< Fitowa 35 >

1 Musa ya tara dukan jama’ar Isra’ilawa ya ce musu, “Waɗannan su ne abubuwan da Ubangiji ya umarce ku, ku yi.
And Moses sent for all the children of Israel to come together, and said to them, This is what the Lord has said and these are his orders.
2 Kwana shida za ku yi aiki, amma rana ta bakwai za tă zama rana mai tsarki, Asabbaci ne na hutu ga Ubangiji. Duk wanda ya yi aiki a wannan rana dole a kashe shi.
Six days let work be done, but the seventh day is to be a holy day to you, a Sabbath of rest to the Lord; whoever does any work on that day is to be put to death.
3 Kada ku hura wuta a cikin duk mazauninku a ranar Asabbaci.”
No fire is to be lighted in any of your houses on the Sabbath day.
4 Musa ya ce wa dukan jama’ar Isra’ilawa, “Ga abin da Ubangiji ya umarta.
And Moses said to all the meeting of the children of Israel, This is the order which the Lord has given:
5 Daga cikin abin da kuke da shi, ku ɗauki kyauta domin Ubangiji, duk wanda yana niyya, sai yă kawo wa Ubangiji kyauta ta, “zinariya, azurfa da tagulla;
Take from among you an offering to the Lord; everyone who has the impulse in his heart, let him give his offering to the Lord; gold and silver and brass;
6 shuɗi, shunayya da jan zare, lallausan lilin, da gashin akuya;
And blue and purple and red and the best linen and goats' hair,
7 fatun rago da aka rina ja, da fatun shanun teku; da itacen ƙirya
And sheepskins coloured red, and leather, and hard wood,
8 da man zaitun don fitila; da kayan yaji don man shafewa, da kuma turare mai ƙanshi;
And oil for the lights, and spices for the holy oil and for the sweet perfumes for burning.
9 duwatsun onis, da sauran duwatsu masu daraja waɗanda za a mammanne a efod da ƙyallen maƙalawa a ƙirji.
And beryls and jewels to be cut for the ephod and for the priest's bag.
10 “Duk waɗanda suke da fasaha a cikinku, su zo su yi dukan abin da Ubangiji ya umarta,
And let every wise-hearted man among you come and make whatever has been ordered by the Lord;
11 “wato, aikin tabanakul da tentinsa tare da murfinsa, maɗauransa, katakansa, sandunansa da tussansa;
The House and its tent and its cover, its hooks and its boards, its rods and its pillars and its bases;
12 akwatin alkawari da sandunansa, murfin kafara da labulen da ya rufe shi;
The ark with its cover and its rods and the veil hanging before it;
13 tebur da sandunansa, da dukan kayansa da kuma burodin kasancewa;
The table and its rods and all its vessels, and the holy bread;
14 wurin ajiye fitila da yake don fitilu da kayayyakinsa, fitilu da mai don fitila;
And the support for the lights, with its vessels and its lights and the oil for the light;
15 bagaden turare da sandunansa, man shafewa da turare mai ƙanshi; da labulen ƙofar shiga tabanakul;
And the altar for burning spices, with its rods, and the holy oil and the sweet perfume, and the curtain for the door, at the door of the House;
16 bagaden hadaya ta ƙonawa da rigarsa ta tagulla da sandunansa da duk kayayyakinsa, daron tagulla da wurin ajiye shi.
The altar of burned offerings, with its network of brass, its rods, and all its vessels, the washing-vessel and its base;
17 Labulen filin tenti da sandunansa da tussansa, da kuma labulen ƙofar shiga fili;
The hangings for the open space, its pillars and their bases, and the curtain for the doorway;
18 turakun tenti don tabanakul da kuma don filin, da igiyoyinsu;
The nails for the House, and the nails for the open space and their cords;
19 saƙaƙƙun riguna na sawa don hidima cikin wuri mai tsarki da tsarkakakkun riguna na Haruna firist, da riguna don’ya’yansa maza lokacin da suke aiki a matsayin firistoci.”
The robes of needlework for the work of the holy place, the holy robes for Aaron the priest, and the robes for his sons when acting as priests.
20 Sai dukan jama’ar Isra’ilawa suka janye daga fuskar Musa,
And all the children of Israel went away from Moses.
21 duk waɗanda suke da niyya, waɗanda kuma zukatansu suka motsa su, suka kawo kyautai wa Ubangiji, don aikin Tentin Sujada, don duk aikinsa, da don tsarkakakkun riguna.
