< Fitowa 6 >

1 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Yanzu za ka gan abin da zan yi da Fir’auna. Zan sa shi dole yă bar su su tafi, har ma yă iza ƙyeyarsu don su bar ƙasarsa!”
Et l'Éternel dit à Moïse: Maintenant tu verras ce que je ferai à Pharaon; car il les laissera aller, contraint par une main forte; et, contraint par une main forte, il les chassera de son pays.
2 Allah ya kuma ce wa Musa, “Ni ne Ubangiji.
Et Dieu parla à Moïse, et lui dit: Je suis l'Éternel.
3 Na bayyana ga Ibrahim, ga Ishaku da kuma ga Yaƙub a matsayin Allah Maɗaukaki, amma sunan nan nawa Ubangiji, ban bayyana kaina a gare su ba.
Je suis apparu à Abraham, à Isaac, et à Jacob, comme le Dieu Tout-Puissant; mais sous mon nom, l'Éternel, je n'ai point été connu d'eux.
4 Na kuma kafa alkawari da su don in ba su ƙasar Kan’ana, inda suka yi zaman baƙunci.
Et j'ai aussi établi mon alliance avec eux, pour leur donner le pays de Canaan, le pays dans lequel ils ont séjourné comme étrangers.
5 Ban da haka ma, na ji nishe-nishen Isra’ilawa, waɗanda Masarawa suka bautar, na kuma tuna da alkawarina.
J'ai aussi entendu les gémissements des enfants d'Israël, que les Égyptiens tiennent esclaves; et je me suis souvenu de mon alliance.
6 “Saboda haka, ka ce wa Isra’ilawa, ‘Ni ne Ubangiji, zan kuma fitar da ku daga bauta ta Masarawa. Zan’yantar da ku daga zama bayinsu, da ƙarfina zan fanshe ku, in kawo hukunci mai zafi a kansu, don in cece ku.
C'est pourquoi, dis aux enfants d'Israël: Je suis l'Éternel, je vous retirerai de dessous les fardeaux d'Égypte; je vous délivrerai de leur servitude, et je vous rachèterai à bras étendu, et par de grands jugements.
7 Zan ɗauke ku tamƙar mutanena, in kuma zama Allahnku. Sa’an nan za ku sani Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga wahalar Masarawa.
Je vous prendrai pour mon peuple, et je vous serai Dieu, et vous connaîtrez que je suis l'Éternel votre Dieu, qui vous retire de dessous les fardeaux de l'Égypte.
8 Zan kuwa kawo ku a ƙasar da na rantse da hannun da na ɗaga sama, cewa zan ba wa Ibrahim, wa Ishaku, da kuma wa Yaƙub. Zan ba da ita gare ku gādo. Ni ne Ubangiji.’”
Et je vous ferai entrer au pays au sujet duquel j'ai levé ma main que je le donnerais à Abraham, à Isaac, et à Jacob; et je vous le donnerai en héritage: Je suis l'Éternel.
9 Musa ya faɗa wa Isra’ilawa wannan magana, amma ba su kasa kunne a gare shi ba, don ɓacin rai saboda tsananin aikin bauta.
Moïse parla donc ainsi aux enfants d'Israël; mais ils n'écoutèrent point Moïse, par impatience et à cause de leur dure servitude.
10 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa,
Et l'Éternel parla à Moïse, en disant:
11 “Koma ka ce wa Fir’auna sarkin Masar, yă bar Isra’ilawa su fita daga ƙasarsa.”
Va, parle à Pharaon, roi d'Égypte, et qu'il laisse sortir les enfants d'Israël de son pays.
12 Amma Musa ya ce wa Ubangiji, “In Isra’ilawa ba su ji ni ba, yaya Fir’auna zai ji ni, da yake ina magana da ƙyar?”
Alors Moïse parla devant l'Éternel, et dit: Voici, les enfants d'Israël ne m'ont pas écouté; et comment Pharaon m'écoutera-t-il, moi qui suis incirconcis de lèvres?
13 Ubangiji ya yi magana da Musa da Haruna game da Isra’ilawa da Fir’auna sarkin Masar, ya umarce su su fitar da Isra’ilawa daga Masar.
L'Éternel parla donc à Moïse et à Aaron, et leur ordonna d'aller trouver les enfants d'Israël, et Pharaon, roi d'Égypte, pour retirer les enfants d'Israël du pays d'Égypte.
14 Waɗannan su ne shugabannin iyalansu.’Ya’yan Ruben maza ɗan farin Isra’ila su ne, Hanok da Fallu, Hezron da Karmi. Waɗannan su ne dangin Ruben.
Voici les chefs des maisons de leurs pères. Les fils de Ruben, premier-né d'Israël: Hénoc et Pallu, Hetsron et Carmi. Voilà les familles de Ruben.
