< Fitowa 33 >
1 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka bar wannan wuri, kai da mutanen da ka fito da su daga Masar, ka haura zuwa ƙasar da na alkawarta da rantsuwa wa Ibrahim, Ishaku da Yaƙub cewa, ‘Zan ba zuriyarka.’
Yahweh falou a Moisés: “Parta, suba daqui, você e o povo que você criou da terra do Egito, para a terra da qual eu jurei a Abraão, a Isaac e a Jacó, dizendo: 'Eu o darei à sua descendência'.
2 Zan aika da mala’ika a gabanka in kuma kori Kan’aniyawa, Amoriyawa, Hittiyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa.
Enviarei um anjo diante de vocês; e expulsarei os cananeus, os amorreus, e os hititas, e os perizeus, os hivitas, e os jebuseus.
3 Ka haura zuwa ƙasar da take zub da madara da zuma. Amma ba zan tafi tare da ku ba, saboda ku mutane ne masu taurinkai domin mai yiwuwa in hallaka ku a hanya.”
Ide a uma terra que flui com leite e mel; mas não subirei entre vós, pois sois um povo de pescoço duro, para que eu não vos consuma no caminho”.
4 Da mutane suka ji wannan mugun magana, sai suka fara makoki. Ba kuma wanda ya sa kayan ado.
Quando as pessoas ouviram esta má notícia, lamentaram; e ninguém colocou suas jóias.
5 Gama Ubangiji ya riga ya ce wa Musa, “Ka faɗa wa Isra’ilawa, ‘Ku mutane ne masu taurinkai. In na yi tafiya da ku ko na ɗan lokaci, mai yiwuwa in hallaka ku. Yanzu sai ku tuɓe kayan adonku, zan kuwa yanke shawara a kan abin da zan yi da ku.’”
Yahweh havia dito a Moisés: “Diga aos filhos de Israel: 'Vocês são um povo de pescoço duro'. Se eu subisse entre vocês por um momento, eu os consumiria”. Portanto, agora tirem suas jóias de vocês, para que eu possa saber o que fazer com vocês””.
6 Saboda haka Isra’ilawa suka tuttuɓe kayan adonsu a Dutsen Horeb.
As crianças de Israel se despojaram de suas jóias do Monte Horeb em diante.
7 Musa fa ya saba ɗaukan tenti yă kafa shi a bayan sansani da ɗan nisa, yana kiransa “Tentin Sujada.” Duk wanda yake neman wani abu daga wurin Ubangiji sai yă tafi Tentin Sujada a bayan sansani.
Agora Moisés costumava pegar a tenda e armá-la fora do acampamento, longe do acampamento, e ele a chamava de “A Tenda do Encontro”. Todos que procuravam Yahweh saíam para a Tenda do Encontro, que ficava fora do acampamento.
8 A sa’ad da kuma Musa ya fita zuwa Tentin, dukan mutanen sukan tashi su tsaya a ƙofofin tentinsu, suna kallon Musa, sai ya shiga tentin.
Quando Moisés saiu para a Tenda, todo o povo se levantou e ficou de pé, todos à porta de sua tenda, e observou Moisés, até que ele entrasse na Tenda.
9 Yayinda Musa ya shiga cikin tentin, sai al’amudin girgije yă sauko, yă tsaya a ƙofar yayinda Ubangiji yana magana da Musa.
Quando Moisés entrou na Tenda, a coluna de nuvem desceu, ficou à porta da Tenda, e Yahweh falou com Moisés.
10 Lokacin da mutane suka ga al’amudin girgije a tsaye a ƙofar tentin, sai duk su miƙe tsaye su yi sujada, kowa a ƙofar tentinsa.
Todas as pessoas viram a coluna de nuvem ficar à porta da Tenda, e todas as pessoas se levantaram e adoraram, todas à porta de suas tendas.
11 Ubangiji yakan yi magana da Musa fuska da fuska, kamar yadda mutum yake magana da abokinsa. Sa’an nan Musa yă koma sansani, amma saurayin nan Yoshuwa ɗan Nun mai taimakonsa ba ya barin tentin.
