< Fitowa 6 >

1 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Yanzu za ka gan abin da zan yi da Fir’auna. Zan sa shi dole yă bar su su tafi, har ma yă iza ƙyeyarsu don su bar ƙasarsa!”
Le Seigneur dit à Moïse: C’est maintenant que tu verras ce que je vais faire à Pharaon; car par l’effet d’une main puissante il les laissera aller, et en vertu d’une main forte, il les pressera de sortir de son pays.
2 Allah ya kuma ce wa Musa, “Ni ne Ubangiji.
Le Seigneur parla encore à Moïse, disant: Je suis le Seigneur,
3 Na bayyana ga Ibrahim, ga Ishaku da kuma ga Yaƙub a matsayin Allah Maɗaukaki, amma sunan nan nawa Ubangiji, ban bayyana kaina a gare su ba.
Qui ai apparu à Abraham, à Isaac et à Jacob en Dieu tout-puissant; mais mon nom Adonaï, je ne le leur ai pas manifesté.
4 Na kuma kafa alkawari da su don in ba su ƙasar Kan’ana, inda suka yi zaman baƙunci.
Et j’ai fait alliance avec eux, afin de leur donner la terre de Chanaan, terre de leur pèlerinage dans laquelle ils ont été étrangers.
5 Ban da haka ma, na ji nishe-nishen Isra’ilawa, waɗanda Masarawa suka bautar, na kuma tuna da alkawarina.
J’ai entendu le gémissement des enfants d’Israël, que les Egyptiens ont opprimés; et je me suis souvenu de mon alliance.
6 “Saboda haka, ka ce wa Isra’ilawa, ‘Ni ne Ubangiji, zan kuma fitar da ku daga bauta ta Masarawa. Zan’yantar da ku daga zama bayinsu, da ƙarfina zan fanshe ku, in kawo hukunci mai zafi a kansu, don in cece ku.
C’est pourquoi dis aux enfants d’Israël: Je suis le Seigneur qui vous tirerai de la prison des Egyptiens, et vous délivrerai de la servitude: et je vous rachèterai par un bras élevé et de grands jugements.
7 Zan ɗauke ku tamƙar mutanena, in kuma zama Allahnku. Sa’an nan za ku sani Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga wahalar Masarawa.
Et je vous prendrai pour mon peuple, et je serai votre Dieu; ainsi vous saurez que c’est moi, qui suis le Seigneur votre Dieu, qui vous aurai tirés de la prison des Egyptiens,
8 Zan kuwa kawo ku a ƙasar da na rantse da hannun da na ɗaga sama, cewa zan ba wa Ibrahim, wa Ishaku, da kuma wa Yaƙub. Zan ba da ita gare ku gādo. Ni ne Ubangiji.’”
Et fait entrer dans la terre, sur laquelle j’ai levé la main, jurant que je la donnerais à Abraham, à Isaac et à Jacob; car je vous la donnerai en possession, moi le Seigneur.
9 Musa ya faɗa wa Isra’ilawa wannan magana, amma ba su kasa kunne a gare shi ba, don ɓacin rai saboda tsananin aikin bauta.
Moïse raconta donc toutes ces choses aux enfants d’Israël, qui ne l’écoutèrent pas à cause de l’angoisse de leur esprit et de leur travail très pénible.
10 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa,
Et le Seigneur parla à Moïse, disant:
11 “Koma ka ce wa Fir’auna sarkin Masar, yă bar Isra’ilawa su fita daga ƙasarsa.”
Entre, et parle à Pharaon, roi d’Egypte, pour qu’il laisse sortir les enfants d’Israël de son pays.
12 Amma Musa ya ce wa Ubangiji, “In Isra’ilawa ba su ji ni ba, yaya Fir’auna zai ji ni, da yake ina magana da ƙyar?”
Moïse répondit devant le Seigneur: Voilà que les enfants d’Israël ne m’écoutent pas: et comment Pharaon m’écoutera-t-il, surtout moi étant incirconcis des lèvres?
13 Ubangiji ya yi magana da Musa da Haruna game da Isra’ilawa da Fir’auna sarkin Masar, ya umarce su su fitar da Isra’ilawa daga Masar.
C’est ainsi que le Seigneur parla à Moïse et Aaron et qu’il leur donna ses ordres pour les enfants d’Israël et pour Pharaon, roi d’Egypte, afin qu’ils fissent sortir les enfants d’Israël de la terre d’Egypte.
14 Waɗannan su ne shugabannin iyalansu.’Ya’yan Ruben maza ɗan farin Isra’ila su ne, Hanok da Fallu, Hezron da Karmi. Waɗannan su ne dangin Ruben.
