< Fitowa 33 >

1 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka bar wannan wuri, kai da mutanen da ka fito da su daga Masar, ka haura zuwa ƙasar da na alkawarta da rantsuwa wa Ibrahim, Ishaku da Yaƙub cewa, ‘Zan ba zuriyarka.’
خداوند به موسی فرمود: «اینجا را ترک کنید، تو و این قوم که از سرزمین مصر بیرون آوردی، و به سوی سرزمینی بروید که وعدهٔ آن را به ابراهیم، اسحاق و یعقوب داده‌ام، چون به آنها سوگند یاد کردم که آن را به فرزندان ایشان ببخشم.
2 Zan aika da mala’ika a gabanka in kuma kori Kan’aniyawa, Amoriyawa, Hittiyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa.
من فرشته‌ای پیشاپیش تو خواهم فرستاد تا کنعانی‌ها، اموری‌ها، حیتی‌ها، فرزی‌ها، حوی‌ها و یبوسی‌ها را بیرون خواهم راند.
3 Ka haura zuwa ƙasar da take zub da madara da zuma. Amma ba zan tafi tare da ku ba, saboda ku mutane ne masu taurinkai domin mai yiwuwa in hallaka ku a hanya.”
به سرزمینی بروید که شیر و عسل در آن جاری است. اما من در این سفر همراه شما نخواهم آمد، چون مردمی سرکش هستید و ممکن است شما را در بین راه هلاک کنم.»
4 Da mutane suka ji wannan mugun magana, sai suka fara makoki. Ba kuma wanda ya sa kayan ado.
وقتی قوم این سخنان را شنیدند ماتم گرفتند و هیچ‌کس زیورآلات بر خود نیاویخت.
5 Gama Ubangiji ya riga ya ce wa Musa, “Ka faɗa wa Isra’ilawa, ‘Ku mutane ne masu taurinkai. In na yi tafiya da ku ko na ɗan lokaci, mai yiwuwa in hallaka ku. Yanzu sai ku tuɓe kayan adonku, zan kuwa yanke shawara a kan abin da zan yi da ku.’”
چون خداوند به موسی فرموده بود به قوم اسرائیل بگوید: «شما مردمی سرکش هستید. اگر لحظه‌ای در میان شما باشم، شما را هلاک می‌کنم. پس تا زمانی که تکلیف شما را روشن نکرده‌ام، هر نوع آلات زینتی و جواهرات را از خود دور کنید.»
6 Saboda haka Isra’ilawa suka tuttuɓe kayan adonsu a Dutsen Horeb.
پس بنی‌اسرائیل بعد از عزیمت از کوه سینا، زیورآلات خود را کنار گذاشتند.
7 Musa fa ya saba ɗaukan tenti yă kafa shi a bayan sansani da ɗan nisa, yana kiransa “Tentin Sujada.” Duk wanda yake neman wani abu daga wurin Ubangiji sai yă tafi Tentin Sujada a bayan sansani.
از آن پس، موسی خیمهٔ مقدّس را که «خیمهٔ ملاقات» نامگذاری کرده بود، همیشه بیرون از اردوگاه بنی‌اسرائیل بر پا می‌کرد و کسانی که می‌خواستند با خداوند راز و نیاز کنند، به آنجا می‌رفتند.
8 A sa’ad da kuma Musa ya fita zuwa Tentin, dukan mutanen sukan tashi su tsaya a ƙofofin tentinsu, suna kallon Musa, sai ya shiga tentin.
هر وقت موسی به طرف این خیمهٔ می‌رفت، تمام قوم دم در خیمه‌های خود جمع می‌شدند و او را تماشا می‌کردند.
9 Yayinda Musa ya shiga cikin tentin, sai al’amudin girgije yă sauko, yă tsaya a ƙofar yayinda Ubangiji yana magana da Musa.
زمانی که موسی وارد خیمهٔ عبادت می‌شد، ستون ابر نازل شده بر مدخل خیمه می‌ایستاد و خدا با موسی صحبت می‌کرد.
10 Lokacin da mutane suka ga al’amudin girgije a tsaye a ƙofar tentin, sai duk su miƙe tsaye su yi sujada, kowa a ƙofar tentinsa.
قوم اسرائیل وقتی ستون ابر را می‌دیدند، در برابر در خیمه‌های خود به خاک افتاده خدا را پرستش می‌کردند.
11 Ubangiji yakan yi magana da Musa fuska da fuska, kamar yadda mutum yake magana da abokinsa. Sa’an nan Musa yă koma sansani, amma saurayin nan Yoshuwa ɗan Nun mai taimakonsa ba ya barin tentin.