And everyone whose heart was moved, everyone who was guided by the impulse of his spirit, came with his offering for the Lord, for whatever was needed for the Tent of meeting and its work and for the holy robes.
22 Duk waɗanda suke da niyya, maza da mata, gaba ɗaya, suka kawo kayan ado na zinariya na kowane iri.’Yan kunne, da ƙawane, da mundaye, da kayayyakin zinariya iri-iri. Dukansu suka miƙa zinariyarsu a matsayin hadaya ga Ubangiji.
They came, men and women, all who were ready to give, and gave pins and nose-rings and finger-rings and neck-ornaments, all of gold; everyone gave an offering of gold to the Lord.
23 Kowane mutumin da yake da shuɗi, shunayya ko jan zare, ko lallausan lilin, ko gashin akuya, ko fatun rago da aka rina ja, ko fatun shanun teku, suka kawo.
And everyone who had blue and purple and red and the best linen and goats' hair and sheepskins coloured red and leather, gave them.
24 Masu miƙa kyautar azurfa, ko tagulla suka kawo su a matsayin kyautai ga Ubangiji, kuma kowane mutumin da yake da itacen ƙirya don kowane sashin aikin, ya kawo.
Everyone who had silver and brass gave an offering of them to the Lord; and everyone who had hard wood, such as was needed for the work, gave it.
25 Kowace mace mai fasaha ta kaɗa zare da hannuwanta, ta kuma kawo abin da ta kaɗa na shuɗi, shunayya, ko jan zare, ko lallausan lilin.
And all the women who were expert with their hands, made cloth, and gave the work of their hands, blue and purple and red and the best linen.
26 Kuma dukan matan da suke da niyya, suke kuma da fasaha, suka kaɗa gashin akuya.
And those women who had the knowledge, made the goats' hair into cloth.
27 Shugabannin suka kawo duwatsun Onis. Da duwatsu masu daraja don a jera a kan efod da ƙyallen maƙalawa a ƙirji.
And the rulers gave the beryls and the cut jewels for the ephod and the priest's bag;
28 Suka kawo kayan yaji da man zaitun don fitila da don man shafewa da kuma don turare mai ƙanshi.
And the spice and the oil for the light, and the holy oil and the sweet perfumes.
29 Dukan mazan Isra’ilawa da matan da suke da niyya suka kawo wa Ubangiji kyautai na yardar rai, domin dukan aikin da Ubangiji ya umarce su ta bakin Musa.
The children of Israel, every man and woman, from the impulse of their hearts, gave their offerings freely to the Lord for the work which the Lord had given Moses orders to have done.
30 Sa’an nan ya ce wa Isra’ilawa, “Duba Ubangiji ya zaɓi Bezalel ɗan Uri, ɗan Hur, daga kabilar Yahuda,
And Moses said to the children of Israel, See, the Lord has made selection of Bezalel, the son of Uri, the son of Hur, of the tribe of Judah;
31 ya kuma cika shi da Ruhun Allah, da fasaha, azanci da kuma sani cikin dukan sana’ar hannu,
And he has made him full of the spirit of God, in all wisdom and knowledge and art of every sort;
32 don yă ƙirƙiro zāne-zāne na gwaninta waɗanda za yi da zinariya, da azurfa da kuma tagulla.
As an expert designer of beautiful things, working in gold and silver and brass;
33 Haka kuma wajen sassaƙar duwatsu na jerawa, da sassaƙar itace, da kowane irin aiki na gwaninta.
Trained in the cutting of stones and the ornamenting of wood and in every sort of handwork.
34 Ya kuma ba Bezalel da Oholiyab ɗan Ahisamak, daga kabilar Dan, iyawa don koya wa waɗansu.
And he has given to him, and to Oholiab, the son of Ahisamach, of the tribe of Dan, the power of training others.
35 Ya cika su da fasaha don yin kowane irin aikin sana’a, zāne-zāne, ɗinke-ɗinke shuɗi, shunayya da jan zare, da lallausan lilin, da kuma masu yin saƙa, sun gwaninta ƙwarai cikin kowane irin aikin hannu da kuma zāne-zāne.
To them he has given knowledge of all the arts of the handworker, of the designer, and the expert workman; of the maker of needlework in blue and purple and red and the best linen, and of the maker of cloth; in all the arts of the designer and the trained workman they are expert.

< Fitowa 35 >