< Fitowa 40 >

1 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa,
And the LORD spoke unto Moses, saying:
2 “Ka kafa tabanakul, da Tentin Sujada, a kan rana ta fari ga watan fari.
'On the first day of the first month shalt thou rear up the tabernacle of the tent of meeting.
3 Ka sa akwatin Alkawari a cikinsa, sa’an nan ka rufe shi da labule.
And thou shalt put therein the ark of the testimony, and thou shalt screen the ark with the veil.
4 Ka shigar da teburin ka shirya kayayyakin a kansa. Sa’an nan ka shigar da wurin ajiye fitilan ka kuma sa fitilunsa.
And thou shalt bring in the table, and set in order the bread that is upon it; and thou shalt bring in the candlestick, and light the lamps thereof.
5 Ka sa bagaden zinariya na ƙona turare a gaban akwatin Alkawari, ka kuma sa labule a ƙofar shiga tabanakul.
And thou shalt set the golden altar for incense before the ark of the testimony, and put the screen of the door to the tabernacle.
6 “Ka ajiye bagade na yin hadaya ta ƙonawa a gaban ƙofar tabanakul, da Tentin Sujada;
And thou shalt set the altar of burnt-offering before the door of the tabernacle of the tent of meeting.
7 ka ajiye daron tsakanin Tentin Sujada da bagaden, ka kuma zuba ruwa a cikinsa.
And thou shalt set the laver between the tent of meeting and the altar, and shalt put water therein.
8 Ka yi fili kewaye da shi, ka kuma sa labule a ƙofar shiga filin.
And thou shalt set up the court round about, and hang up the screen of the gate of the court.
9 “Ka ɗauki man shafewa ka shafe tabanakul da duka abin da yake cikinsa; ka keɓe shi da dukan kayayyakinsa, zai zama tsarkake.
And thou shalt take the anointing oil, and anoint the tabernacle, and all that is therein, and shalt hallow it, and all the furniture thereof; and it shall be holy.
10 Sa’an nan ka shafe bagaden hadaya ta ƙonawa da kayansa; ka keɓe bagaden, zai zama mai tsarki.
And thou shalt anoint the altar of burnt-offering, and all its vessels, and sanctify the altar; and the altar shall be most holy.
11 Ka shafe daron da wurin ajiyarsa, ka kuma keɓe su.
And thou shalt anoint the laver and its base, and sanctify it.
12 “Ka kawo Haruna da’ya’yansa a ƙofar Tentin Sujada ka wanke su da ruwa.
And thou shalt bring Aaron and his sons unto the door of the tent of meeting, and shalt wash them with water.
13 Sa’an nan ka sa wa Haruna tsarkakun riguna, ka shafe shi, ka kuma keɓe shi don yă yi mini hidima a matsayin firist.
And thou shalt put upon Aaron the holy garments; and thou shalt anoint him, and sanctify him, that he may minister unto Me in the priest's office.
14 Ka kawo’ya’yansa maza ka sa musu taguwoyi.
And thou shalt bring his sons, and put tunics upon them.
15 Ka shafe su yadda ka shafe mahaifinsu, don su yi mini hidima a matsayin firistoci. Shafe musu man, zai sa su zama firistoci na ɗinɗinɗin, dukan zamanansu.”
And thou shalt anoint them, as thou didst anoint their father, that they may minister unto Me in the priest's office; and their anointing shall be to them for an everlasting priesthood throughout their generations.'
16 Musa ya aikata dukan kome yadda Ubangiji ya umarce shi.
Thus did Moses; according to all that the LORD commanded him, so did he.
17 Da haka aka kafa tabanakul, a rana ta fari ga wata na fari a shekara ta biyu.
And it came to pass in the first month in the second year, on the first day of the month, that the tabernacle was reared up.
18 Sa’ad da Musa ya kafa tabanakul, ya sa rammuka a wurinsu, ya sa katakan, ya kuma sa sandunan, ya kakkafa dogayen sandunan.
And Moses reared up the tabernacle, and laid its sockets, and set up the boards thereof, and put in the bars thereof, and reared up its pillars.
19 Sa’an nan ya shimfiɗa tentin a bisa tabanakul, ya kuma sa murfi a bisa tentin, yadda Ubangiji ya umarce shi.
And he spread the tent over the tabernacle, and put the covering of the tent above upon it; as the LORD commanded Moses.
