< Fitowa 40 >

1 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa,
And Jehovah speaketh unto Moses, saying,
2 “Ka kafa tabanakul, da Tentin Sujada, a kan rana ta fari ga watan fari.
'On the first day of the month, in the first month, thou dost raise up the tabernacle of the tent of meeting,
3 Ka sa akwatin Alkawari a cikinsa, sa’an nan ka rufe shi da labule.
and hast set there the ark of the testimony, and hast covered over the ark with the vail,
4 Ka shigar da teburin ka shirya kayayyakin a kansa. Sa’an nan ka shigar da wurin ajiye fitilan ka kuma sa fitilunsa.
and hast brought in the table, and set its arrangement in order, and hast brought in the candlestick, and caused its lamps to go up.
5 Ka sa bagaden zinariya na ƙona turare a gaban akwatin Alkawari, ka kuma sa labule a ƙofar shiga tabanakul.
'And thou hast put the golden altar for perfume before the ark of the testimony, and hast put the covering of the opening to the tabernacle,
6 “Ka ajiye bagade na yin hadaya ta ƙonawa a gaban ƙofar tabanakul, da Tentin Sujada;
and hast put the altar of the burnt-offering before the opening of the tabernacle of the tent of meeting,
7 ka ajiye daron tsakanin Tentin Sujada da bagaden, ka kuma zuba ruwa a cikinsa.
and hast put the laver between the tent of meeting and the altar, and hast put water there.
8 Ka yi fili kewaye da shi, ka kuma sa labule a ƙofar shiga filin.
'And thou hast set the court round about, and hast placed the covering of the gate of the court,
9 “Ka ɗauki man shafewa ka shafe tabanakul da duka abin da yake cikinsa; ka keɓe shi da dukan kayayyakinsa, zai zama tsarkake.
and hast taken the anointing oil, and anointed the tabernacle, and all that [is] in it, and hallowed it, and all its vessels, and it hath been holy;
10 Sa’an nan ka shafe bagaden hadaya ta ƙonawa da kayansa; ka keɓe bagaden, zai zama mai tsarki.
and thou hast anointed the altar of the burnt-offering, and all its vessels, and sanctified the altar, and the altar hath been most holy;
11 Ka shafe daron da wurin ajiyarsa, ka kuma keɓe su.
and thou hast anointed the laver and its base, and sanctified it.
12 “Ka kawo Haruna da’ya’yansa a ƙofar Tentin Sujada ka wanke su da ruwa.
'And thou hast brought near Aaron and his sons unto the opening of the tent of meeting, and hast bathed them with water;
13 Sa’an nan ka sa wa Haruna tsarkakun riguna, ka shafe shi, ka kuma keɓe shi don yă yi mini hidima a matsayin firist.
and thou hast clothed Aaron with the holy garments, and anointed him, and sanctified him, and he hath acted as priest to Me.
14 Ka kawo’ya’yansa maza ka sa musu taguwoyi.
'And his sons thou dost bring near, and hast clothed them with coats,
15 Ka shafe su yadda ka shafe mahaifinsu, don su yi mini hidima a matsayin firistoci. Shafe musu man, zai sa su zama firistoci na ɗinɗinɗin, dukan zamanansu.”
and anointed them as thou hast anointed their father, and they have acted as priests to Me, and their anointing hath been to be to them for a priesthood age-during, to their generations.'
16 Musa ya aikata dukan kome yadda Ubangiji ya umarce shi.
And Moses doth according to all that Jehovah hath commanded him; so he hath done.
17 Da haka aka kafa tabanakul, a rana ta fari ga wata na fari a shekara ta biyu.
And it cometh to pass, in the first month, in the second year, in the first of the month, the tabernacle hath been raised up;
18 Sa’ad da Musa ya kafa tabanakul, ya sa rammuka a wurinsu, ya sa katakan, ya kuma sa sandunan, ya kakkafa dogayen sandunan.
and Moses raiseth up the tabernacle, and setteth its sockets, and placeth its boards, and placeth its bars, and raiseth its pillars,
19 Sa’an nan ya shimfiɗa tentin a bisa tabanakul, ya kuma sa murfi a bisa tentin, yadda Ubangiji ya umarce shi.
and spreadeth the tent over the tabernacle, and putteth the covering of the tent upon it above, as Jehovah hath commanded Moses.
20 Ya ɗauki dokokin Alkawari ya sa a cikin akwatin, ya kuma zura sandunan a zoban akwatin, sa’an nan ya sa murfin kafara a bisansa.
