< Fitowa 5 >

1 Daga bisani sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir’auna suka ce, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Bari mutanena su tafi domin su yi mini biki a hamada.’”
Derefter gikk Moses og Aron inn til Farao og sa: Så sier Herren, Israels Gud: La mitt folk fare, så de kan holde høitid for mig i ørkenen!
2 Fir’auna ya ce, “Wane ne Ubangiji da zan yi biyayya da shi, har in bar Isra’ila su tafi? Ban san Ubangiji ba, kuma ba zan bar Isra’ila su tafi ba.”
Men Farao sa: Hvem er Herren som jeg skal lyde og la Israel fare? Jeg kjenner ikke Herren, og heller ikke vil jeg la Israel fare.
3 Sai suka ce, “Allah na Ibraniyawa ya sadu da mu. Yanzu bari mu ɗauki tafiyar kwana uku cikin hamada domin mu miƙa hadaya ga Ubangiji Allahnmu, don kada yă buga mu da annoba ko takobi.”
Da sa de: Hebreernes Gud har møtt oss; la oss dra tre dagsreiser ut i ørkenen og ofre til Herren vår Gud, så han ikke skal slå oss med pest eller sverd!
4 Amma sarkin Masar ya ce wa, “Musa da Haruna, don me kuke hana mutane yin aikinsu? Ku koma wurin aikinku!”
Men kongen i Egypten sa til dem: Hvorfor vil I, Moses og Aron, dra folket fra dets arbeid? Gå og gjør det I skal!
5 Sa’an nan Fir’auna ya ce, “Ga shi mutane sun yi yawa a ƙasar Masar, ku kuma yanzu kuna so ku hana su yin aiki.”
Så sa Farao: Se, folket er nu blitt altfor tallrikt i landet, og så vil I dra dem bort fra det de har å gjøre!
6 A wannan rana Fir’auna ya ba da wannan umarni wa shugabannin masu gandu,
Og samme dag bød Farao arbeidsfogdene og opsynsmennene over folket og sa:
7 “Kada ku ƙara ba wa mutanen ciyawar tattaka domin su yi tubula, bari su tafi su tattara tattaka da kansu.
I skal ikke mere gi folket halm til teglarbeidet, som før; de skal selv gå og sanke sig halm.
8 Ku kuma bukace su su yi tubula daidai yawan tubalin da suka saba yi, kada ku rage. Ragwaye ne, shi ya sa suke kuka cewa, ‘Bari mu tafi mu yi hadaya ga Allahnmu.’
Men den samme mengde teglsten som de før har gjort, skal I pålegge dem; I skal ikke avkorte noget i deres arbeid. For de er dovne; derfor skriker de og sier: La oss gå og ofre til vår Gud!
9 Ku sa waɗannan mutane su yi aiki mai tsanani sosai, don kada su sami zarafin kasa kunne ga maganganun ƙarya.”
Legg tungt arbeid på disse mennesker, så de har nok med det og ikke hører efter løgnaktige ord!
10 Sai shugabannin masu aikin gandu suka fita suka gaya wa mutanen Isra’ila, “Ga abin da Fir’auna ya ce, ‘Ba zan ƙara ba ku tattaka ba.
Da gikk arbeidsfogdene og opsynsmennene ut og sa til folket: Så sier Farao: Jeg gir eder ikke lenger halm.
11 Ku tafi ku nemo wa kanku tattaka duk inda za ku samu, amma ba za a rage aikinku ba ko kaɗan.’”
Gå selv og finn eder halm, hvor I kan; Men i eders arbeid skal det ikke avkortes noget.
12 Saboda haka mutane suka warwatsu ko’ina a Masar domin tattara bunnun da za su yi amfani da su, maimakon tattaka.
Da spredte folket sig over hele Egyptens land for å sanke stubber til å bruke istedenfor halm.
13 Shugabannin gandu suka dinga matsa musu suna cewa, “Ku cika aikin da aka bukace ku na kowace rana kamar yadda kuke yi sa’ad da kuke da tattaka.”
Men arbeidsfogdene drev på og sa: Gjør eders arbeid ferdig, fullt dagsverk for hver dag, likesom dengang I hadde halm.
14 Manyan Isra’ilawa waɗanda shugabannin gandun Fir’auna suka naɗa, suka sha dūka, aka kuma yi musu tambayoyi ana cewa, “Don me ba ku cika yawan tubula na jiya da na yau kamar yadda kuka saba ba?”
Og opsynsmennene som Faraos arbeidsfogder hadde satt over Israels barn, fikk hugg, og arbeidsfogdene sa til dem: Hvorfor har I ikke gjort ferdig den fastsatte mengde teglsten, likesom før, hverken igår eller idag?
15 Sai manyan Isra’ila masu bi da aikin gandu suka tafi wurin Fir’auna suka yi roƙo suna cewa, “Don me kake yi wa bayinka haka?
Da gikk opsynsmennene over Israels barn til Farao og klaget høilydt for ham og sa: Hvorfor gjør du således med dine tjenere?
16 Ba a ba wa bayinka tattaka, duk da haka ana ce mana, ‘Ku yi tubula!’ Ana wa bayinka dūka, amma fa laifin na mutanenka ne.”
Dine tjenere får ikke halm, og allikevel sier de til oss: Gjør tegl! Og så får dine tjenere hugg, enda det er ditt eget folk som har skylden.
17 Fir’auna ya ce, “Ku ragwaye ne! Shi ya sa kuke cewa, ‘Bari mu tafi mu yi hadaya wa Ubangiji.’
Men han sa: Dovne er I, dovne! Derfor sier I: Vi vil gå og ofre til Herren.
18 Ku ɓace yanzu daga nan, ku koma wurin aikinku. Ba za a ba ku tattaka ba, kuma dole ku fid da tubula kamar yadda kuka saba.”
Så gå nu og arbeid! Halm får I ikke, men den fastsatte mengde tegl skal I komme med.
19 Manyan Isra’ilawa da suke bi da aikin gandu suka gane cewa sun shiga uku, sa’ad da aka gaya musu, “Ba za ku rage yawan tubulan da aka bukace ku ku yi na kowace rana ba.”
Israels barns opsynsmenn så at de var ille farne, da det blev sagt til dem: I skal ikke avkorte noget i den teglsten I skal ha ferdig - fullt dagsverk for hver dag!
20 Da suka bar Fir’auna, sai suka sadu da Musa da Haruna suna jira su sadu da su,
Og da de kom ut fra Farao, møtte de Moses og Aron, som stod og ventet på dem.
21 sai suka ce, “Bari Ubangiji yă duba, yă kuma hukunta ku! Kun maishe mu abin ƙyama ga Fir’auna da bayinsa, kuka kuma sa musu takobi a hannunsu don su kashe mu.”
Og de sa til dem: Herren hjemsøke eder og dømme eder fordi I har ført oss i vanrykte hos Farao og hans tjenere, så I har gitt dem sverd i hånden til å slå oss ihjel.
22 Musa ya koma wurin Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji, don me ka kawo wahala a kan mutanen nan? Abin da ya sa ka aiko ni ke nan?
Da vendte Moses sig igjen til Herren og sa: Herre, hvorfor har du gjort så ille med dette folk? Hvorfor har du sendt mig?
23 Gama tun da na tafi wurin Fir’auna, na yi masa magana da sunanka, sai ya fara gasa wa mutanen nan azaba, ba ka kuma ceci mutanenka.”
For fra den stund jeg gikk inn til Farao for å tale i ditt navn, har han gjort ille mot dette folk, og du har aldeles ikke hjulpet ditt folk.

< Fitowa 5 >