< Fitowa 4 >
1 Musa ya amsa ya ce, “In ba su gaskata ni ba, suka kuma ce, ‘Ubangiji bai bayyana gare ka ba fa’?”
Mısee inəxdun alidghıniy qele: – Sayid manbışis zal k'ırı alixhxhes diykkıne, zal haydepxha uvheene: «Rəbb vas dyagu deşva»?
2 Sai Ubangiji ya ce, “Mene ne wannan a hannunka?” Musa ya amsa ya ce, “Sanda.”
Manke Rəbbe eyhen: – Yiğne xıledın hucoone? Mısee eyhen: – Əsaa.
3 Sai Ubangiji ya ce, “Jefa shi ƙasa.” Musa ya jefa shi ƙasa, sai sandan ya zama maciji, Musa kuwa ya gudu daga gare shi.
Rəbbee eyhen: – Man ç'iyelqa dağeççe. Mısee ç'iyelqa dağetçumee, əsaa xoçelqa siyk'al. Mısar çisse hexvana.
4 Sai Ubangiji ya ce masa, “Sa hannunka ka ɗauke shi ta wutsiya.” Sai Musa ya miƙa hannu, ya kama macijin, macijin kuwa ya dawo sanda a hannunsa.
Rəbbee Mısayk'le eyhen: – Xıl hotku mana bı'ttike avqve. Mısee xıl hotku xoçe bı'ttike avquyng'a, mana xıle əsaalqa siviyk'al.
5 Ubangiji ya ce, “Wannan zai sa su ba da gaskiya cewa Ubangiji, Allah na kakanninsu, Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku, da kuma Allah da Yaƙub, ya bayyana gare ka.”
Rəbbee eyhen: – Ğu man kar he'e, İzrailybı hayepxhecen Rəbb, manbışde dekkaaşee, İbrahimee, I'saq'ee, Yaaq'ubee ı'bəədat ha'ana Allah, vas dyaguva.
6 Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Sa hannunka cikin rigarka.” Sai Musa ya sa hannunsa cikin rigarsa, sa’ad da ya fitar da shi, sai hannun ya a kuturce fari fat, kamar ƙanƙara.
Qiyğa Rəbbee meed eyhen: – Xıl eqanaqa k'eççe. Mısee xıl eqanaqa k'eççu qığavhumee, mang'un xıl ık'arıke yiz xhinne cagvara qexhe.
7 Sai Ubangiji ya ce, “Yanzu, mayar da hannunka a rigarka.” Sai Musa ya sa hannunsa cikin rigarsa, da ya fitar da shi, sai hannun ya koma kamar sauran jikinsa.
Qiyğa Rəbbee eyhen: – Xıl meed eqanaqa k'eççe. Mısee q'öd'es xıl eqanaqa k'eççu qığavhumee, mang'un xıl yug qexhe.
8 Sa’an nan Ubangiji ya ce, “In ba su gaskata ba, ko kuma ba su kula da mu’ujiza ta fari ba, wataƙila su gaskata da ta biyun.
Rəbbee eyhen: – Manbı yiğne ts'eppiyne əlaamatıl haydeepxhene, q'öb'esınçil vuxhesınbı.
9 Amma in ba su gaskata mu’ujizan nan biyu ba, ko kuwa ba su saurare ka ba, sai ka ɗibo ruwa daga Nilu, ka zuba a busasshiyar ƙasa. Ruwan da ka ɗebo daga kogin zai zama jini a ƙasar.”
Sayid manbışe val k'ırı ilydiyxhı q'öd'esde əlaamatılib haydeepxhene, Nil eyhene dameençe xhyan alyat'u ç'iyelqa haç'e'e. Manke man xhyan ebalqa sak'alas.
10 Musa ya ce wa Ubangiji, “Ya Ubangiji, ni ban mai iya magana ba ne, ban taɓa iya ba, ko a yanzu ma, bayan ka yi magana da ni, gama ni mai nauyin baki ne, mai nauyin harshe kuma.”
