< Fitowa 4 >
1 Musa ya amsa ya ce, “In ba su gaskata ni ba, suka kuma ce, ‘Ubangiji bai bayyana gare ka ba fa’?”
And he answered Moses and he said and here! not they will believe me and not they will listen to voice my for they will say not he appeared to you Yahweh.
2 Sai Ubangiji ya ce, “Mene ne wannan a hannunka?” Musa ya amsa ya ce, “Sanda.”
And he said to him Yahweh (what [is] this? *Q(K)*) [is] in hand your and he said a staff.
3 Sai Ubangiji ya ce, “Jefa shi ƙasa.” Musa ya jefa shi ƙasa, sai sandan ya zama maciji, Musa kuwa ya gudu daga gare shi.
And he said throw it [the] ground towards and he threw it [the] ground towards and it became a snake and he fled Moses from before it.
4 Sai Ubangiji ya ce masa, “Sa hannunka ka ɗauke shi ta wutsiya.” Sai Musa ya miƙa hannu, ya kama macijin, macijin kuwa ya dawo sanda a hannunsa.
And he said Yahweh to Moses stretch out hand your and hold on tail its and he stretched out hand his and he took hold on it and it became a staff in hand his.
5 Ubangiji ya ce, “Wannan zai sa su ba da gaskiya cewa Ubangiji, Allah na kakanninsu, Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku, da kuma Allah da Yaƙub, ya bayyana gare ka.”
So that they may believe that he appeared to you Yahweh [the] God ancestors their [the] God of Abraham [the] God of Isaac and [the] God of Jacob.
6 Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Sa hannunka cikin rigarka.” Sai Musa ya sa hannunsa cikin rigarsa, sa’ad da ya fitar da shi, sai hannun ya a kuturce fari fat, kamar ƙanƙara.
And he said Yahweh to him again put please hand your in bosom your and he put hand his in bosom his and he brought out it and there! hand his [was] leprous like snow.
7 Sai Ubangiji ya ce, “Yanzu, mayar da hannunka a rigarka.” Sai Musa ya sa hannunsa cikin rigarsa, da ya fitar da shi, sai hannun ya koma kamar sauran jikinsa.
And he said return hand your into bosom your and he returned hand his into bosom his and he brought out it from bosom his and there! it had turned back like flesh his.
8 Sa’an nan Ubangiji ya ce, “In ba su gaskata ba, ko kuma ba su kula da mu’ujiza ta fari ba, wataƙila su gaskata da ta biyun.
And it will be if not they will believe you and not they will listen to [the] voice of the sign former and they will believe [the] voice of the sign latter.
9 Amma in ba su gaskata mu’ujizan nan biyu ba, ko kuwa ba su saurare ka ba, sai ka ɗibo ruwa daga Nilu, ka zuba a busasshiyar ƙasa. Ruwan da ka ɗebo daga kogin zai zama jini a ƙasar.”
And it will be if not they will believe also [the] two the signs these and not they will listen! to voice your and you will take some of [the] water of the River and you will pour [it] out the dry ground and they will become the waters which you will take from the River and they will become blood on the dry ground.
10 Musa ya ce wa Ubangiji, “Ya Ubangiji, ni ban mai iya magana ba ne, ban taɓa iya ba, ko a yanzu ma, bayan ka yi magana da ni, gama ni mai nauyin baki ne, mai nauyin harshe kuma.”
And he said Moses to Yahweh pardon me O Lord not [am] a man of words I neither from yesterday nor from three days ago nor from then speaking you to servant your for [am] heavy of mouth and heavy of tongue I.
11 Ubangiji ya ce masa, “Wa ya ba mutum bakinsa? Wa yake maishe shi kurma ko bebe? Wa yake ba shi gani ko yă makanta shi? Ashe ba Ni Ubangiji ba ne?
And he said Yahweh to him who? did he make a mouth of person or who? does he make dumb or deaf or seeing or blind ¿ not [do] I Yahweh.
12 Yanzu tafi, zan taimake ka ka yi magana, zan kuma koya maka abin da za ka faɗa.”
And therefore go and I I will be with mouth your and I will teach you [that] which you will say.
13 Amma Musa ya ce, “Ya Ubangiji, ina roƙonka, ka nemi wani ka aika.”
And he said pardon me O Lord send please by [the] hand of [whoever] you will send.
14 Sai Ubangiji ya yi fushi da Musa ya ce, “Ɗan’uwanka Haruna Balawe, ba ya nan ne? Na san ya iya magana. Ya riga ya kama hanya don yă sadu da kai, zai kuma yi farin ciki sa’ad da ya gan ka.
And it burned [the] anger of Yahweh on Moses and he said ¿ not [is] Aaron brother your the Levite I know that well he speaks he and also there! he [is] coming out to meet you and he will see you and he will be glad in heart his.
