< Fitowa 33 >
1 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka bar wannan wuri, kai da mutanen da ka fito da su daga Masar, ka haura zuwa ƙasar da na alkawarta da rantsuwa wa Ibrahim, Ishaku da Yaƙub cewa, ‘Zan ba zuriyarka.’
And the Lord said unto Moses, Depart, go up from here, thou and the people that thou hast brought up out of the land of Egypt, unto the land which I swore unto Abraham, to Isaac, and to Jacob, saying, Unto thy seed will I give it; —
2 Zan aika da mala’ika a gabanka in kuma kori Kan’aniyawa, Amoriyawa, Hittiyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa.
And I will send before thee an angel; and I will drive out the Canaanite, the Emorite, and the Hittite, and the Perizzite, the Hivite, and the Jebusite; —
3 Ka haura zuwa ƙasar da take zub da madara da zuma. Amma ba zan tafi tare da ku ba, saboda ku mutane ne masu taurinkai domin mai yiwuwa in hallaka ku a hanya.”
Unto a land flowing with milk and honey; for I will not go up in the midst of thee, because thou art a stiffnecked people; lest I consume thee on the way.
4 Da mutane suka ji wannan mugun magana, sai suka fara makoki. Ba kuma wanda ya sa kayan ado.
And when the people heard these evil tidings, they mourned; and no man did put his ornaments on him.
5 Gama Ubangiji ya riga ya ce wa Musa, “Ka faɗa wa Isra’ilawa, ‘Ku mutane ne masu taurinkai. In na yi tafiya da ku ko na ɗan lokaci, mai yiwuwa in hallaka ku. Yanzu sai ku tuɓe kayan adonku, zan kuwa yanke shawara a kan abin da zan yi da ku.’”
For the Lord had said unto Moses, Say unto the children of Israel, Ye are a stiffnecked people; should I go up one moment in the midst of thee, I would consume thee; now therefore put off thy ornaments from thee, and I shall know what I will do unto thee.
6 Saboda haka Isra’ilawa suka tuttuɓe kayan adonsu a Dutsen Horeb.
The children of Israel then stripped themselves of their ornaments [they wore] from [the time they were at] mount Horeb.
7 Musa fa ya saba ɗaukan tenti yă kafa shi a bayan sansani da ɗan nisa, yana kiransa “Tentin Sujada.” Duk wanda yake neman wani abu daga wurin Ubangiji sai yă tafi Tentin Sujada a bayan sansani.
And Moses took the tent, and pitched it without the camp, afar off from the camp, and called it, Tabernacle of the congregation; and it came to pass, that every one who sought [instruction of] the Lord went out unto the tabernacle of the congregation, which was without the camp.
8 A sa’ad da kuma Musa ya fita zuwa Tentin, dukan mutanen sukan tashi su tsaya a ƙofofin tentinsu, suna kallon Musa, sai ya shiga tentin.
And it came to pass, that when Moses went out unto the tent, all the people would rise up, and stand every man at the door of his tent, and look after Moses, until he was gone into the tent.
9 Yayinda Musa ya shiga cikin tentin, sai al’amudin girgije yă sauko, yă tsaya a ƙofar yayinda Ubangiji yana magana da Musa.
And it came to pass, that as Moses entered into the tent, the pillar of cloud descended, and stood at the door of the tent, and spoke with Moses.
10 Lokacin da mutane suka ga al’amudin girgije a tsaye a ƙofar tentin, sai duk su miƙe tsaye su yi sujada, kowa a ƙofar tentinsa.
And when all the people saw the pillar of cloud stand at the door of the tent: then all the people rose up and prostrated themselves, every man at the door of his tent.
11 Ubangiji yakan yi magana da Musa fuska da fuska, kamar yadda mutum yake magana da abokinsa. Sa’an nan Musa yă koma sansani, amma saurayin nan Yoshuwa ɗan Nun mai taimakonsa ba ya barin tentin.
And the Lord spoke unto Moses face to face, as a man speaketh unto his friend; and then he returned into the camp; but his servant, Joshua the son of Nun, a young man, departed not out of the tent.
12 Musa ya ce wa Ubangiji, “Kana ta faɗa mini cewa, ‘Ka jagoranci mutane nan,’ amma ba ka faɗa mini wanda zai tafi tare da ni ba. Ga shi ka ƙara ce mini, ‘Na san ka, na san sunanka, ka kuma sami tagomashi a wurina.’
And Moses said unto the Lord, See, thou sayest unto me, Bring up this people; but thou hast not let me know whom thou wilt send with me: and yet thou hast said, I have chosen thee by name, and thou hast also found grace in my eyes.
13 In ka ji daɗina, ka koya mini hanyarka don in san ka, in kuma ci gaba da samun tagomashi daga gare ka. Ka tuna cewa wannan al’umma mutanenka ne.”
Now, therefore, I pray thee, if I have found grace in thy eyes, do make me know thy way, that I may know thee, in order that I may find grace in thy eyes; and consider that this nation is thy people.
14 Ubangiji ya amsa ya ce, “Zan tafi tare da kai, zan kuma rage maka nauyin kaya.”
And he said, My presence shall go in advance, and I will give thee rest.
15 Musa kuwa ya ce masa, “In ba za tă tafi tare da mu ba, to, kada ka ɗaga mu daga nan.
And he said unto him, If thy presence go not [with us, ] carry us not up from here.
16 Yaya wani zai sani ko ka ji daɗina da kuma mutanenka, in ba ka tafi tare da mu ba? Mene ne kuma zai bambanta ni da mutanenka daga sauran jama’ar da suke a duniya?”
For wherein shall it be known in any wise that I have found grace in thy eyes, I with thy people? is it not in that thou goest with us? so shall we be distinguished, I and thy people, from all the people that are upon the face of the earth.
17 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Zan yi yadda ka faɗa, gama ka sami tagomashi a wurina, na san ka, na kuma san sunanka.”
And the Lord said unto Moses, Also this thing that thou hast spoken will I do; for thou hast found grace in my eyes, and I have chosen thee by name.
18 Musa kuwa ya ce, “To, ka nuna mini ɗaukakarka.”
And he said, Let me see, I beseech thee, thy glory.
19 Sai Ubangiji ya ce, “Zan wuce a gabanka, Ni Ubangiji zan yi shelar sunana a gabanka. Zan yi alheri ga duk wanda na so in yi masa alheri, zan nuna jinƙai ga duk wanda na so in yi masa jinƙai.
And he said, I will cause all my goodness to pass before thy face, and I will proclaim, by name, the Lord before thee; and I will be gracious to whom I will be gracious, and I will show mercy to whom I will show mercy.
20 Amma ya ce, ba za ka ga fuskata ba, don ba mutumin da zai gan ni yă rayu.”
And he said, Thou canst not see my face; for no man can see me, and live.
21 Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Ga wani wuri kusa da ni inda za ka tsaya bisa dutsen.
And the Lord said, Behold, there is a place by me, and thou shalt stand upon the rock:
22 A sa’ad da ɗaukakata tana wucewa, zan sa ka a cikin tsaguwar dutsen, in rufe ka da hannuna har sai na wuce.
And it shall come to pass, while my glory passeth by, that I will put thee in the cleft of the rock, and I will cover thee with my hand, until I have passed by.
23 Sa’an nan zan ɗauke hannuna, ka kuwa ga bayana; amma fuskata, ba za ka gani ba.”
And then I will take away my hand, and thou shalt see my back parts; but my face shall not be seen.