< Fitowa 6 >
1 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Yanzu za ka gan abin da zan yi da Fir’auna. Zan sa shi dole yă bar su su tafi, har ma yă iza ƙyeyarsu don su bar ƙasarsa!”
Jahve reče Mojsiju: “Naskoro ćeš vidjeti kako ću ja s faraonom! Pod jakom rukom pustit će ih da odu; pod jakom rukom sam će ih iz svoje zemlje istjerati.”
2 Allah ya kuma ce wa Musa, “Ni ne Ubangiji.
Još reče Bog Mojsiju: “Ja sam Jahve.
3 Na bayyana ga Ibrahim, ga Ishaku da kuma ga Yaƙub a matsayin Allah Maɗaukaki, amma sunan nan nawa Ubangiji, ban bayyana kaina a gare su ba.
Abrahamu, Izaku i Jakovu objavljivao sam se kao El Šadaj. Ali njima se nisam očitovao pod svojim imenom - Jahve.
4 Na kuma kafa alkawari da su don in ba su ƙasar Kan’ana, inda suka yi zaman baƙunci.
I sklopio sam svoj Savez s njima da ću im dati kanaansku zemlju, zemlju gdje su živjeli kao pridošlice.
5 Ban da haka ma, na ji nishe-nishen Isra’ilawa, waɗanda Masarawa suka bautar, na kuma tuna da alkawarina.
A sada, pošto sam čuo uzdisaje Izraelaca koje Egipćani drže u ropstvu, sjetih se svoga Saveza.
6 “Saboda haka, ka ce wa Isra’ilawa, ‘Ni ne Ubangiji, zan kuma fitar da ku daga bauta ta Masarawa. Zan’yantar da ku daga zama bayinsu, da ƙarfina zan fanshe ku, in kawo hukunci mai zafi a kansu, don in cece ku.
Kaži, dakle, Izraelcima da sam ja Jahve; da ću vas izbaviti od tereta što su vam ga Egipćani nametnuli. Oslobodit ću vas od ropstva u kojem vas drže; izbavit ću vas udarajući jako i kažnjavajući strogo.
7 Zan ɗauke ku tamƙar mutanena, in kuma zama Allahnku. Sa’an nan za ku sani Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga wahalar Masarawa.
Za svoj ću vas narod uzeti i bit ću vašim Bogom. Tada ćete znati da sam vas ja, Jahve, vaš Bog, izbavio od egipatske tlake.
8 Zan kuwa kawo ku a ƙasar da na rantse da hannun da na ɗaga sama, cewa zan ba wa Ibrahim, wa Ishaku, da kuma wa Yaƙub. Zan ba da ita gare ku gādo. Ni ne Ubangiji.’”
Dovest ću vas u zemlju za koju sam se zakleo da ću je dati Abrahamu, Izaku i Jakovu i dat ću vam je u baštinu, ja, Jahve.”
9 Musa ya faɗa wa Isra’ilawa wannan magana, amma ba su kasa kunne a gare shi ba, don ɓacin rai saboda tsananin aikin bauta.
Mojsije to kazivaše Izraelcima, ali ga ne htjedoše slušati: duhovi su im bili pomućeni od teškoga ropstva.
10 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa,
Onda Jahve reče Mojsiju:
11 “Koma ka ce wa Fir’auna sarkin Masar, yă bar Isra’ilawa su fita daga ƙasarsa.”
“Idi i reci faraonu, kralju egipatskome, da otpusti Izraelce iz svoje zemlje.”
12 Amma Musa ya ce wa Ubangiji, “In Isra’ilawa ba su ji ni ba, yaya Fir’auna zai ji ni, da yake ina magana da ƙyar?”
Mojsije prozbori Jahvi: “Kad me Izraelci nisu slušali, kako će me, spora u govoru, saslušati faraon!”
13 Ubangiji ya yi magana da Musa da Haruna game da Isra’ilawa da Fir’auna sarkin Masar, ya umarce su su fitar da Isra’ilawa daga Masar.
Ali je Jahve govorio Mojsiju i Aronu i slao ih sad k Izraelcima, a sad k faraonu, kralju egipatskome, da pusti Izraelce iz Egipta.
14 Waɗannan su ne shugabannin iyalansu.’Ya’yan Ruben maza ɗan farin Isra’ila su ne, Hanok da Fallu, Hezron da Karmi. Waɗannan su ne dangin Ruben.
Ovo su glave njihovih domova. Sinovi Izraelova prvorođenca Rubena: Henok, Palu, Hesron i Karmi. To su obitelji potekle od Rubena.