Mısee Rəbbık'le eyhen: – Xudaavanda, zasse şenker uftanra yuşana'as əxı' deş, həşder Ğu zaka yuşanı'ıyle qiyğar əxə deş. Zı yı'q'ra, g'idiyğal yuşana'a.
11 Ubangiji ya ce masa, “Wa ya ba mutum bakinsa? Wa yake maishe shi kurma ko bebe? Wa yake ba shi gani ko yă makanta shi? Ashe ba Ni Ubangiji ba ne?
Rəbbee mang'uk'le eyhen: – Şavaane insanıs miz huvu? Şavaane insanıke lalıy g'idiyxhena ha'a? Şavaane insanıs uleppı huvu? Şavaane insan bı'rq' qa'a? Nya'a Rəbbee, Zı dişde man gırgın ha'a?
12 Yanzu tafi, zan taimake ka ka yi magana, zan kuma koya maka abin da za ka faɗa.”
Həşdiylemee hora hak'ne, Zı vas eyhesınıd xət qa'asın, yuşana'asıd kumag ha'asın.
13 Amma Musa ya ce, “Ya Ubangiji, ina roƙonka, ka nemi wani ka aika.”
Mısee eyhen: – Hucoone ixhes, Xudaavanda, merna insan g'axıle.
14 Sai Ubangiji ya yi fushi da Musa ya ce, “Ɗan’uwanka Haruna Balawe, ba ya nan ne? Na san ya iya magana. Ya riga ya kama hanya don yă sadu da kai, zai kuma yi farin ciki sa’ad da ya gan ka.
Rəbbe Mısalqa qəl hav'u eyhen: – Nya'a Leviyne nasıleençena yiğna çoc Harun? Zak'le ats'an mana yugra yuşana'a. Həşde mana yiğne ögiylqa ı'qqə vor. Ğu g'acu mana şadxhesda.
15 Za ka yi masa magana. Ka kuma sa masa maganata a baki; zan kuma taimake ku magana, in koya muku abin da za ku yi.
Çocuka yuşane'e, hucooyiy eyhes ıkkan mang'us xət qe'e. Zı vuşde q'öngussana yuşana'as kumag ha'asın, hucooyiy ha'as ıkkanvad xət qa'asın.
16 Zai yi magana da mutane a madadinka, zai zama kamar bakinka, kai kuwa kamar Allah a gare shi.
Vas eyhes ıkkananbı, mang'vee insanaaşilqa hixhara'as. Ğunad mang'ulqa Yizın cuvab hixhar ha'as, manar yiğne cigee yuşan ha'as.
17 Amma ka ɗauki wannan sanda a hannunka domin yă aikata mu’ujizan.”
İn əsaa vaka aleet'e, ğu inçika əlaamatbı hagvas.
18 Sai Musa ya koma wurin Yetro surukinsa, ya ce masa, “Bari in koma wurin mutanena a Masar, in ga ko da mai rai a cikinsu.” Yetro ya ce, “Tafi, ka kuma sauka lafiya.”
Mısa cune abbateysqa İtronusqa sark'ıl eyhen: – Hasre zı Misireeqa ı'qqəs, ilyakkas yizın xınıbı avxucabee? İtronee eyhen: – Yugna yəq vuxhena.
19 Ubangiji ya riga ya gaya wa Musa a Midiyan, “Koma Masar, domin dukan mutanen da suke neman su kashe ka sun mutu.”
Midyanee Rəbbee Mısayk'le eyhen: – Misirqa sak'le, ğu gik'as ıkkanan gırgınbı hapt'ıynbı.
20 Sai Musa ya ɗauki matarsa da’ya’yansa maza, ya sa su a kan jaki, suka kama hanya zuwa Masar. Ya kuma ɗauki sandan Allah a hannunsa.
Mısee dixbıyiy xhunaşşe əməlelqa gyav'u, Allahee uvhuyn əsaayıd xılyaqa alyat'u Misirqa yəqqıl gexha.
