< Fitowa 40 >

1 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa,
Locutusque est Dominus ad Moysen, dicens:
2 “Ka kafa tabanakul, da Tentin Sujada, a kan rana ta fari ga watan fari.
Mense primo, prima die mensis, eriges tabernaculum testimonii,
3 Ka sa akwatin Alkawari a cikinsa, sa’an nan ka rufe shi da labule.
et pones in eo arcam, dimittesque ante illam velum:
4 Ka shigar da teburin ka shirya kayayyakin a kansa. Sa’an nan ka shigar da wurin ajiye fitilan ka kuma sa fitilunsa.
et illata mensa, pones super eam quæ rite præcepta sunt. Candelabrum stabit cum lucernis suis,
5 Ka sa bagaden zinariya na ƙona turare a gaban akwatin Alkawari, ka kuma sa labule a ƙofar shiga tabanakul.
et altare aureum in quo adoletur incensum, coram arca testimonii. Tentorium in introitu tabernaculi pones,
6 “Ka ajiye bagade na yin hadaya ta ƙonawa a gaban ƙofar tabanakul, da Tentin Sujada;
et ante illud altare holocausti:
7 ka ajiye daron tsakanin Tentin Sujada da bagaden, ka kuma zuba ruwa a cikinsa.
labrum inter altare et tabernaculum, quod implebis aqua.
8 Ka yi fili kewaye da shi, ka kuma sa labule a ƙofar shiga filin.
Circumdabisque atrium tentoriis, et ingressum eius.
9 “Ka ɗauki man shafewa ka shafe tabanakul da duka abin da yake cikinsa; ka keɓe shi da dukan kayayyakinsa, zai zama tsarkake.
Et assumpto unctionis oleo unges tabernaculum cum vasis suis, ut sanctificentur:
10 Sa’an nan ka shafe bagaden hadaya ta ƙonawa da kayansa; ka keɓe bagaden, zai zama mai tsarki.
altare holocausti et omnia vasa eius:
11 Ka shafe daron da wurin ajiyarsa, ka kuma keɓe su.
labrum cum basi sua: omnia unctionis oleo consecrabis, ut sint Sancta sanctorum.
12 “Ka kawo Haruna da’ya’yansa a ƙofar Tentin Sujada ka wanke su da ruwa.
Applicabisque Aaron et filios eius ad fores tabernaculi testimonii, et lotos aqua
13 Sa’an nan ka sa wa Haruna tsarkakun riguna, ka shafe shi, ka kuma keɓe shi don yă yi mini hidima a matsayin firist.
14 Ka kawo’ya’yansa maza ka sa musu taguwoyi.
15 Ka shafe su yadda ka shafe mahaifinsu, don su yi mini hidima a matsayin firistoci. Shafe musu man, zai sa su zama firistoci na ɗinɗinɗin, dukan zamanansu.”
indues sanctis vestibus, ut ministrent mihi, et unctio eorum in sacerdotium sempiternum proficiat.
16 Musa ya aikata dukan kome yadda Ubangiji ya umarce shi.
Fecitque Moyses omnia quæ præceperat Dominus.
17 Da haka aka kafa tabanakul, a rana ta fari ga wata na fari a shekara ta biyu.
Igitur mense primo anni secundi, prima die mensis, collocatum est tabernaculum.
18 Sa’ad da Musa ya kafa tabanakul, ya sa rammuka a wurinsu, ya sa katakan, ya kuma sa sandunan, ya kakkafa dogayen sandunan.
Erexitque Moyses illud, et posuit tabulas ac bases et vectes, statuitque columnas,
19 Sa’an nan ya shimfiɗa tentin a bisa tabanakul, ya kuma sa murfi a bisa tentin, yadda Ubangiji ya umarce shi.
et expandit tectum super tabernaculum, imposito desuper operimento, sicut Dominus imperaverat.
20 Ya ɗauki dokokin Alkawari ya sa a cikin akwatin, ya kuma zura sandunan a zoban akwatin, sa’an nan ya sa murfin kafara a bisansa.
Posuit et testimonium in arca, subditis infra vectibus, et oraculum desuper.
