< Fitowa 7 >

1 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Duba, na maishe ka kamar Allah ga Fir’auna, ɗan’uwanka Haruna kuma zai zama annabinka.
And the Lord said to Moses, See I have made you a god to Pharaoh, and Aaron your brother will be your prophet.
2 Za ka faɗi kome da na umarce ka, ɗan’uwanka Haruna kuwa zai faɗa wa Fir’auna, yă bar Isra’ilawa su fita daga ƙasarsa.
Say whatever I give you orders to say: and Aaron your brother will give word to Pharaoh to let the children of Israel go out of his land.
3 Amma zan taurare zuciyar Fir’auna, kuma ko da na ninka mu’ujizai da kuma alamu a Masar,
And I will make Pharaoh's heart hard, and my signs and wonders will be increased in the land of Egypt.
4 ba zai saurare ku ba. Don haka zan miƙa hannuna a kan Masar, in murƙushe ta da bala’i iri-iri, bayan haka zan fitar da taron mutanen Isra’ila daga ƙasar Masar ta wurin hukuntaina masu girma.
But Pharaoh will not give ear to you, and I will put my hand on Egypt, and take my armies, my people, the children of Israel, out of Egypt, after great punishments.
5 Masarawa kuwa za su san cewa ni ne Ubangiji sa’ad da na miƙa hannuna a kan Masar, na kuma fitar da Isra’ilawa daga gare ta.”
And the Egyptians will see that I am the Lord, when my hand is stretched out over Egypt, and I take the children of Israel out from among them.
6 Musa da Haruna suka aikata yadda Ubangiji ya umarce su.
And Moses and Aaron did so: as the Lord gave them orders, so they did.
7 Musa yana da shekara tamanin da haihuwa, Haruna kuma yana da shekara tamanin da uku, sa’ad da suka yi magana da Fir’auna.
And Moses was eighty years old, and Aaron eighty-three years old, when they gave the Lord's word to Pharaoh.
8 Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
And the Lord said to Moses and Aaron,
9 “Sa’ad da Fir’auna ya ce muku, ‘Aikata wani al’ajabi,’ sai ka ce wa Haruna, ‘Ɗauki sandanka ka jefa shi a ƙasa, a gaban Fir’auna,’ zai kuwa zama maciji.”
If Pharaoh says to you, Let me see a wonder: then say to Aaron, Take your rod and put it down on the earth before Pharaoh so that it may become a snake.
10 Sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir’auna, suka yi yadda Ubangiji ya umarce su. Haruna ya jefa sandansa ƙasa, a gaban Fir’auna da bayinsa, sai sandan ya zama maciji.
Then Moses and Aaron went in to Pharaoh and they did as the Lord had said: and Aaron put his rod down on the earth before Pharaoh and his servants, and it became a snake.
11 Fir’auna kuwa ya kira masu hikima da masu sihiri, sai bokayen Masarawa ma suka yi irin abubuwan nan da bokancinsu.
Then Pharaoh sent for the wise men and the wonder-workers, and they, the wonder-workers of Egypt, did the same with their secret arts.
12 Kowannensu ya jefa sandansa ƙasa, ya kuwa zama maciji. Amma sandan Haruna ya haɗiye sandunansu.
For every one of them put down his rod on the earth, and they became snakes: but Aaron's rod made a meal of their rods.
13 Duk da haka zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa saurare su ba, kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
But Pharaoh's heart was made hard, and he did not give ear to them, as the Lord had said.
14 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Zuciyar Fir’auna taurariya ce, ya ƙi yă bar mutanen su tafi.
And the Lord said to Moses and Aaron, Pharaoh's heart is unchanged; he will not let the people go.
15 Ka je wurin Fir’auna da safe, yayinda za shi kogi. Ka jira a bakin Nilu don ka sadu da shi, ka ɗauki sandan nan da ya canja zuwa maciji a hannunka.
Go to Pharaoh in the morning; when he goes out to the water, you will be waiting for him by the edge of the Nile, with the rod which was turned into a snake in your hand;
16 Sa’an nan ka ce masa, ‘Ubangiji, Allah na Ibraniyawa, ya aiko ni in faɗa maka, Ka bar mutanena su tafi domin su yi mini sujada a hamada. Amma har yanzu ba ka yi biyayya ba.
And say to him, The Lord, the God of the Hebrews, has sent me to you, saying, Let my people go so that they may give me worship in the waste land; but up to now you have not given ear to his words.
17 Ga abin da Ubangiji ya ce, da wannan za ka san cewa ni ne Ubangiji. Da sandan da yake hannuna zan bugi ruwan Nilu, zai kuma zama jini.
So the Lord says, By this you may be certain that I am the Lord; see, by the touch of this rod in my hand the waters of the Nile will be turned to blood;
18 Kifi a ciki Nilu za su mutu, ruwan kuma zai yi ɗoyi; Masarawa ba za su iya shan ruwansa ba.’”
And the fish in the Nile will come to destruction, and the river will send up a bad smell, and the Egyptians will not be able, for disgust, to make use of the water of the Nile for drinking.
19 Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ce wa Haruna, ‘Ka ɗauki sandanka, ka miƙa hannunka kan ruwan Masar, kan kogunansu da rafuffukansu da kududdufansu da kuma dukan tafkunansu, za su zama jini.’ Jini zai kasance ko’ina a Masar, har ma a cikin abubuwan ajiyar ruwansu da aka yi da itace da kuma dutse.”
And the Lord said, Say to Aaron, Let the rod in your hand be stretched out over the waters of Egypt, and over the rivers and the streams and the pools, and over every stretch of water, so that they may be turned to blood; and there will be blood through all the land of Egypt, in vessels of wood and in vessels of stone.
20 Musa da Haruna suka yi yadda Ubangiji ya umarta. Ya ɗaga sandansa a gaban Fir’auna da bayinsa, ya bugi ruwan Nilu, dukan ruwan kuwa ya zama jini.
And Moses and Aaron did as the Lord had said; and when his rod had been lifted up and stretched out over the waters of the Nile before the eyes of Pharaoh and his servants, all the water in the Nile was turned to blood;
21 Kifin da suke cikin Nilu suka mutu, kogin kuwa ya yi wari sosai yadda Masarawa ba su iya shan ruwan ba. Jini ya bazu ko’ina a Masar.
And the fish in the Nile came to destruction, and a bad smell went up from the river, and the Egyptians were not able to make use of the water of the Nile for drinking; and there was blood through all the land of Egypt.
22 Amma bokayen Masar ma suka yi abubuwan nan da sihirinsu, sai zuciyar Fir’auna ta taurare; bai saurari Musa da Haruna ba, kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
And the wonder-workers of Egypt did the same with their secret arts: but Pharaoh's heart was made hard, and he would not give ear to them, as the Lord had said.
23 A maimakon yă saurara, sai ya juya ya koma fadarsa, bai ma damu da abin da aka yi ba.
Then Pharaoh went into his house, and did not take even this to heart.
24 Sai dukan Masarawa suka yi ta tonon gefen Nilu don su sami ruwan sha, domin ba su iya shan ruwan kogin ba.
And all the Egyptians made holes round about the Nile to get drinking-water, for they were not able to make use of the Nile water.
25 Kwana bakwai suka wuce bayan da Ubangiji ya bugi kogin.
And seven days went past, after the Lord had put his hand on the Nile.

< Fitowa 7 >