خداوند مانند کسی که با دوست خود گفتگو کند، با موسی رو در رو گفتگو می‌کرد. سپس موسی به اردوگاه بازمی‌گشت، ولی دستیار جوان او یوشع، پسر نون، خیمه را ترک نمی‌کرد.
12 Musa ya ce wa Ubangiji, “Kana ta faɗa mini cewa, ‘Ka jagoranci mutane nan,’ amma ba ka faɗa mini wanda zai tafi tare da ni ba. Ga shi ka ƙara ce mini, ‘Na san ka, na san sunanka, ka kuma sami tagomashi a wurina.’
موسی به خداوند عرض کرد: «تو به من می‌گویی این قوم را به سرزمین موعود ببرم، ولی نمی‌گویی چه کسی را با من خواهی فرستاد. گفته‌ای:”تو را به نام می‌شناسم و مورد لطف من قرار گرفته‌ای.“
13 In ka ji daɗina, ka koya mini hanyarka don in san ka, in kuma ci gaba da samun tagomashi daga gare ka. Ka tuna cewa wannan al’umma mutanenka ne.”
پس اگر حقیقت اینطور است مرا به راهی که باید بروم راهنمایی کن تا تو را آن طور که باید بشناسم و به شایستگی در حضورت زندگی کنم. این مردم نیز قوم تو هستند، پس لطف خود را از ایشان دریغ مدار.»
14 Ubangiji ya amsa ya ce, “Zan tafi tare da kai, zan kuma rage maka nauyin kaya.”
خداوند در جواب موسی فرمود: «من خود همراه شما خواهم آمد و به شما آرامی خواهم بخشید.»
15 Musa kuwa ya ce masa, “In ba za tă tafi tare da mu ba, to, kada ka ɗaga mu daga nan.
آنگاه موسی به خداوند گفت: «اگر خودت با ما نمی‌آیی ما را نیز نگذار که از اینجا جلوتر رویم.
16 Yaya wani zai sani ko ka ji daɗina da kuma mutanenka, in ba ka tafi tare da mu ba? Mene ne kuma zai bambanta ni da mutanenka daga sauran jama’ar da suke a duniya?”
اگر تو همراه ما نیایی از کجا معلوم خواهد شد که من و قوم من مورد لطف تو قرار گرفته‌ایم و با سایر قومهای جهان فرق داریم؟»
17 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Zan yi yadda ka faɗa, gama ka sami tagomashi a wurina, na san ka, na kuma san sunanka.”
خداوند فرمود: «در این مورد هم دعای تو را اجابت می‌کنم، چون تو مورد لطف من قرار گرفته‌ای و تو را به نام می‌شناسم.»
18 Musa kuwa ya ce, “To, ka nuna mini ɗaukakarka.”
موسی عرض کرد: «استدعا دارم جلال خود را به من نشان دهی.»
19 Sai Ubangiji ya ce, “Zan wuce a gabanka, Ni Ubangiji zan yi shelar sunana a gabanka. Zan yi alheri ga duk wanda na so in yi masa alheri, zan nuna jinƙai ga duk wanda na so in yi masa jinƙai.
خداوند فرمود: «من تمامی نیکویی خود را از برابر تو عبور می‌دهم و نام خود، یهوه را در حضور تو ندا می‌کنم. من خداوند هستم و بر هر کس که بخواهم رحم می‌کنم و بر هر کس که بخواهم شفقت می‌کنم.
20 Amma ya ce, ba za ka ga fuskata ba, don ba mutumin da zai gan ni yă rayu.”
من نخواهم گذاشت چهرهٔ مرا ببینی، چون انسان نمی‌تواند مرا ببیند و زنده بماند.
21 Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Ga wani wuri kusa da ni inda za ka tsaya bisa dutsen.
حال برخیز و روی این صخره، کنار من بایست.
22 A sa’ad da ɗaukakata tana wucewa, zan sa ka a cikin tsaguwar dutsen, in rufe ka da hannuna har sai na wuce.
وقتی جلال من می‌گذرد، تو را در شکاف این صخره می‌گذارم و با دستم تو را می‌پوشانم تا از اینجا عبور کنم؛
23 Sa’an nan zan ɗauke hannuna, ka kuwa ga bayana; amma fuskata, ba za ka gani ba.”
سپس دست خود را برمی‌دارم تا مرا از پشت ببینی، اما چهرهٔ مرا نخواهی دید.»

< Fitowa 33 >