< Fitowa 35 >

1 Musa ya tara dukan jama’ar Isra’ilawa ya ce musu, “Waɗannan su ne abubuwan da Ubangiji ya umarce ku, ku yi.
Potom sabra Mojsije sav zbor sinova Izrailjevih, i reèe im: ovo je zapovjedio Gospod da èinite:
2 Kwana shida za ku yi aiki, amma rana ta bakwai za tă zama rana mai tsarki, Asabbaci ne na hutu ga Ubangiji. Duk wanda ya yi aiki a wannan rana dole a kashe shi.
Šest dana da se radi, a sedmi da vam je svet, subota poèivanja Gospodnjega; ko bi radio u taj dan, da se pogubi.
3 Kada ku hura wuta a cikin duk mazauninku a ranar Asabbaci.”
Vatre ne ložite po stanovima svojim u dan subotni.
4 Musa ya ce wa dukan jama’ar Isra’ilawa, “Ga abin da Ubangiji ya umarta.
Još reèe Mojsije svemu zboru sinova Izrailjevih govoreæi: ovo je zapovjedio Gospod i rekao:
5 Daga cikin abin da kuke da shi, ku ɗauki kyauta domin Ubangiji, duk wanda yana niyya, sai yă kawo wa Ubangiji kyauta ta, “zinariya, azurfa da tagulla;
Skupite izmeðu sebe prilog Gospodu; ko god hoæe drage volje, neka donese prilog Gospodu: zlato i srebro i mjed,
6 shuɗi, shunayya da jan zare, lallausan lilin, da gashin akuya;
I porfiru i skerlet i crvac i tanko platno i kostrijet,
7 fatun rago da aka rina ja, da fatun shanun teku; da itacen ƙirya
I kože ovnujske crvene obojene i kože jazavèije i drvo sitim,
8 da man zaitun don fitila; da kayan yaji don man shafewa, da kuma turare mai ƙanshi;
I ulje za vidjelo, i mirise za ulje pomazanja i za kad mirisni,
9 duwatsun onis, da sauran duwatsu masu daraja waɗanda za a mammanne a efod da ƙyallen maƙalawa a ƙirji.
I kamenje onihovo, i kamenje za ukivanje po opleæku i po naprsniku.
10 “Duk waɗanda suke da fasaha a cikinku, su zo su yi dukan abin da Ubangiji ya umarta,
I koji su god vješti meðu vama neka doðu da rade što je zapovjedio Gospod:
11 “wato, aikin tabanakul da tentinsa tare da murfinsa, maɗauransa, katakansa, sandunansa da tussansa;
Šator, i naslon njegov, i pokrivaè njegov, i kuke njegove, i daske njegove, prijevornice njegove, stupove njegove i stopice njegove,
12 akwatin alkawari da sandunansa, murfin kafara da labulen da ya rufe shi;
Kovèeg, i poluge njegove, i zaklopac, i zavjes,
13 tebur da sandunansa, da dukan kayansa da kuma burodin kasancewa;
Sto, i poluge njegove i sve sprave njegove, i hljeb za postavljanje,
14 wurin ajiye fitila da yake don fitilu da kayayyakinsa, fitilu da mai don fitila;
I svijetnjak za vidjelo sa spravama njegovijem, i žiške njegove, i ulje za vidjelo,
15 bagaden turare da sandunansa, man shafewa da turare mai ƙanshi; da labulen ƙofar shiga tabanakul;
I oltar kadioni, i poluge njegove, i ulje pomazanja, i kad mirisni, i zavjes na vrata od šatora,
16 bagaden hadaya ta ƙonawa da rigarsa ta tagulla da sandunansa da duk kayayyakinsa, daron tagulla da wurin ajiye shi.
Oltar za žrtvu paljenicu, i rešetku njegovu od mjedi, poluge njegove i sve sprave njegove, umivaonicu i podnožje njezino,
17 Labulen filin tenti da sandunansa da tussansa, da kuma labulen ƙofar shiga fili;
Zavjese za trijem, stupove njegove i stopice njegove, i zavjes na vrata od trijema,
18 turakun tenti don tabanakul da kuma don filin, da igiyoyinsu;
Kolje za šator, i kolje za trijem s užima njihovijem.
19 saƙaƙƙun riguna na sawa don hidima cikin wuri mai tsarki da tsarkakakkun riguna na Haruna firist, da riguna don’ya’yansa maza lokacin da suke aiki a matsayin firistoci.”
Haljine službene za službu u svetinji, i haljine svete Aronu svešteniku, i haljine sinovima njegovijem za službu sveštenièku.
20 Sai dukan jama’ar Isra’ilawa suka janye daga fuskar Musa,
Tada otide sav zbor sinova Izrailjevijeh od Mojsija;
21 duk waɗanda suke da niyya, waɗanda kuma zukatansu suka motsa su, suka kawo kyautai wa Ubangiji, don aikin Tentin Sujada, don duk aikinsa, da don tsarkakakkun riguna.
