< Fitowa 6 >
1 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Yanzu za ka gan abin da zan yi da Fir’auna. Zan sa shi dole yă bar su su tafi, har ma yă iza ƙyeyarsu don su bar ƙasarsa!”
Adonai said to Moses [Drawn out], “Now you shall see what I will do to Pharaoh, for by a strong hand he shall let them go, and by a strong hand he shall divorce them out of his land.”
2 Allah ya kuma ce wa Musa, “Ni ne Ubangiji.
God spoke to Moses [Drawn out], and said to him, “I am Adonai;
3 Na bayyana ga Ibrahim, ga Ishaku da kuma ga Yaƙub a matsayin Allah Maɗaukaki, amma sunan nan nawa Ubangiji, ban bayyana kaina a gare su ba.
and I appeared to Abraham [Father of a multitude], to Isaac [Laughter], and to Jacob [Supplanter], as El Shaddai [God Almighty]; but by my name Adonai I was not known to them.
4 Na kuma kafa alkawari da su don in ba su ƙasar Kan’ana, inda suka yi zaman baƙunci.
I have also established my covenant ·binding contract between two or more parties· with them, to give them the land of Canaan [Humbled], the land of their travels, in which they lived as aliens.
5 Ban da haka ma, na ji nishe-nishen Isra’ilawa, waɗanda Masarawa suka bautar, na kuma tuna da alkawarina.
Moreover I have sh'ma ·heard obeyed· the groaning of the children of Israel [God prevails], whom the Egyptians [people from Abode of slavery] keep in bondage, and I have remembered my covenant.
6 “Saboda haka, ka ce wa Isra’ilawa, ‘Ni ne Ubangiji, zan kuma fitar da ku daga bauta ta Masarawa. Zan’yantar da ku daga zama bayinsu, da ƙarfina zan fanshe ku, in kawo hukunci mai zafi a kansu, don in cece ku.
Therefore tell the children of Israel [God prevails], ‘I am Adonai, and I will bring you out from under the burdens of the Egyptians [people from Abode of slavery], and I will rid you out of their bondage, and I will redeem you with an outstretched arm, and with great judgments:
7 Zan ɗauke ku tamƙar mutanena, in kuma zama Allahnku. Sa’an nan za ku sani Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga wahalar Masarawa.
and I will take you to be my people, and I will be your God; and you shall know that I am Adonai your God, who brings you out from under the burdens of the Egyptians [people from Abode of slavery].
8 Zan kuwa kawo ku a ƙasar da na rantse da hannun da na ɗaga sama, cewa zan ba wa Ibrahim, wa Ishaku, da kuma wa Yaƙub. Zan ba da ita gare ku gādo. Ni ne Ubangiji.’”
I will bring you into the land which I swore to give to Abraham [Father of a multitude], to Isaac [Laughter], and to Jacob [Supplanter]; and I will give it to you for a heritage: I am Adonai.’”
9 Musa ya faɗa wa Isra’ilawa wannan magana, amma ba su kasa kunne a gare shi ba, don ɓacin rai saboda tsananin aikin bauta.
Moses [Drawn out] spoke so to the children of Israel [God prevails], but they didn’t sh'ma ·hear obey· unto Moses [Drawn out] for anguish of spirit, and for cruel bondage.
10 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa,
Adonai spoke to Moses [Drawn out], saying,
11 “Koma ka ce wa Fir’auna sarkin Masar, yă bar Isra’ilawa su fita daga ƙasarsa.”
“Go in, speak to Pharaoh king of Egypt [Abode of slavery], that he let the children of Israel [God prevails] go out of his land.”
12 Amma Musa ya ce wa Ubangiji, “In Isra’ilawa ba su ji ni ba, yaya Fir’auna zai ji ni, da yake ina magana da ƙyar?”
Moses [Drawn out] spoke before Adonai, saying, “Behold, the children of Israel [God prevails] haven’t sh'ma ·heard obeyed· unto me. How then shall Pharaoh listen to me, who am of uncircumcised lips?”
13 Ubangiji ya yi magana da Musa da Haruna game da Isra’ilawa da Fir’auna sarkin Masar, ya umarce su su fitar da Isra’ilawa daga Masar.
Adonai spoke to Moses [Drawn out] and to Aaron [Light-bringer], and gave them an enjoinment to the children of Israel [God prevails], and to Pharaoh king of Egypt [Abode of slavery], to bring the children of Israel [God prevails] out of the land of Egypt [Abode of slavery].
14 Waɗannan su ne shugabannin iyalansu.’Ya’yan Ruben maza ɗan farin Isra’ila su ne, Hanok da Fallu, Hezron da Karmi. Waɗannan su ne dangin Ruben.
These are the heads of their fathers’ houses. The sons of Reuben [See, a son!] the firstborn of Israel [God prevails]: Hanoch, and Pallu, Hezron, and Carmi; these are the families of Reuben [See, a son!].
