< Fitowa 7 >
1 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Duba, na maishe ka kamar Allah ga Fir’auna, ɗan’uwanka Haruna kuma zai zama annabinka.
I řekl Hospodin Mojžíšovi: Aj, ustanovil jsem tě za Boha Faraonovi; Aron pak bratr tvůj bude prorokem tvým.
2 Za ka faɗi kome da na umarce ka, ɗan’uwanka Haruna kuwa zai faɗa wa Fir’auna, yă bar Isra’ilawa su fita daga ƙasarsa.
Ty mluviti budeš všecko, což tobě přikáži; Aron pak bratr tvůj mluviti bude k Faraonovi, aby propustil syny Izraelské z země své.
3 Amma zan taurare zuciyar Fir’auna, kuma ko da na ninka mu’ujizai da kuma alamu a Masar,
Ale jáť zatvrdím srdce Faraonovo, a množiti budu znamení svá a zázraky své v zemi Egyptské.
4 ba zai saurare ku ba. Don haka zan miƙa hannuna a kan Masar, in murƙushe ta da bala’i iri-iri, bayan haka zan fitar da taron mutanen Isra’ila daga ƙasar Masar ta wurin hukuntaina masu girma.
Aniž poslechne vás Farao. I vzložím ruku svou na Egypt, a vyvedu vojska svá, lid svůj, syny Izraelské, z země Egyptské skrze soudy veliké.
5 Masarawa kuwa za su san cewa ni ne Ubangiji sa’ad da na miƙa hannuna a kan Masar, na kuma fitar da Isra’ilawa daga gare ta.”
I zvědíť Egyptští, že já jsem Hospodin, když vztáhnu ruku svou na Egypt; a vyvedu syny Izraelské z prostředku jich.
6 Musa da Haruna suka aikata yadda Ubangiji ya umarce su.
Tedy učinil Mojžíš a Aron tak; jakž přikázal jim Hospodin, tak učinili.
7 Musa yana da shekara tamanin da haihuwa, Haruna kuma yana da shekara tamanin da uku, sa’ad da suka yi magana da Fir’auna.
A byl Mojžíš v osmdesáti, Aron pak v osmdesáti a třech letech, když mluvili s Faraonem.
8 Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
I řekl Hospodin Mojžíšovi a Aronovi takto:
9 “Sa’ad da Fir’auna ya ce muku, ‘Aikata wani al’ajabi,’ sai ka ce wa Haruna, ‘Ɗauki sandanka ka jefa shi a ƙasa, a gaban Fir’auna,’ zai kuwa zama maciji.”
Když mluviti k vám bude Farao, řka: Ukažte od sebe zázrak, tedy díš Aronovi: Vezmi hůl svou, a povrz před Faraonem, i obrátí se v hada.
10 Sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir’auna, suka yi yadda Ubangiji ya umarce su. Haruna ya jefa sandansa ƙasa, a gaban Fir’auna da bayinsa, sai sandan ya zama maciji.
Tedy všel Mojžíš s Aronem k Faraonovi, a učinili tak, jakž přikázal Hospodin; a povrhl Aron hůl svou před Faraonem i před služebníky jeho, a obrácena jest v hada.
11 Fir’auna kuwa ya kira masu hikima da masu sihiri, sai bokayen Masarawa ma suka yi irin abubuwan nan da bokancinsu.
Povolal pak také Farao mudrců a čarodějníků; a učinili i ti čarodějníci Egyptští skrze čáry své tolikéž.
12 Kowannensu ya jefa sandansa ƙasa, ya kuwa zama maciji. Amma sandan Haruna ya haɗiye sandunansu.
Nebo povrhl každý z nich hůl svou, a obráceny jsou v hady; ale požřela hůl Aronova hole jejich.
13 Duk da haka zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa saurare su ba, kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
I posililo se srdce Faraonovo, a neuposlechl jich, tak jakž byl mluvil Hospodin.
14 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Zuciyar Fir’auna taurariya ce, ya ƙi yă bar mutanen su tafi.
Protož řekl Hospodin Mojžíšovi: Obtížilo se srdce Faraonovo; nechce propustiti lidu toho.
