< Fitowa 33 >
1 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka bar wannan wuri, kai da mutanen da ka fito da su daga Masar, ka haura zuwa ƙasar da na alkawarta da rantsuwa wa Ibrahim, Ishaku da Yaƙub cewa, ‘Zan ba zuriyarka.’
Le hoe t’Iehovà amy Mosè, Mionjona, angao ty atoy, ihe naho ondaty nampiavote’o an-tane Mitsraimeo, homb’ an-tane nifantàko amy Avrahame, am’ Ietsàke naho am’ Iakòbe ami’ty hoe: Hatoloko amo tarira’oo izay.
2 Zan aika da mala’ika a gabanka in kuma kori Kan’aniyawa, Amoriyawa, Hittiyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa.
Le hahitriko hiaolo anahareo t’i Sorotàko, handroahako i nte-Kanàney, i nte-Amòrey naho i nte-Kìtey naho i nte-Perìzey, i nte-Kìvey vaho i nte-Iebòsey,
3 Ka haura zuwa ƙasar da take zub da madara da zuma. Amma ba zan tafi tare da ku ba, saboda ku mutane ne masu taurinkai domin mai yiwuwa in hallaka ku a hanya.”
mb’an-tane kararahen-dronono naho tantele añe; fa tsy hionjom-beo añivo’o ao iraho kera habotseko an-dalambey, ie ondaty gan-katoke.
4 Da mutane suka ji wannan mugun magana, sai suka fara makoki. Ba kuma wanda ya sa kayan ado.
Ie nahajanjiñe i tsara maràñe zay ondatio le nangoihoy vaho tsy ama’e ty niravake,
5 Gama Ubangiji ya riga ya ce wa Musa, “Ka faɗa wa Isra’ilawa, ‘Ku mutane ne masu taurinkai. In na yi tafiya da ku ko na ɗan lokaci, mai yiwuwa in hallaka ku. Yanzu sai ku tuɓe kayan adonku, zan kuwa yanke shawara a kan abin da zan yi da ku.’”
amy natao’ Iehovà amy Mosè ty hoe, Ano ty hoe o ana’ Israeleo: Ondaty gam-pititia nahareo; aa naho nihelatse añivo’ areo ao iraho tsy ho nagodrako aniany hao? Ko miravak’ arè, hisafiriako ty hanoako.
6 Saboda haka Isra’ilawa suka tuttuɓe kayan adonsu a Dutsen Horeb.
Aa le hinalo’ o ana’ Israeleo am’iereo ze ravake naho bange ambohi-Koreba.
7 Musa fa ya saba ɗaukan tenti yă kafa shi a bayan sansani da ɗan nisa, yana kiransa “Tentin Sujada.” Duk wanda yake neman wani abu daga wurin Ubangiji sai yă tafi Tentin Sujada a bayan sansani.
Ie amy zay, nendese’ i Mosè i kibohoy vaho naore’e alafe’ i tobey, lavitse i tobey eñe, le nitokave’e ty hoe kibohom-pamantañañe. Aa le songa niavotse mb’ amy kivohom-pamantañañe alafe’ i tobey eiy ze nipay Iehovà.
8 A sa’ad da kuma Musa ya fita zuwa Tentin, dukan mutanen sukan tashi su tsaya a ƙofofin tentinsu, suna kallon Musa, sai ya shiga tentin.
Aa naho nienga mb’amy kibohotsey mb’ eo t’i Mosè, le hene niongake ondatio sambe nijohañe an-dala’ i kiboho’ey nandrèndreke i Mose ampara-piziliha’e an-kibohotse ao.
9 Yayinda Musa ya shiga cikin tentin, sai al’amudin girgije yă sauko, yă tsaya a ƙofar yayinda Ubangiji yana magana da Musa.
Aa naho nizilik’ an-kibohotse ao t’i Mosè, le nizotso mb’eo i rahoñe nijoalay nijohañe an-dala’ i kibohotsey, le nifanaontsy amy Mosè t’Iehovà.
10 Lokacin da mutane suka ga al’amudin girgije a tsaye a ƙofar tentin, sai duk su miƙe tsaye su yi sujada, kowa a ƙofar tentinsa.
Ie hene nahaisake i rahoñe nijoalay nijohañe an-dala’ i kibohotsey ondatio le sindre niongake ondatio vaho songa niambane an-dalan-kiboho’e.
11 Ubangiji yakan yi magana da Musa fuska da fuska, kamar yadda mutum yake magana da abokinsa. Sa’an nan Musa yă koma sansani, amma saurayin nan Yoshuwa ɗan Nun mai taimakonsa ba ya barin tentin.