15 ’Ya’yan Simeyon maza su ne, Yemuwel, Yamin, Ohad, Yakin, Zohar da Sha’ul ɗan mutuniyar Kan’ana. Waɗannan su ne dangin Simeyon.
A sinovi Šimunovi: Jemuel, Jamin, Ohad, Jakin, Sohar i Šaul, sin Kanaanke. To su obitelji potekle od Šimuna.
16 Waɗannan su ne sunayen’ya’yan Lawi maza bisa ga abin da aka rubuta, Gershon, Kohat da Merari. Lawi ya yi shekara 137.
Ovo su imena Levijevih sinova s njihovim potomstvom: Geršon, Kehat i Merari. Levi je živio sto trideset i sedam godina.
17 ’Ya’yan Gershon maza, bisa ga dangi su ne, Libni da Shimeyi.
Sinovi su Geršonovi: Libni i Šimi sa svojim obiteljima.
18 ’Ya’yan Kohat maza, su ne, Amram, Izhar, Hebron da Uzziyel. Kohat ya yi shekara 133.
Sinovi su Kehatovi: Amram, Jishar, Hebron i Uziel. Kehat je živio sto trideset i tri godine.
19 ’Ya’yan Merari maza, su ne, Mali da Mushi. Waɗannan su ne dangin Lawi bisa ga abin da aka rubuta.
Merarijevi su sinovi: Mahli i Muši. To su Levijeve obitelji s njihovim potomcima.
20 Amram ya auri’yar’uwar mahaifinsa Yokebed, wadda ta haifa masa Haruna da Musa. Amram ya yi shekara 137.
Amram se oženi svojom tetkom Jokebedom, koja mu rodi Arona i Mojsija. Amram je živio sto trideset i sedam godina.
21 ’Ya’yan Izhar maza, su ne, Kora, Nefeg da Zikri.
Sinovi Jisharovi bijahu: Korah, Nefeg i Zikri.
22 ’Ya’yan Uzziyel maza, su ne, Mishayel, Elzafan da Sitri.
A sinovi su Uzielovi: Mišael, Elsafan i Sitri.
23 Haruna ya auri Elisheba,’yar Amminadab,’yar’uwar Nashon, sai ta haifa masa Nadab da Abihu, Eleyazar da Itamar.
Aron se oženi Elišebom, kćerkom Aminadabovom, a sestrom Nahšonovom, koja mu rodi: Nadaba, Abihua, Eleazara i Itamara.
24 ’Ya’yan Kora maza, su ne, Assir, Elkana da Abiyasaf. Waɗannan su ne dangin Kora.
Korahovi su sinovi: Asir, Elkana i Abiasaf. To su Korahovi potomci.
25 Eleyazar ɗan Haruna, ya auri ɗaya daga cikin’yan matan Futiyel, sai ta haifa masa Finehas. Waɗannan su ne shugabannin iyalan Lawi, dangi, dangi.
Aronov sin Eleazar oženi se jednom Putielovom kćeri, koja mu rodi Pinhasa. To su glave Levijevih domova prema njihovim koljenima.
26 Wannan Haruna da Musa ne, waɗanda Ubangiji ya yi musu magana ya ce, “Ku fitar da Isra’ilawa daga Masar ɓangare-ɓangare.”
To je onaj Aron i Mojsije kojima je Jahve zapovjedio da izvedu Izraelce iz Egipta po njihovim četama.
27 Su ne suka yi magana da Fir’auna sarkin Masar game da fitar da Isra’ilawa daga Masar, wannan Musa da Haruna.
To su oni isti, Mojsije i Aron, koji su govorili faraonu, kralju egipatskome, da pusti Izraelce iz Egipta.
28 Ana nan, sa’ad da Ubangiji ya yi magana da Musa a Masar,
U dan kad je Jahve govorio s Mojsijem u egipatskoj zemlji,
29 ya ce masa, “Ni ne Ubangiji. Sai ka faɗa wa Fir’auna sarkin Masar kome da na faɗa maka.”
rekao mu je: “Ja sam Jahve. Izvijesti faraona, egipatskoga kralja, o svemu što ti kažem.”
30 Amma Musa ya ce wa Ubangiji, “Ni mai nauyin baki ne, ina magana da ƙyar, ƙaƙa Fir’auna zai kasa kunne gare ni?”
Mojsije se pred Jahvom ispričavao: “Spor sam ja u govoru. Kako će me faraon poslušati?”