20 Ya ɗauki dokokin Alkawari ya sa a cikin akwatin, ya kuma zura sandunan a zoban akwatin, sa’an nan ya sa murfin kafara a bisansa.
And he took and put the testimony into the ark, and set the staves on the ark, and put the ark-cover above upon the ark.
21 Sai ya kawo akwatin a cikin tabanakul, ya kuma rataye labulen rufewa ya tsare akwatin Alkawarin, yadda Ubangiji ya umarce shi.
And he brought the ark into the tabernacle, and set up the veil of the screen, and screened the ark of the testimony; as the LORD commanded Moses.
22 Musa ya sa teburin a Tentin Sujada, a gefen arewa na tabanakul waje da labulen.
And he put the table in the tent of meeting, upon the side of the tabernacle northward, without the veil.
23 Ya shirya burodin a kai a gaban Ubangiji, yadda Ubangiji ya umarce shi.
And he set a row of bread in order upon it before the LORD; as the LORD commanded Moses.
24 Ya sa wurin ajiye fitilan a Tentin Sujada ɗaura da teburin a gefen kudu na tabanakul
And he put the candlestick in the tent of meeting, over against the table, on the side of the tabernacle southward.
25 ya kuma shirya fitilun a gaban Ubangiji, yadda Ubangiji ya umarce shi.
And he lighted the lamps before the LORD; as the LORD commanded Moses.
26 Musa ya sa bagaden zinariya a cikin Tentin Sujada a gaban labulen
And he put the golden altar in the tent of meeting before the veil;
27 ya ƙone turare mai ƙanshi a kai, yadda Ubangiji ya umarce shi.
and he burnt thereon incense of sweet spices; as the LORD commanded Moses.
28 Sa’an nan ya sa labule a ƙofar shiga na tabanakul.
And he put the screen of the door to the tabernacle.
29 Ya sa bagaden hadaya ta ƙonawa kusa da ƙofar tabanakul, Tentin Sujada, sa’an nan ya miƙa hadaya ta ƙonawa da hadaya ta gari a kansa, yadda Ubangiji ya umarce shi.
And the altar of burnt-offering he set at the door of the tabernacle of the tent of meeting, and offered upon it the burnt-offering and the meal-offering; as the LORD commanded Moses.
30 Ya sa daro tsakanin Tentin Sujada da bagade, ya kuma zuba ruwa a cikinsa don wanki,
And he set the laver between the tent of meeting and the altar, and put water therein, wherewith to wash;
31 a cikin kuwa Musa da Haruna da’ya’yansa maza sukan wanke hannunsa da ƙafafunsu.
that Moses and Aaron and his sons might wash their hands and their feet thereat;
32 Sukan yi wanka a duk sa’ad da suka shiga Tentin Sujada, ko in suka kusaci bagade, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
when they went into the tent of meeting, and when they came near unto the altar, they should wash; as the LORD commanded Moses.
33 Sa’an nan Musa ya yi fili kewaye da tabanakul da kuma bagaden, ya rataye labule a ƙofar shiga filin. Da haka Musa ya gama aikin.
And he reared up the court round about the tabernacle and the altar, and set up the screen of the gate of the court. So Moses finished the work.
34 Sa’an nan girgije ya rufe Tentin Sujada sai ɗaukakar Ubangiji ta cika tabanakul.
Then the cloud covered the tent of meeting, and the glory of the LORD filled the tabernacle.
35 Musa bai iya shiga Tentin Sujada ba domin girgije ya riga ya sauka a kansa, ɗaukakar Ubangiji kuwa ta cika tabanakul.
And Moses was not able to enter into the tent of meeting, because the cloud abode thereon, and the glory of the LORD filled the tabernacle. —
36 Cikin tafiyar Isra’ilawa duka, sukan kama tafiyarsu ne a duk sa’ad da girgijen ya tashi daga kan tabanakul.
And whenever the cloud was taken up from over the tabernacle, the children of Israel went onward, throughout all their journeys.
37 Idan girgijen bai tashi ba, ba za su tashi ba, sai a ranar da ya tashi.
But if the cloud was not taken up, then they journeyed not till the day that it was taken up.
38 Gama a cikin tafiyarsu duka, girgijen Ubangiji yana kan tabanakul da rana, da dare kuwa wuta yake cikinsa domin dukan Isra’ilawa su gani.
For the cloud of the LORD was upon the tabernacle by day, and there was fire therein by night, in the sight of all the house of Israel, throughout all their journeys. —

< Fitowa 40 >