Vaho nifanaontsy am-piatrefan-daharañe t’Iehovà naho i Mosè, manahake ty fifañòhahohàm-pirañetse. Aa ie nimpoly mb’an-tobe mb’eo, tsy nienga i kibohoy ty ajalahy atao Iehosoa ana’ i None mpitoro’e.
12 Musa ya ce wa Ubangiji, “Kana ta faɗa mini cewa, ‘Ka jagoranci mutane nan,’ amma ba ka faɗa mini wanda zai tafi tare da ni ba. Ga shi ka ƙara ce mini, ‘Na san ka, na san sunanka, ka kuma sami tagomashi a wurina.’
Hoe t’i Mosè am’ Iehovà: Ingo, i tsinara’o amako ty hoe: Ampionjono ondaty retoa; fa tsy nampandrendrehe’o ahy o hampindreze’o amakoo. Fa nanao ty hoe irehe, Fantako ami’ty tahina’o irehe vaho isoheñe am-pivazohoako.
13 In ka ji daɗina, ka koya mini hanyarka don in san ka, in kuma ci gaba da samun tagomashi daga gare ka. Ka tuna cewa wannan al’umma mutanenka ne.”
Aa naho nitendreke fañisohañe am-pihaino’o iraho le mihalaly ama’o, Atorò ahy o lala’oo, haharendrehako Azo, hahazoako falalàñe am-pihaino’o vaho ereñerèño te ondati’o ty fifeheañe toy.
14 Ubangiji ya amsa ya ce, “Zan tafi tare da kai, zan kuma rage maka nauyin kaya.”
Le hoe re: Hindre lia ama’o ty fiatrefako vaho hampitofàko.
15 Musa kuwa ya ce masa, “In ba za tă tafi tare da mu ba, to, kada ka ɗaga mu daga nan.
Aa le hoe ty navale’e: Naho tsy hiaolo anay ty fiatrefa’o le ko ampionjone’o boak’ etoa.
16 Yaya wani zai sani ko ka ji daɗina da kuma mutanenka, in ba ka tafi tare da mu ba? Mene ne kuma zai bambanta ni da mutanenka daga sauran jama’ar da suke a duniya?”
Aa ino ty hahafohinako henaneo t’ie nitendreke fañisohañe am-pihaino’o, izaho naho ondati’oo, lehe tsy mindre ama’ay irehe? ie hampiavaheñe amy ze hene ondaty ambone’ ty tane atoy, izaho naho ondati’oo?
17 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Zan yi yadda ka faɗa, gama ka sami tagomashi a wurina, na san ka, na kuma san sunanka.”
Hoe t’Iehovà amy Mosè, Toe hanoeko ka o sinaontsi’o anianio; amy te ihe nahaisa-pañosihañe am-pañenteako, toe fantako ami’ty añara’o.
18 Musa kuwa ya ce, “To, ka nuna mini ɗaukakarka.”
Le hoe re, Mihalaly ama’o, Ehe aboaho amako ty asi’o.
19 Sai Ubangiji ya ce, “Zan wuce a gabanka, Ni Ubangiji zan yi shelar sunana a gabanka. Zan yi alheri ga duk wanda na so in yi masa alheri, zan nuna jinƙai ga duk wanda na so in yi masa jinƙai.
Le hoe re: Hene hampiarieko añatrefa’o ty hasoako naho ho taroñeko aolo’o eo ty tahinañe ty hoe Iehovà; le hisoheko ze hisoheko vaho ho tretrezeko ze ho tretrezeko.
20 Amma ya ce, ba za ka ga fuskata ba, don ba mutumin da zai gan ni yă rayu.”
Hoe ka re: Tsy mete hañisake ty tareheko irehe; amy te tsy ho veloñe t’indaty mahaisak’ aze.
21 Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Ga wani wuri kusa da ni inda za ka tsaya bisa dutsen.
Aa hoe t’Iehovà, Ingo ty toetse marine’ ahy etia, mijohaña amo vatoo;
22 A sa’ad da ɗaukakata tana wucewa, zan sa ka a cikin tsaguwar dutsen, in rufe ka da hannuna har sai na wuce.
vaho ie miary eo ty engeko le hifireko an-tsifitsifi’ o vatoo irehe naho ho lombofa’ ty tañako t’ie miary;
23 Sa’an nan zan ɗauke hannuna, ka kuwa ga bayana; amma fuskata, ba za ka gani ba.”
le hasintako amy zao ty tañako vaho ho isa’o ty vòhoko fe tsy isaheñe ty tareheko.