21 Ubangiji ya ce wa Musa, “Bayan ka koma Masar, ka tabbata ka aikata dukan mu’ujizan da na sa cikin ikonka a gaban Fir’auna. Amma zan taurare zuciyarsa domin kada yă bar mutanen su tafi.
Rəbbee Mısayk'le eyhen: – Ğu Misirqa sak'ımee Zı vas xət qı'iyn gırgın əlaamatbı fironusne he'e. Zımee mang'uke hı't'iy qa'as, mang'veeyid millet g'aykkas deş.
22 Sa’an nan ka gaya wa Fir’auna, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce; Isra’ila shi ne ɗan farina,
Ğu fironuk'le eyhe: «Rəbbee inəxüdud eyhe: «İzrail Yizda ts'erriyna dix vorna.
23 na gaya maka, “Ka bar ɗana yă tafi domin yă yi mini sujada.” Amma ka ƙi ka bari yă tafi, saboda haka zan kashe ɗan farinka.’”
Zı vak'le uvhuyn, Zas ı'bəədat he'ecenva Yizda dix g'aykke! Ğumee mana g'aykkı deş. Həşde Zı mançil-allar yiğna ts'erriyna dix gik'as“».
24 Ya zama kuwa sa’ad da Musa yake masauki a kan hanya sai Ubangiji ya gamu da shi, ya nema ya kashe shi.
Yəqqə xəm g'ahaane cigee Rəbb Mısaysqa arı, mana gik'as ıkkiykan.
25 Amma Ziffora ta ɗauki dutsen ƙanƙara mai ci, ta yanke loɓar ɗanta ta taɓa ƙafafun Musa da shi. Ta ce, “Tabbatacce kai angon jini ne a gare ni.”
Mane gahıl, Tsiporee ek'na g'aye alyapt'ı dix sunnat hı'ı çike g'ayşuyn ç'ürüx Mısayne g'elybışik set'u eyhen: – Ğu həşde yizdemee ebana adamiy eyxhe.
26 Sai Ubangiji ya ƙyale shi. (A lokacin ta ce “angon jini,” tana nufin kaciya.)
Məxüb Rəbbee mang'uke xıl ts'ıts'a'ana. Dix sunnat hı'il-alla Tsiporee Mısayk'le «Ebana adamiyva» eyhe.
27 Ubangiji ya ce wa Haruna, “Tafi cikin hamada ka sadu da Musa.” Sai ya sadu da Musa a dutsen Allah, ya sumbace shi.
Sabara gah ılğevç'uyle qiyğa, Rəbbee Harunuk'le eyhen: – Mısayne ögiylqa sahreeqa hak'ne. Harunus Mısa Allahne suvaysne qızaxxımee, mang'vee Mısays ubbabı ha'a.
28 Sai Musa ya gaya wa Haruna dukan abin da Ubangiji ya aike yă faɗa, da kuma dukan mu’ujizan da ya umarce shi yă aikata.
Mısee Harunus Rəbbee cuk'le gırgın uvhiynbıyiy hagveva uvhuyn əlaamatbı yuşan ha'a.
29 Musa da Haruna suka tattara dukan dattawan Isra’ilawa,
Mıseeyiy Harunee İzrailin ağsaqqalar sav'umee,
30 sai Haruna ya gaya musu dukan abin da Ubangiji ya ce wa Musa. Ya kuma aikata mu’ujizan a gaban mutanen,
Rəbbee Mısayk'le uvhuyn gırgın kar Harunee yuşana'an. Qiyğaled mang'vee insanaaşine ögiyl man əlaamatbı hagva.
31 sai suka gaskata. Sa’ad da suka ji cewa Ubangiji ya damu da su, ya kuma ga azabarsu, sai suka durƙusa suka yi sujada.
İzrailybı manbışilqa hayebaxhenbı. Rəbbıkl'e manbışe opxhanna əq'üba g'avcuna, manbı məxüb g'alepçes deşva, manbışik'le g'ayxhımee, İzrailybı gugaybışil gyuv'ur ı'bəədatbı ha'a.