< Fitowa 4 >

1 Musa ya amsa ya ce, “In ba su gaskata ni ba, suka kuma ce, ‘Ubangiji bai bayyana gare ka ba fa’?”
Répondant, Moïse dit: Ils ne me croiront point, et ils n’écouteront point ma voix, mais ils diront: Non, le Seigneur ne t’a pas apparu.
2 Sai Ubangiji ya ce, “Mene ne wannan a hannunka?” Musa ya amsa ya ce, “Sanda.”
Le Seigneur lui dit donc: Qu’est-ce que tu tiens en ta main? Il répondit: Une verge.
3 Sai Ubangiji ya ce, “Jefa shi ƙasa.” Musa ya jefa shi ƙasa, sai sandan ya zama maciji, Musa kuwa ya gudu daga gare shi.
Le Seigneur ajouta: Jette-la à terre. Il la jeta, et elle fut changée en serpent; de sorte que Moïse s’enfuyait.
4 Sai Ubangiji ya ce masa, “Sa hannunka ka ɗauke shi ta wutsiya.” Sai Musa ya miƙa hannu, ya kama macijin, macijin kuwa ya dawo sanda a hannunsa.
Mais le Seigneur dit: Etends ta main et prends sa queue. Il l’étendit, saisit la queue, et elle fut changée en verge.
5 Ubangiji ya ce, “Wannan zai sa su ba da gaskiya cewa Ubangiji, Allah na kakanninsu, Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku, da kuma Allah da Yaƙub, ya bayyana gare ka.”
C’est afin qu’ils croient, ajouta-t-il, que t’a apparu le Seigneur Dieu de leurs pères, le Dieu d’Abraham, le Dieu d’Isaac et le Dieu de Jacob.
6 Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Sa hannunka cikin rigarka.” Sai Musa ya sa hannunsa cikin rigarsa, sa’ad da ya fitar da shi, sai hannun ya a kuturce fari fat, kamar ƙanƙara.
Et le Seigneur lui dit de nouveau: Mets ta main dans ton sein. Quand il l’eut mise dans son sein, il la retira lépreuse et blanche comme la neige.
7 Sai Ubangiji ya ce, “Yanzu, mayar da hannunka a rigarka.” Sai Musa ya sa hannunsa cikin rigarsa, da ya fitar da shi, sai hannun ya koma kamar sauran jikinsa.
Remets ta main dans ton sein, ajouta le Seigneur. Il la remit, et il la retira une seconde fois, et elle était semblable au reste de sa chair.
8 Sa’an nan Ubangiji ya ce, “In ba su gaskata ba, ko kuma ba su kula da mu’ujiza ta fari ba, wataƙila su gaskata da ta biyun.
S’ils ne te croient point, reprit le Seigneur, et s’ils n’entendent point le langage du premier signe, ils croiront à la parole du signe suivant.
9 Amma in ba su gaskata mu’ujizan nan biyu ba, ko kuwa ba su saurare ka ba, sai ka ɗibo ruwa daga Nilu, ka zuba a busasshiyar ƙasa. Ruwan da ka ɗebo daga kogin zai zama jini a ƙasar.”
Que s’ils ne croient pas même à ces deux signes, et n’écoutent pas ta voix, prends de l’eau du fleuve, et répands-la sur la terre, et tout ce que tu auras puisé au fleuve sera changé en sang.
10 Musa ya ce wa Ubangiji, “Ya Ubangiji, ni ban mai iya magana ba ne, ban taɓa iya ba, ko a yanzu ma, bayan ka yi magana da ni, gama ni mai nauyin baki ne, mai nauyin harshe kuma.”
Moïse dit: Je vous conjure. Seigneur, je n’ai pas la parole facile depuis hier et avant-hier; et même depuis que vous avez parlé à votre serviteur, j’ai la langue plus embarrassée et plus lente.
11 Ubangiji ya ce masa, “Wa ya ba mutum bakinsa? Wa yake maishe shi kurma ko bebe? Wa yake ba shi gani ko yă makanta shi? Ashe ba Ni Ubangiji ba ne?
Le Seigneur lui dit: Qui a fait la bouche de l’homme? ou qui a formé le muet et le sourd, le voyant et l’aveugle? n’est-ce pas moi?
12 Yanzu tafi, zan taimake ka ka yi magana, zan kuma koya maka abin da za ka faɗa.”
Va donc, et moi je serai en ta bouche, et je t’enseignerai ce que tu dois dire.
13 Amma Musa ya ce, “Ya Ubangiji, ina roƙonka, ka nemi wani ka aika.”
Mais lui: Je vous conjure, Seigneur, dit-il, envoyez celui que vous devez envoyer.
14 Sai Ubangiji ya yi fushi da Musa ya ce, “Ɗan’uwanka Haruna Balawe, ba ya nan ne? Na san ya iya magana. Ya riga ya kama hanya don yă sadu da kai, zai kuma yi farin ciki sa’ad da ya gan ka.
Le Seigneur, irrité contre Moïse, dit: Je sais qu’Aaron ton frère, le Lévite, parle avec facilité; voilà qu’il sort lui-même au devant de toi, et te voyant, il se réjouira en son cœur.