15 ’Ya’yan Simeyon maza su ne, Yemuwel, Yamin, Ohad, Yakin, Zohar da Sha’ul ɗan mutuniyar Kan’ana. Waɗannan su ne dangin Simeyon.
The sons of Simeon [Hearing]: Jemuel, and Jamin, and Ohad, and Jachin, and Zohar, and Shaul [Asked for] the son of a Canaanite [Descendant of Humbled] woman; these are the families of Simeon [Hearing].
16 Waɗannan su ne sunayen’ya’yan Lawi maza bisa ga abin da aka rubuta, Gershon, Kohat da Merari. Lawi ya yi shekara 137.
These are the names of the sons of Levi [United with] according to their generations: Gershon, and Kohath, and Merari; and the years of the life of Levi [United with] were one hundred thirty-seven years.
17 ’Ya’yan Gershon maza, bisa ga dangi su ne, Libni da Shimeyi.
The sons of Gershon: Libni and Shimei, according to their families.
18 ’Ya’yan Kohat maza, su ne, Amram, Izhar, Hebron da Uzziyel. Kohat ya yi shekara 133.
The sons of Kohath: Amram, and Izhar, and Hebron, and Uzziel; and the years of the life of Kohath were one hundred thirty-three years.
19 ’Ya’yan Merari maza, su ne, Mali da Mushi. Waɗannan su ne dangin Lawi bisa ga abin da aka rubuta.
The sons of Merari: Mahli and Mushi. These are the families of the Levites [Descendants of United with] according to their generations.
20 Amram ya auri’yar’uwar mahaifinsa Yokebed, wadda ta haifa masa Haruna da Musa. Amram ya yi shekara 137.
Amram took Jochebed his father’s sister to himself as wife; and she bore him Aaron [Light-bringer] and Moses [Drawn out]: and the years of the life of Amram were one hundred and thirty-seven years.
21 ’Ya’yan Izhar maza, su ne, Kora, Nefeg da Zikri.
The sons of Izhar: Korach [Bald one, Frost], and Nepheg, and Zichri.
22 ’Ya’yan Uzziyel maza, su ne, Mishayel, Elzafan da Sitri.
The sons of Uzziel: Mishael, and Elzaphan, and Sithri.
23 Haruna ya auri Elisheba,’yar Amminadab,’yar’uwar Nashon, sai ta haifa masa Nadab da Abihu, Eleyazar da Itamar.
Aaron [Light-bringer] took Elisheba, the daughter of Amminadab, the sister of Nahshon, as his wife; and she bore him Nadab and Abihu, Eleazar [Help of God] and Ithamar.
24 ’Ya’yan Kora maza, su ne, Assir, Elkana da Abiyasaf. Waɗannan su ne dangin Kora.
The sons of Korach [Bald one, Frost]: Assir, and Elkanah, and Abiasaph; these are the families of the Korahites.
25 Eleyazar ɗan Haruna, ya auri ɗaya daga cikin’yan matan Futiyel, sai ta haifa masa Finehas. Waɗannan su ne shugabannin iyalan Lawi, dangi, dangi.
Eleazar [Help of God] Aaron [Light-bringer]’s son took one of the daughters of Putiel as his wife; and she bore him Pinchas [Bronze skin]. These are the heads of the fathers’ houses of the Levites [Descendants of United with] according to their families.
26 Wannan Haruna da Musa ne, waɗanda Ubangiji ya yi musu magana ya ce, “Ku fitar da Isra’ilawa daga Masar ɓangare-ɓangare.”
These are that Aaron [Light-bringer] and Moses [Drawn out], to whom Adonai said, “Bring out the children of Israel [God prevails] from the land of Egypt [Abode of slavery] according to their armies.”
27 Su ne suka yi magana da Fir’auna sarkin Masar game da fitar da Isra’ilawa daga Masar, wannan Musa da Haruna.
These are those who spoke to Pharaoh king of Egypt [Abode of slavery], to bring out the children of Israel [God prevails] from Egypt [Abode of slavery]. These are that Moses [Drawn out] and Aaron [Light-bringer].
28 Ana nan, sa’ad da Ubangiji ya yi magana da Musa a Masar,
On the day when Adonai spoke to Moses [Drawn out] in the land of Egypt [Abode of slavery],
29 ya ce masa, “Ni ne Ubangiji. Sai ka faɗa wa Fir’auna sarkin Masar kome da na faɗa maka.”
Adonai spoke to Moses [Drawn out], saying, “I am Adonai. Speak to Pharaoh king of Egypt [Abode of slavery] all that I speak to you.”
30 Amma Musa ya ce wa Ubangiji, “Ni mai nauyin baki ne, ina magana da ƙyar, ƙaƙa Fir’auna zai kasa kunne gare ni?”
Moses [Drawn out] said before Adonai, “Behold, I am of uncircumcised lips, and how shall Pharaoh sh'ma ·hear obey· unto me?”