And he taketh and putteth the testimony unto the ark, and setteth the staves on the ark, and putteth the mercy-seat on the ark above;
21 Sai ya kawo akwatin a cikin tabanakul, ya kuma rataye labulen rufewa ya tsare akwatin Alkawarin, yadda Ubangiji ya umarce shi.
and bringeth in the ark unto the tabernacle, and placeth the vail of the covering, and covereth over the ark of the testimony, as Jehovah hath commanded Moses.
22 Musa ya sa teburin a Tentin Sujada, a gefen arewa na tabanakul waje da labulen.
And he putteth the table in the tent of meeting, on the side of the tabernacle northward, at the outside of the vail,
23 Ya shirya burodin a kai a gaban Ubangiji, yadda Ubangiji ya umarce shi.
and setteth in order upon it the arrangement of bread, before Jehovah, as Jehovah hath commanded Moses.
24 Ya sa wurin ajiye fitilan a Tentin Sujada ɗaura da teburin a gefen kudu na tabanakul
And he putteth the candlestick in the tent of meeting, over-against the table, on the side of the tabernacle southward,
25 ya kuma shirya fitilun a gaban Ubangiji, yadda Ubangiji ya umarce shi.
and causeth the lamps to go up before Jehovah, as Jehovah hath commanded Moses.
26 Musa ya sa bagaden zinariya a cikin Tentin Sujada a gaban labulen
And he setteth the golden altar in the tent of meeting, before the vail,
27 ya ƙone turare mai ƙanshi a kai, yadda Ubangiji ya umarce shi.
and maketh perfume on it — spice-perfume — as Jehovah hath commanded Moses.
28 Sa’an nan ya sa labule a ƙofar shiga na tabanakul.
And he setteth the covering of the opening to the tabernacle,
29 Ya sa bagaden hadaya ta ƙonawa kusa da ƙofar tabanakul, Tentin Sujada, sa’an nan ya miƙa hadaya ta ƙonawa da hadaya ta gari a kansa, yadda Ubangiji ya umarce shi.
and the altar of the burnt-offering he hath set at the opening of the tabernacle of the tent of meeting, and causeth the burnt-offering to go up upon it, and the present, as Jehovah hath commanded Moses.
30 Ya sa daro tsakanin Tentin Sujada da bagade, ya kuma zuba ruwa a cikinsa don wanki,
And he putteth the laver between the tent of meeting and the altar, and putteth water there for washing,
31 a cikin kuwa Musa da Haruna da’ya’yansa maza sukan wanke hannunsa da ƙafafunsu.
and Moses and Aaron and his sons have washed their hands and their feet at the same;
32 Sukan yi wanka a duk sa’ad da suka shiga Tentin Sujada, ko in suka kusaci bagade, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
in their going in unto the tent of meeting, and in their drawing near unto the altar, they wash, as Jehovah hath commanded Moses.
33 Sa’an nan Musa ya yi fili kewaye da tabanakul da kuma bagaden, ya rataye labule a ƙofar shiga filin. Da haka Musa ya gama aikin.
And he raiseth up the court round about the tabernacle, and about the altar, and placeth the covering of the gate of the court; and Moses completeth the work.
34 Sa’an nan girgije ya rufe Tentin Sujada sai ɗaukakar Ubangiji ta cika tabanakul.
And the cloud covereth the tent of meeting, and the honour of Jehovah hath filled the tabernacle;
35 Musa bai iya shiga Tentin Sujada ba domin girgije ya riga ya sauka a kansa, ɗaukakar Ubangiji kuwa ta cika tabanakul.
and Moses hath not been able to go in unto the tent of meeting, for the cloud hath tabernacled on it, and the honour of Jehovah hath filled the tabernacle.
36 Cikin tafiyar Isra’ilawa duka, sukan kama tafiyarsu ne a duk sa’ad da girgijen ya tashi daga kan tabanakul.
And in the going up of the cloud from off the tabernacle the sons of Israel journey in all their journeys;
37 Idan girgijen bai tashi ba, ba za su tashi ba, sai a ranar da ya tashi.
and if the cloud go not up then they journey not, until the day of its going up:
38 Gama a cikin tafiyarsu duka, girgijen Ubangiji yana kan tabanakul da rana, da dare kuwa wuta yake cikinsa domin dukan Isra’ilawa su gani.
for the cloud of Jehovah [is] on the tabernacle by day, and fire is in it by night, before the eyes of all the house of Israel in all their journeys.

< Fitowa 40 >