15 Ka je wurin Fir’auna da safe, yayinda za shi kogi. Ka jira a bakin Nilu don ka sadu da shi, ka ɗauki sandan nan da ya canja zuwa maciji a hannunka.
Jdi k Faraonovi ráno, aj, půjde ven k vodě, a stůj naproti němu při břehu řeky; a hůl, kteráž obrácena byla v hada, vezmeš do ruky své.
16 Sa’an nan ka ce masa, ‘Ubangiji, Allah na Ibraniyawa, ya aiko ni in faɗa maka, Ka bar mutanena su tafi domin su yi mini sujada a hamada. Amma har yanzu ba ka yi biyayya ba.
A díš mu: Hospodin Bůh Hebrejský poslal mne k tobě, aťbych řekl: Propusť lid můj, aby sloužili mi na poušti; a aj, neuposlechls až dosavad.
17 Ga abin da Ubangiji ya ce, da wannan za ka san cewa ni ne Ubangiji. Da sandan da yake hannuna zan bugi ruwan Nilu, zai kuma zama jini.
Protož takto praví Hospodin: Po tomto poznáš, že já jsem Hospodin: Aj, já udeřím holí, kteráž jest v ruce mé, na vody, kteréž jsou v řece, a obráceny budou v krev.
18 Kifi a ciki Nilu za su mutu, ruwan kuma zai yi ɗoyi; Masarawa ba za su iya shan ruwansa ba.’”
A ryby, kteréž jsou v řece, pomrou; i nasmradí se řeka, a ustávati budou Egyptští, hledajíce vody, kterouž by pili z řeky.
19 Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ce wa Haruna, ‘Ka ɗauki sandanka, ka miƙa hannunka kan ruwan Masar, kan kogunansu da rafuffukansu da kududdufansu da kuma dukan tafkunansu, za su zama jini.’ Jini zai kasance ko’ina a Masar, har ma a cikin abubuwan ajiyar ruwansu da aka yi da itace da kuma dutse.”
Protož řekl Hospodin Mojžíšovi: Rci Aronovi: Vezmi hůl svou, a vztáhni ruku svou na vody Egyptské, na řeky jejich, na potoky jejich, i na jezera jejich, a na všecka shromáždění vod jejich, aby se obrátily v krev; i bude krev po vší zemi Egyptské, tak v nádobách dřevěných, jako kamenných.
20 Musa da Haruna suka yi yadda Ubangiji ya umarta. Ya ɗaga sandansa a gaban Fir’auna da bayinsa, ya bugi ruwan Nilu, dukan ruwan kuwa ya zama jini.
Tedy učinili tak Mojžíš a Aron, jakž byl přikázal Hospodin; a zdvihna hůl, udeřil v vodu, kteráž byla v řece, před očima Faraonovýma a před očima služebníků jeho; i obráceny jsou všecky vody, kteréž byly v řece, v krev.
21 Kifin da suke cikin Nilu suka mutu, kogin kuwa ya yi wari sosai yadda Masarawa ba su iya shan ruwan ba. Jini ya bazu ko’ina a Masar.
Ryby pak, kteréž byly v řece, pomřely, a nasmradila se řeka, tak že nemohli Egyptští píti vody z řeky; a byla krev po vší zemi Egyptské.
22 Amma bokayen Masar ma suka yi abubuwan nan da sihirinsu, sai zuciyar Fir’auna ta taurare; bai saurari Musa da Haruna ba, kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
To též učinili i čarodějníci Egyptští skrze čáry své. I zsililo se srdce Faraonovo, aby neuposlechl jich, tak jakž byl mluvil Hospodin.
23 A maimakon yă saurara, sai ya juya ya koma fadarsa, bai ma damu da abin da aka yi ba.
A odvrátiv se Farao, přišel do domu svého; a ani k tomu nepřiložil srdce svého.
24 Sai dukan Masarawa suka yi ta tonon gefen Nilu don su sami ruwan sha, domin ba su iya shan ruwan kogin ba.
Kopali pak všickni Egyptští vůkol řeky, hledajíce vody ku pití; nebo nemohli píti vody z řeky.
25 Kwana bakwai suka wuce bayan da Ubangiji ya bugi kogin.
A vyplnilo se dní sedm, jakž ranil Hospodin řeku.