15 Za ka yi masa magana. Ka kuma sa masa maganata a baki; zan kuma taimake ku magana, in koya muku abin da za ku yi.
Parle-lui, et mets mes paroles en sa bouche: et moi, je serai en ta bouche et en sa bouche, et je vous montrerai ce que vous devez faire.
16 Zai yi magana da mutane a madadinka, zai zama kamar bakinka, kai kuwa kamar Allah a gare shi.
Lui parlera pour toi au peuple, et sera ta bouche; et toi, tu le guideras dans les choses qui regardent Dieu.
17 Amma ka ɗauki wannan sanda a hannunka domin yă aikata mu’ujizan.”
Prends aussi en ta main cette verge avec laquelle tu dois faire les signes.
18 Sai Musa ya koma wurin Yetro surukinsa, ya ce masa, “Bari in koma wurin mutanena a Masar, in ga ko da mai rai a cikinsu.” Yetro ya ce, “Tafi, ka kuma sauka lafiya.”
Moïse s’en alla, et retourna vers Jéthro, son beau-père, et lui dit: Je m’en irai et je retournerai vers mes frères en Egypte, pour que je voie s’ils vivent encore. Jéthro lui dit: Va en paix.
19 Ubangiji ya riga ya gaya wa Musa a Midiyan, “Koma Masar, domin dukan mutanen da suke neman su kashe ka sun mutu.”
Ainsi le Seigneur dit à Moïse à Madian: Va, et retourne en Egypte; car ils sont morts tous ceux qui cherchaient ton âme.
20 Sai Musa ya ɗauki matarsa da’ya’yansa maza, ya sa su a kan jaki, suka kama hanya zuwa Masar. Ya kuma ɗauki sandan Allah a hannunsa.
Moïse prit donc sa femme et ses fils, les mit sur l’âne et retourna en Egypte, portant la verge de Dieu en sa main.
21 Ubangiji ya ce wa Musa, “Bayan ka koma Masar, ka tabbata ka aikata dukan mu’ujizan da na sa cikin ikonka a gaban Fir’auna. Amma zan taurare zuciyarsa domin kada yă bar mutanen su tafi.
Et le Seigneur lui dit pendant qu’il retournait en Egypte: Aie soin de faire devant Pharaon tous les prodiges que j’ai mis en ta main; moi, j’endurcirai son cœur, et il ne laissera pas aller le peuple.
22 Sa’an nan ka gaya wa Fir’auna, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce; Isra’ila shi ne ɗan farina,
Et tu lui diras: Voici ce que dit le Seigneur: Mon fils premier-né est Israël.
23 na gaya maka, “Ka bar ɗana yă tafi domin yă yi mini sujada.” Amma ka ƙi ka bari yă tafi, saboda haka zan kashe ɗan farinka.’”
Je t’ai dit: Laisse aller mon fils, afin qu’il me serve, et tu n’as pas voulu le laisser: voilà que que moi, je tuerai ton fils premier-né.
24 Ya zama kuwa sa’ad da Musa yake masauki a kan hanya sai Ubangiji ya gamu da shi, ya nema ya kashe shi.
Or, comme Moïse était en chemin, le Seigneur se présenta à lui à l’hôtellerie, et il voulait le faire mourir.
25 Amma Ziffora ta ɗauki dutsen ƙanƙara mai ci, ta yanke loɓar ɗanta ta taɓa ƙafafun Musa da shi. Ta ce, “Tabbatacce kai angon jini ne a gare ni.”
Séphora prit aussitôt une pierre très aiguë et circoncit son fils, puis elle toucha ses pieds et dit: Tu m’es un époux de sang.
26 Sai Ubangiji ya ƙyale shi. (A lokacin ta ce “angon jini,” tana nufin kaciya.)
Et il le laissa, après qu’elle eut dit: Époux de sang, à cause de la circoncision.
27 Ubangiji ya ce wa Haruna, “Tafi cikin hamada ka sadu da Musa.” Sai ya sadu da Musa a dutsen Allah, ya sumbace shi.
Cependant le Seigneur dit à Aaron: Va à la rencontre de Moïse dans le désert. Et il alla au-devant de lui à la montagne de Dieu, et il l’embrassa.
28 Sai Musa ya gaya wa Haruna dukan abin da Ubangiji ya aike yă faɗa, da kuma dukan mu’ujizan da ya umarce shi yă aikata.
Et Moïse raconta à Aaron toutes les paroles par lesquelles le Seigneur l’avait envoyé, et les miracles qu’il lui avait commandés.
29 Musa da Haruna suka tattara dukan dattawan Isra’ilawa,
Ils vinrent donc ensemble, et ils assemblèrent tous les anciens des enfants d’Israël.
30 sai Haruna ya gaya musu dukan abin da Ubangiji ya ce wa Musa. Ya kuma aikata mu’ujizan a gaban mutanen,
Et Aaron raconta toutes les paroles que le Seigneur avait dites à Moïse; et il fit les miracles devant le peuple.
31 sai suka gaskata. Sa’ad da suka ji cewa Ubangiji ya damu da su, ya kuma ga azabarsu, sai suka durƙusa suka yi sujada.
Et le peuple crut. C’est ainsi qu’ils apprirent que le Seigneur avait visité les enfants d’Israël, et qu’il avait regardé leur affliction: et inclinés ils adorèrent.

< Fitowa 4 >