< Fitowa 32 >

1 Sa’ad da mutane suka ga Musa ya daɗe bai sauko daga dutse ba, sai suka taru kewaye da Haruna suka ce, “Zo, ka yi mana alloli waɗanda za su yi mana jagora. Game da wannan Musa wanda ya fitar da mu daga Masar dai, ba mu san abin da ya faru da shi ba.”
Quando o povo viu que Moisés demorou a descer da montanha, o povo se reuniu a Arão e lhe disse: “Vem, faze-nos deuses, que irão adiante de nós; pois quanto a este Moisés, o homem que nos tirou da terra do Egito, não sabemos o que aconteceu com ele”.
2 Haruna ya amsa musu ya ce, “Ku tuttuɓe zoban zinariya waɗanda suke kunnuwan matanku, da na’ya’yanku maza da mata, ku kawo mini.”
Aaron disse-lhes: “Tirem os anéis dourados, que estão nos ouvidos de suas esposas, de seus filhos e de suas filhas, e tragam-mos até mim”.
3 Saboda haka dukan mutane suka tuttuɓe’yan kunnensu suka kawo wa Haruna.
Todas as pessoas tiraram os anéis dourados que estavam em seus ouvidos, e os trouxeram para Aaron.
4 Sai ya karɓi abubuwan da suka ba shi, ya yi gunki na siffar ɗan maraƙi, ya sassaƙa shi da kayan aiki. Sa’ad da mutane suka gani, sai suka tā da murya suka ce, “Waɗannan su ne allolinku, ya Isra’ila, waɗanda suka fitar da ku daga Masar.”
Ele recebeu o que lhe entregaram, moldou-o com uma ferramenta de gravação e fez dele um bezerro moldado. Depois disseram: “Estes são seus deuses, Israel, que o trouxeram para fora da terra do Egito”.
5 Da Haruna ya ga haka, sai ya gina bagade a gaban ɗan maraƙi, ya yi shela ya ce, “Gobe akwai biki ga Ubangiji.”
Quando Aaron viu isto, construiu um altar diante dele; e Aaron fez uma proclamação, e disse: “Amanhã será uma festa para Yahweh”.
6 Saboda haka kashegari, mutane suka tashi da sassafe suka miƙa hadaya ta ƙonawa, da hadaya ta salama. Bayan haka suka zauna suka ci, suka sha, suka kuma tashi suka yi rawa.
Eles se levantaram cedo no dia seguinte, ofereceram holocaustos e trouxeram ofertas de paz; e as pessoas se sentaram para comer e beber, e se levantaram para brincar.
7 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Sauka, gama mutanenka, waɗanda ka fitar da su daga Masar sun ƙazantu.
Yahweh falou a Moisés: “Vai, desce; pois seu povo, que você criou fora da terra do Egito, se corrompeu!
8 Sun yi saurin juyawa daga abin da na umarce su, sun kuma yi wa kansu gunki na siffar ɗan maraƙi. Sun yi sujada ga ɗan maraƙi, suka yi hadaya gare shi, suka kuma ce, waɗannan su ne allolinka ya Isra’ila, waɗanda suka fito da kai daga Masar.”
Eles se afastaram rapidamente do caminho que eu lhes ordenei. Fizeram para si um bezerro moldado, adoraram-no e se sacrificaram a ele, e disseram: “Estes são os vossos deuses, Israel, que vos fizeram subir da terra do Egito”.
9 Ubangiji ya ce wa Musa, “Na ga waɗannan mutane, mutane ne masu taurinkai.”
Yahweh disse a Moisés: “Eu vi estas pessoas, e eis que são um povo de pescoço duro.
10 Yanzu ka bar ni kurum fushina yă yi ƙuna a kansu, in hallaka su. Sa’an nan in maishe ka al’umma mai girma.
Agora, portanto, deixai-me em paz, para que minha ira arda contra eles, e para que eu os consuma; e eu farei de vós uma grande nação”.
11 Amma Musa ya nemi tagomashin Ubangiji, Allahnsa ya ce, “Ya Ubangiji don me fushinka zai yi ƙuna a kan mutanenka, waɗanda ka fisshe su daga Masar da ikon hannunka mai girma?
Moisés implorou a Javé seu Deus, e disse: “Javé, por que sua ira arde contra seu povo, que você tirou da terra do Egito com grande poder e com uma mão poderosa?