15 ’Ya’yan Simeyon maza su ne, Yemuwel, Yamin, Ohad, Yakin, Zohar da Sha’ul ɗan mutuniyar Kan’ana. Waɗannan su ne dangin Simeyon.
Les fils de Siméon: Jémuël, Jamin, Ohad, Jakin, Tsochar et Saül, fils de la Cananéenne. Voilà les familles de Siméon.
16 Waɗannan su ne sunayen’ya’yan Lawi maza bisa ga abin da aka rubuta, Gershon, Kohat da Merari. Lawi ya yi shekara 137.
Et voici les noms des fils de Lévi, selon leurs générations: Guershon, Kéhath et Mérari. Et les années de la vie de Lévi furent de cent trente-sept ans.
17 ’Ya’yan Gershon maza, bisa ga dangi su ne, Libni da Shimeyi.
Les fils de Guershon: Libni et Shimei, selon leurs familles.
18 ’Ya’yan Kohat maza, su ne, Amram, Izhar, Hebron da Uzziyel. Kohat ya yi shekara 133.
Les fils de Kéhath: Amram, Jitsehar, Hébron et Uziel. Et les années de la vie de Kéhath furent de cent trente-trois ans.
19 ’Ya’yan Merari maza, su ne, Mali da Mushi. Waɗannan su ne dangin Lawi bisa ga abin da aka rubuta.
Les fils de Mérari: Machli et Mushi. Voilà les familles de Lévi, selon leurs générations.
20 Amram ya auri’yar’uwar mahaifinsa Yokebed, wadda ta haifa masa Haruna da Musa. Amram ya yi shekara 137.
Or, Amram prit pour femme Jokébed, sa tante, et elle lui enfanta Aaron et Moïse. Et les années de la vie d'Amram furent de cent trente-sept ans.
21 ’Ya’yan Izhar maza, su ne, Kora, Nefeg da Zikri.
Les fils de Jitsehar: Coré, Népheg et Zicri.
22 ’Ya’yan Uzziyel maza, su ne, Mishayel, Elzafan da Sitri.
Les fils d'Uziel: Mishaël, Eltsaphan et Sithri.
23 Haruna ya auri Elisheba,’yar Amminadab,’yar’uwar Nashon, sai ta haifa masa Nadab da Abihu, Eleyazar da Itamar.
Et Aaron épousa Elishéba, fille d'Amminadab, sœur de Nahashon, et elle lui enfanta Nadab, Abihu, Éléazar et Ithamar.
24 ’Ya’yan Kora maza, su ne, Assir, Elkana da Abiyasaf. Waɗannan su ne dangin Kora.
Les fils de Coré: Assir, Elkana et Abiasaph. Voilà les familles des Corites.
25 Eleyazar ɗan Haruna, ya auri ɗaya daga cikin’yan matan Futiyel, sai ta haifa masa Finehas. Waɗannan su ne shugabannin iyalan Lawi, dangi, dangi.
Or, Éléazar, fils d'Aaron, prit pour sa femme une des filles de Puthiel, et elle lui enfanta Phinées. Tels sont les chefs des maisons des pères des Lévites, selon leurs familles.
26 Wannan Haruna da Musa ne, waɗanda Ubangiji ya yi musu magana ya ce, “Ku fitar da Isra’ilawa daga Masar ɓangare-ɓangare.”
C'est cet Aaron et ce Moïse, à qui l'Éternel dit: Retirez les enfants d'Israël du pays d'Égypte, selon leurs armées.
27 Su ne suka yi magana da Fir’auna sarkin Masar game da fitar da Isra’ilawa daga Masar, wannan Musa da Haruna.
Ce sont eux qui parlèrent à Pharaon, roi d'Égypte, pour retirer d'Égypte les enfants d'Israël. C'est ce Moïse et cet Aaron.
28 Ana nan, sa’ad da Ubangiji ya yi magana da Musa a Masar,
Il arriva donc qu'au jour où l'Éternel parla à Moïse, dans le pays d'Égypte,
29 ya ce masa, “Ni ne Ubangiji. Sai ka faɗa wa Fir’auna sarkin Masar kome da na faɗa maka.”
L'Éternel parla à Moïse, en disant: Je suis l'Éternel; dis à Pharaon, roi d'Égypte, tout ce que je te dirai.
30 Amma Musa ya ce wa Ubangiji, “Ni mai nauyin baki ne, ina magana da ƙyar, ƙaƙa Fir’auna zai kasa kunne gare ni?”
Alors Moïse dit devant l'Éternel: Voici, je suis incirconcis de lèvres; comment Pharaon m'écouterait-il?

< Fitowa 6 >