Voici les chefs des maisons selon leurs familles: Les fils de Ruben, premier-né d’Israël: Hénoch et Phallu, Hesron et Charmi:
15 ’Ya’yan Simeyon maza su ne, Yemuwel, Yamin, Ohad, Yakin, Zohar da Sha’ul ɗan mutuniyar Kan’ana. Waɗannan su ne dangin Simeyon.
C’est là la parenté de Ruben. Les fils de Siméon: Jamuel, Jamin, Ahod, Jachin, Soar et Saül, fils d’une Chananéenne. C’est là la race de Siméon.
16 Waɗannan su ne sunayen’ya’yan Lawi maza bisa ga abin da aka rubuta, Gershon, Kohat da Merari. Lawi ya yi shekara 137.
Et voici les noms des fils de Lévi, selon leur parenté: Gerson, Caath et Mérari. Or les années de la vie de Lévi furent cent trente-sept.
17 ’Ya’yan Gershon maza, bisa ga dangi su ne, Libni da Shimeyi.
Les fils de Gerson: Lobni et Séméi, selon leur parenté.
18 ’Ya’yan Kohat maza, su ne, Amram, Izhar, Hebron da Uzziyel. Kohat ya yi shekara 133.
Les fils de Caath: Amram-Isaar, Hébron et Oziel: et les années de la vie de Caath furent cent trente-trois.
19 ’Ya’yan Merari maza, su ne, Mali da Mushi. Waɗannan su ne dangin Lawi bisa ga abin da aka rubuta.
Les fils de Mérari: Moholi et Musi: c’est là la parenté de Lévi selon ses familles.
20 Amram ya auri’yar’uwar mahaifinsa Yokebed, wadda ta haifa masa Haruna da Musa. Amram ya yi shekara 137.
Or Amram prit pour femme Jochabed, fille de son oncle paternel, laquelle lui enfanta Aaron et Moïse. Et les années de la vie d’Amram furent cent trente-sept.
21 ’Ya’yan Izhar maza, su ne, Kora, Nefeg da Zikri.
Les fils d’Isaar: Coré, Nepheg et Zéchri.
22 ’Ya’yan Uzziyel maza, su ne, Mishayel, Elzafan da Sitri.
Les fils d’Oziel: Misaël, Elisaphan et Séthri
23 Haruna ya auri Elisheba,’yar Amminadab,’yar’uwar Nashon, sai ta haifa masa Nadab da Abihu, Eleyazar da Itamar.
Or Aaron prit pour femme Elisabeth, fille d’Aminadab, sœur de Nahasson, laquelle lui enfanta Nadab, Abiu, Eléazar et Ithamar.
24 ’Ya’yan Kora maza, su ne, Assir, Elkana da Abiyasaf. Waɗannan su ne dangin Kora.
Les fils de Coré: Aser, Elcana, et Abiasaph: c’est là la parenté des Corites.
25 Eleyazar ɗan Haruna, ya auri ɗaya daga cikin’yan matan Futiyel, sai ta haifa masa Finehas. Waɗannan su ne shugabannin iyalan Lawi, dangi, dangi.
Mais Eléazar, fils d’Aaron, prit une femme d’entre les filles le Phutiel, laquelle lui enfanta Phinéès. Ce sont là les chefs des familles lévitiques selon leur parenté.
26 Wannan Haruna da Musa ne, waɗanda Ubangiji ya yi musu magana ya ce, “Ku fitar da Isra’ilawa daga Masar ɓangare-ɓangare.”
C’est Aaron et Moïse auxquels le Seigneur commanda de retirer les enfants d’Israël de l’Egypte, selon leurs bandes.
27 Su ne suka yi magana da Fir’auna sarkin Masar game da fitar da Isra’ilawa daga Masar, wannan Musa da Haruna.
Ce sont eux qui parlent à Pharaon, roi d’Egypte, pour qu’ils retirent les enfants d’Israël de l’Egypte: c’est Moïse et Aaron,
28 Ana nan, sa’ad da Ubangiji ya yi magana da Musa a Masar,
Au jour où le Seigneur parla à Moïse dans la terre d’Egypte.
29 ya ce masa, “Ni ne Ubangiji. Sai ka faɗa wa Fir’auna sarkin Masar kome da na faɗa maka.”
Et le Seigneur parla à Moïse, disant: Je suis le Seigneur; dis à Pharaon, roi d’Egypte, tout ce que moi-même je te dis.
30 Amma Musa ya ce wa Ubangiji, “Ni mai nauyin baki ne, ina magana da ƙyar, ƙaƙa Fir’auna zai kasa kunne gare ni?”
Et Moïse répondit devant le Seigneur: Voici que je suis incirconcis des lèvres, comment Pharaon m’écoutera-t-il?

< Fitowa 6 >