15 Za ka yi masa magana. Ka kuma sa masa maganata a baki; zan kuma taimake ku magana, in koya muku abin da za ku yi.
And you will speak to him and you will put the words in mouth his and I I will be with mouth your and with mouth his and I will teach you [that] which you will do!
16 Zai yi magana da mutane a madadinka, zai zama kamar bakinka, kai kuwa kamar Allah a gare shi.
And he will speak he for you to the people and it will be he he will become of you a mouth and you you will become of him a god.
17 Amma ka ɗauki wannan sanda a hannunka domin yă aikata mu’ujizan.”
And the staff this you will take in hand your which you will do with it the signs.
18 Sai Musa ya koma wurin Yetro surukinsa, ya ce masa, “Bari in koma wurin mutanena a Masar, in ga ko da mai rai a cikinsu.” Yetro ya ce, “Tafi, ka kuma sauka lafiya.”
And he went Moses and he returned - to Jethro father-in-law his and he said to him let me go please so I may return to relatives my who [are] in Egypt so I may see ¿ [are] still they living and he said Jethro to Moses go to peace.
19 Ubangiji ya riga ya gaya wa Musa a Midiyan, “Koma Masar, domin dukan mutanen da suke neman su kashe ka sun mutu.”
And he said Yahweh to Moses in Midian go return Egypt for they have died all the men who sought life your.
20 Sai Musa ya ɗauki matarsa da’ya’yansa maza, ya sa su a kan jaki, suka kama hanya zuwa Masar. Ya kuma ɗauki sandan Allah a hannunsa.
And he took Moses wife his and sons his and he made ride them on the donkey and he returned [the] land of towards Egypt and he took Moses [the] staff of God in hand his.
21 Ubangiji ya ce wa Musa, “Bayan ka koma Masar, ka tabbata ka aikata dukan mu’ujizan da na sa cikin ikonka a gaban Fir’auna. Amma zan taurare zuciyarsa domin kada yă bar mutanen su tafi.
And he said Yahweh to Moses when going you to return Egypt towards see all the wonders which I have put in hand your and you will do them before Pharaoh and I I will make strong heart his and not he will let go the people.
22 Sa’an nan ka gaya wa Fir’auna, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce; Isra’ila shi ne ɗan farina,
And you will say to Pharaoh thus he says Yahweh [is] son my firstborn my Israel.
23 na gaya maka, “Ka bar ɗana yă tafi domin yă yi mini sujada.” Amma ka ƙi ka bari yă tafi, saboda haka zan kashe ɗan farinka.’”
And I said to you let go son my so he may serve me and you refused to let go him here! I [am] about to kill son your firstborn your.
24 Ya zama kuwa sa’ad da Musa yake masauki a kan hanya sai Ubangiji ya gamu da shi, ya nema ya kashe shi.
And it was on the journey at the lodging place and he met him Yahweh and he sought to kill him.
25 Amma Ziffora ta ɗauki dutsen ƙanƙara mai ci, ta yanke loɓar ɗanta ta taɓa ƙafafun Musa da shi. Ta ce, “Tabbatacce kai angon jini ne a gare ni.”
And she took Zipporah a flint and she cut off [the] foreskin of son her and she made [it] touch feet his and she said that [are] a bridegroom of blood you to me.
26 Sai Ubangiji ya ƙyale shi. (A lokacin ta ce “angon jini,” tana nufin kaciya.)
And he withdrew from him then she said a bridegroom of blood to the circumcision.
27 Ubangiji ya ce wa Haruna, “Tafi cikin hamada ka sadu da Musa.” Sai ya sadu da Musa a dutsen Allah, ya sumbace shi.
And he said Yahweh to Aaron go to meet Moses the wilderness towards and he went and he met him at [the] mountain of God and he kissed him.
28 Sai Musa ya gaya wa Haruna dukan abin da Ubangiji ya aike yă faɗa, da kuma dukan mu’ujizan da ya umarce shi yă aikata.
And he told Moses to Aaron all [the] words of Yahweh which he had sent him and all the signs which he had commanded him.
29 Musa da Haruna suka tattara dukan dattawan Isra’ilawa,
And he went Moses and Aaron and they gathered all [the] elders of [the] people of Israel.
30 sai Haruna ya gaya musu dukan abin da Ubangiji ya ce wa Musa. Ya kuma aikata mu’ujizan a gaban mutanen,
And he spoke Aaron all the words which he had spoken Yahweh to Moses and he did the signs to [the] eyes of the people.
31 sai suka gaskata. Sa’ad da suka ji cewa Ubangiji ya damu da su, ya kuma ga azabarsu, sai suka durƙusa suka yi sujada.
And it believed the people and they heard that he had observed Yahweh [the] people of Israel and that he had seen affliction their and they bowed low and they bowed down.