Javé falou com Moisés cara a cara, como um homem fala com seu amigo. Ele se transformou novamente no acampamento, mas seu servo Josué, o filho de Freira, um jovem, não se afastou da Tenda.
12 Musa ya ce wa Ubangiji, “Kana ta faɗa mini cewa, ‘Ka jagoranci mutane nan,’ amma ba ka faɗa mini wanda zai tafi tare da ni ba. Ga shi ka ƙara ce mini, ‘Na san ka, na san sunanka, ka kuma sami tagomashi a wurina.’
Moisés disse a Javé: “Eis que me dizes: 'Trazei este povo'; e não me deixastes saber quem enviareis comigo. Mas você disse: 'Conheço você pelo nome, e você também encontrou um favor na minha vista'.
13 In ka ji daɗina, ka koya mini hanyarka don in san ka, in kuma ci gaba da samun tagomashi daga gare ka. Ka tuna cewa wannan al’umma mutanenka ne.”
Agora, portanto, se eu encontrei favor à sua vista, mostre-me seu caminho, agora, para que eu possa conhecê-lo, para que eu possa encontrar favor à sua vista; e considere que esta nação é seu povo”.
14 Ubangiji ya amsa ya ce, “Zan tafi tare da kai, zan kuma rage maka nauyin kaya.”
Ele disse: “Minha presença irá com você, e eu lhe darei descanso”.
15 Musa kuwa ya ce masa, “In ba za tă tafi tare da mu ba, to, kada ka ɗaga mu daga nan.
Moisés lhe disse: “Se sua presença não for comigo, não nos carregue daqui para cima.
16 Yaya wani zai sani ko ka ji daɗina da kuma mutanenka, in ba ka tafi tare da mu ba? Mene ne kuma zai bambanta ni da mutanenka daga sauran jama’ar da suke a duniya?”
Pois como as pessoas saberiam que encontrei favor em sua vista, eu e seu povo? Não é que você vai conosco, para que estejamos separados, eu e seu povo, de todas as pessoas que estão na superfície da terra”?
17 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Zan yi yadda ka faɗa, gama ka sami tagomashi a wurina, na san ka, na kuma san sunanka.”
Yahweh disse a Moisés: “Eu farei isto também que você falou; pois você encontrou favor à minha vista, e eu o conheço pelo nome”.
18 Musa kuwa ya ce, “To, ka nuna mini ɗaukakarka.”
Moisés disse: “Por favor, mostre-me sua glória”.
19 Sai Ubangiji ya ce, “Zan wuce a gabanka, Ni Ubangiji zan yi shelar sunana a gabanka. Zan yi alheri ga duk wanda na so in yi masa alheri, zan nuna jinƙai ga duk wanda na so in yi masa jinƙai.
Ele disse: “Farei passar toda a minha bondade diante de vocês e proclamarei o nome de Javé diante de vocês”. Eu serei gracioso para com quem eu for gracioso, e terei misericórdia de quem eu for misericordioso”.
20 Amma ya ce, ba za ka ga fuskata ba, don ba mutumin da zai gan ni yă rayu.”
Ele disse: “Você não pode ver meu rosto, pois o homem pode não me ver e viver”.
21 Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Ga wani wuri kusa da ni inda za ka tsaya bisa dutsen.
Yahweh também disse: “Eis que há um lugar ao meu lado, e tu estarás sobre a rocha”.
22 A sa’ad da ɗaukakata tana wucewa, zan sa ka a cikin tsaguwar dutsen, in rufe ka da hannuna har sai na wuce.
Acontecerá, enquanto minha glória passar, que eu te colocarei numa fenda da rocha, e te cobrirei com minha mão até que eu tenha passado;
23 Sa’an nan zan ɗauke hannuna, ka kuwa ga bayana; amma fuskata, ba za ka gani ba.”
então tirarei minha mão, e verás minhas costas; mas meu rosto não será visto”.