I vratiše se, svaki kojega podiže srce njegovo i koga god duh pokrete dragovoljno, i donesoše prilog Gospodu za graðenje šatora od sastanka i za svu službu u njemu i za haljine svete.
22 Duk waɗanda suke da niyya, maza da mata, gaba ɗaya, suka kawo kayan ado na zinariya na kowane iri.’Yan kunne, da ƙawane, da mundaye, da kayayyakin zinariya iri-iri. Dukansu suka miƙa zinariyarsu a matsayin hadaya ga Ubangiji.
Dolaziše ljudi i žene, ko god bješe dragovoljna srca, i donosiše spone i oboce i prstenje i narukvice i svakojake nakite zlatne; i svaki donese prilog zlata Gospodu.
23 Kowane mutumin da yake da shuɗi, shunayya ko jan zare, ko lallausan lilin, ko gashin akuya, ko fatun rago da aka rina ja, ko fatun shanun teku, suka kawo.
Ko god imaše porfire, skerleta, crvca, tankoga platna, kostrijeti, koža ovnujskih crvenijeh obojenih i koža jazavèijih, svaki donošaše.
24 Masu miƙa kyautar azurfa, ko tagulla suka kawo su a matsayin kyautai ga Ubangiji, kuma kowane mutumin da yake da itacen ƙirya don kowane sashin aikin, ya kawo.
I ko god prilagaše srebro ili mjed, donošaše u prilog Gospodu; i u koga god bijaše drveta sitima, za svaku potrebu u službi donošaše.
25 Kowace mace mai fasaha ta kaɗa zare da hannuwanta, ta kuma kawo abin da ta kaɗa na shuɗi, shunayya, ko jan zare, ko lallausan lilin.
I sve žene vješte predoše svojim rukama, i donosiše što napredoše za porfiru, skerlet, crvac i tanko platno.
26 Kuma dukan matan da suke da niyya, suke kuma da fasaha, suka kaɗa gashin akuya.
I sve žene koje podiže srce njihovo i bijahu vješte, predoše kostrijet.
27 Shugabannin suka kawo duwatsun Onis. Da duwatsu masu daraja don a jera a kan efod da ƙyallen maƙalawa a ƙirji.
A glavari donosiše kamenje onihovo i kamenje za ukivanje po opleæku i po naprsniku,
28 Suka kawo kayan yaji da man zaitun don fitila da don man shafewa da kuma don turare mai ƙanshi.
I mirise i ulje za vidjelo i za ulje pomazanja i za kad mirisni.
29 Dukan mazan Isra’ilawa da matan da suke da niyya suka kawo wa Ubangiji kyautai na yardar rai, domin dukan aikin da Ubangiji ya umarce su ta bakin Musa.
Svi ljudi i žene, koje podiže dragovoljno srce da donose što treba za sve djelo koje Gospod zapovjedi preko Mojsija da se naèini, donesoše sinovi Izrailjevi dragovoljni prilog Gospodu.
30 Sa’an nan ya ce wa Isra’ilawa, “Duba Ubangiji ya zaɓi Bezalel ɗan Uri, ɗan Hur, daga kabilar Yahuda,
Tada reèe Mojsije sinovima Izrailjevim: vidite, Gospod pozva po imenu Veseleila sina Urije sina Orova od plemena Judina,
31 ya kuma cika shi da Ruhun Allah, da fasaha, azanci da kuma sani cikin dukan sana’ar hannu,
I napuni ga duha Božijega, mudrosti, razuma i znanja i vještine za svaki posao,
32 don yă ƙirƙiro zāne-zāne na gwaninta waɗanda za yi da zinariya, da azurfa da kuma tagulla.
Da vješto izmišlja kako se što radi od zlata i srebra i od mjedi,
33 Haka kuma wajen sassaƙar duwatsu na jerawa, da sassaƙar itace, da kowane irin aiki na gwaninta.
Da umije rezati kamenje i ukivati, da umije tesati drvo i raditi svaki posao vrlo vješto.
34 Ya kuma ba Bezalel da Oholiyab ɗan Ahisamak, daga kabilar Dan, iyawa don koya wa waɗansu.
I dade mu u srce, njemu i Elijavu sinu Ahisamahovu od plemena Danova, da mogu uèiti druge.
35 Ya cika su da fasaha don yin kowane irin aikin sana’a, zāne-zāne, ɗinke-ɗinke shuɗi, shunayya da jan zare, da lallausan lilin, da kuma masu yin saƙa, sun gwaninta ƙwarai cikin kowane irin aikin hannu da kuma zāne-zāne.
Napuni ih vještine da rade svaki posao, da kuju, tešu, vezu, i tkaju porfiru, skerlet, crvac i tanko platno, i da rade svakojake poslove vješto izmišljajuæi.

< Fitowa 35 >