21 Sai ya kawo akwatin a cikin tabanakul, ya kuma rataye labulen rufewa ya tsare akwatin Alkawarin, yadda Ubangiji ya umarce shi.
Cumque intulisset arcam in tabernaculum, appendit ante eam velum ut expleret Domini iussionem.
22 Musa ya sa teburin a Tentin Sujada, a gefen arewa na tabanakul waje da labulen.
Posuit et mensam in tabernaculo testimonii ad plagam Septentrionalem extra velum,
23 Ya shirya burodin a kai a gaban Ubangiji, yadda Ubangiji ya umarce shi.
ordinatis coram propositionis panibus, sicut præceperat Dominus Moysi.
24 Ya sa wurin ajiye fitilan a Tentin Sujada ɗaura da teburin a gefen kudu na tabanakul
Posuit et candelabrum in tabernaculo testimonii e regione mensæ in parte australi,
25 ya kuma shirya fitilun a gaban Ubangiji, yadda Ubangiji ya umarce shi.
locatis per ordinem lucernis, iuxta præceptum Domini.
26 Musa ya sa bagaden zinariya a cikin Tentin Sujada a gaban labulen
Posuit et altare aureum sub tecto testimonii contra velum,
27 ya ƙone turare mai ƙanshi a kai, yadda Ubangiji ya umarce shi.
et adolevit super eo incensum aromatum, sicut iusserat Dominus Moysi.
28 Sa’an nan ya sa labule a ƙofar shiga na tabanakul.
Posuit et tentorium in introitu tabernaculi testimonii,
29 Ya sa bagaden hadaya ta ƙonawa kusa da ƙofar tabanakul, Tentin Sujada, sa’an nan ya miƙa hadaya ta ƙonawa da hadaya ta gari a kansa, yadda Ubangiji ya umarce shi.
et altare holocausti in vestibulo testimonii, offerens in eo holocaustum, et sacrificia, ut Dominus imperaverat.
30 Ya sa daro tsakanin Tentin Sujada da bagade, ya kuma zuba ruwa a cikinsa don wanki,
Labrum quoque statuit inter tabernaculum testimonii et altare, implens illud aqua.
31 a cikin kuwa Musa da Haruna da’ya’yansa maza sukan wanke hannunsa da ƙafafunsu.
Laveruntque Moyses et Aaron, ac filii eius manus suas et pedes,
32 Sukan yi wanka a duk sa’ad da suka shiga Tentin Sujada, ko in suka kusaci bagade, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
cum ingrederentur tectum fœderis, et accederent ad altare, sicut præceperat Dominus Moysi.
33 Sa’an nan Musa ya yi fili kewaye da tabanakul da kuma bagaden, ya rataye labule a ƙofar shiga filin. Da haka Musa ya gama aikin.
Erexit et atrium per gyrum tabernaculi et altaris, ducto in introitu eius tentorio. Postquam omnia perfecta sunt,
34 Sa’an nan girgije ya rufe Tentin Sujada sai ɗaukakar Ubangiji ta cika tabanakul.
operuit nubes tabernaculum testimonii, et gloria Domini implevit illud.
35 Musa bai iya shiga Tentin Sujada ba domin girgije ya riga ya sauka a kansa, ɗaukakar Ubangiji kuwa ta cika tabanakul.
Nec poterat Moyses ingredi tectum fœderis, nube operiente omnia, et maiestate Domini coruscante, quia cuncta nubes operuerat.
36 Cikin tafiyar Isra’ilawa duka, sukan kama tafiyarsu ne a duk sa’ad da girgijen ya tashi daga kan tabanakul.
Si quando nubes tabernaculum deserebat, proficiscebantur filii Israel per turmas suas:
37 Idan girgijen bai tashi ba, ba za su tashi ba, sai a ranar da ya tashi.
si pendebat desuper, manebant in eodem loco.
38 Gama a cikin tafiyarsu duka, girgijen Ubangiji yana kan tabanakul da rana, da dare kuwa wuta yake cikinsa domin dukan Isra’ilawa su gani.
Nubes quippe Domini incubabat per diem tabernaculo, et ignis in nocte, videntibus cunctis populis Israel per cunctas mansiones suas.

< Fitowa 40 >