har yanzu ba ka yi biyayya ba.
And you shall say to him, The LORD God of the Hebrews has sent me to you, saying, Let my people go, that they may serve me in the wilderness: and, behold, till now you would not hear.
17 Ga abin da Ubangiji ya ce, da wannan za ka san cewa ni ne Ubangiji. Da sandan da yake hannuna zan bugi ruwan Nilu, zai kuma zama jini.
Thus says the LORD, In this you shall know that I am the LORD: behold, I will smite with the rod that is in my hand on the waters which are in the river, and they shall be turned to blood.
18 Kifi a ciki Nilu za su mutu, ruwan kuma zai yi ɗoyi; Masarawa ba za su iya shan ruwansa ba.’”
And the fish that is in the river shall die, and the river shall stink; and the Egyptians shall loathe to drink of the water of the river.
19 Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ce wa Haruna, ‘Ka ɗauki sandanka, ka miƙa hannunka kan ruwan Masar, kan kogunansu da rafuffukansu da kududdufansu da kuma dukan tafkunansu, za su zama jini.’ Jini zai kasance ko’ina a Masar, har ma a cikin abubuwan ajiyar ruwansu da aka yi da itace da kuma dutse.”
And the LORD spoke to Moses, Say to Aaron, Take your rod, and stretch out your hand on the waters of Egypt, on their streams, on their rivers, and on their ponds, and on all their pools of water, that they may become blood; and that there may be blood throughout all the land of Egypt, both in vessels of wood, and in vessels of stone.
20 Musa da Haruna suka yi yadda Ubangiji ya umarta. Ya ɗaga sandansa a gaban Fir’auna da bayinsa, ya bugi ruwan Nilu, dukan ruwan kuwa ya zama jini.
And Moses and Aaron did so, as the LORD commanded; and he lifted up the rod, and smote the waters that were in the river, in the sight of Pharaoh, and in the sight of his servants; and all the waters that were in the river were turned to blood.
21 Kifin da suke cikin Nilu suka mutu, kogin kuwa ya yi wari sosai yadda Masarawa ba su iya shan ruwan ba. Jini ya bazu ko’ina a Masar.
And the fish that was in the river died; and the river stank, and the Egyptians could not drink of the water of the river; and there was blood throughout all the land of Egypt.
22 Amma bokayen Masar ma suka yi abubuwan nan da sihirinsu, sai zuciyar Fir’auna ta taurare; bai saurari Musa da Haruna ba, kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
And the magicians of Egypt did so with their enchantments: and Pharaoh’s heart was hardened, neither did he listen to them; as the LORD had said.
23 A maimakon yă saurara, sai ya juya ya koma fadarsa, bai ma damu da abin da aka yi ba.
And Pharaoh turned and went into his house, neither did he set his heart to this also.
24 Sai dukan Masarawa suka yi ta tonon gefen Nilu don su sami ruwan sha, domin ba su iya shan ruwan kogin ba.
And all the Egyptians dig round about the river for water to drink; for they could not drink of the water of the river.
25 Kwana bakwai suka wuce bayan da Ubangiji ya bugi kogin.
And seven days were fulfilled, after that the LORD had smitten the river.