12 Don me za ka sa Masarawa su ce, ‘Ai, da mugun nufi ne ya fito da su don yă shafe su daga fuskar duniya’? Ka juya daga fushinka mai zafi, ka ji tausayi, kada ka kawo masifa a kan mutanenka.
Por que os egípcios deveriam falar, dizendo: “Ele os trouxe para fora para o mal, para matá-los nas montanhas, e para consumi-los da superfície da terra? Vire-se de sua ira feroz, e afaste-se deste mal contra seu povo.
13 Ka tuna da bayinka Ibrahim, Ishaku da Isra’ila, waɗanda ka rantse da kanka cewa, ‘Zan mai da zuriyarka kamar taurarin sama kuma zan ba wa zuriyarka wannan ƙasa wadda na yi musu alkawari, za tă kuma zama abin gādonsu har abada.’”
Lembre-se de Abraão, Isaac e Israel, seus servos, a quem você jurou por si mesmo, e lhes disse: 'Multiplicarei a sua prole como as estrelas do céu, e toda esta terra de que falei darei à sua prole, e eles a herdarão para sempre'”.
14 Sai Ubangiji ya yi juyayi, bai kuwa kawo wa mutanensa bala’in da ya yi niyya ba.
Então Yahweh se afastou do mal que ele disse que faria ao seu povo.
15 Musa ya juya, ya sauka daga kan dutsen da alluna biyu na Alkawari a hannuwansa. An yi rubutun a kowane gefe, gaba da baya.
Moisés virou-se, e desceu da montanha, com as duas tábuas do pacto na mão; tábuas que estavam escritas de ambos os lados. Elas foram escritas de um lado e do outro.
16 Allunan aikin Allah ne; rubutun kuma rubutun Allah ne, da ya zāna a kan alluna.
As tábuas eram obra de Deus, e a escrita era a escrita de Deus, gravada nas tábuas.
17 Sa’ad da Yoshuwa ya ji surutun mutane suna ihu, sai ya ce wa Musa, “Kamar akwai ƙarar yaƙi a sansani.”
Quando Josué ouviu o barulho do povo enquanto gritavam, disse a Moisés: “Há o barulho da guerra no acampamento”.
18 Musa ya amsa ya ce, “Ba ƙarar nasara ba ce, ba ƙarar wanda yaƙi ya ci ba ne; ƙarar waƙa ce nake ji.”
Ele disse: “Não é a voz daqueles que gritam por vitória. Não é a voz daqueles que clamam por ser vencidos; mas o barulho daqueles que cantam que eu ouço”.
19 Da Musa ya kusato sansanin, sai ya ga ɗan maraƙin da kuma mutane suna rawa. Sai fushinsa ya yi ƙuna, ya kuwa jefar da allunan da suke hannuwansa, allunan kuwa suka farfashe a gindin dutsen.
Assim que chegou perto do acampamento, ele viu o bezerro e a dança. Então a raiva de Moisés esquentou, e ele jogou as tábuas fora de suas mãos, e as quebrou sob a montanha.
20 Sai ya ɗauki ɗan maraƙin da suka yi, ya ƙone a wuta; sa’an nan ya niƙa shi ya zama gari, ya barbaɗa garin a ruwa, ya sa Isra’ilawa suka sha.
Ele pegou o bezerro que eles tinham feito, queimou-o com fogo, moeu-o em pó e o espalhou sobre a água, e fez as crianças de Israel bebê-lo.
21 Ya ce wa Haruna, “Mene ne waɗannan mutane suka yi maka da ka kai su ga wannan zunubi mai girma?”
Moisés disse a Aaron: “O que essas pessoas fizeram com você, que você trouxe um grande pecado sobre eles”?
22 Haruna ya amsa ya ce, “Kada ka yi fushi da ni ranka yă daɗe, ka san yadda mutanen nan suke da saurin yin mugunta.
Aaron disse: “Não deixe a raiva de meu senhor esquentar”. Vocês conhecem o povo, que está voltado para o mal.
23 Sun ce mini, ‘Ka yi mana alloli waɗanda za su yi mana jagora, game da wannan Musa dai, wanda ya fito da mu daga Masar, ba mu san abin da ya faru da shi ba.’
Pois eles me disseram: 'Faça-nos deuses, que irão adiante de nós'. Quanto a este Moisés, o homem que nos tirou da terra do Egito, não sabemos o que aconteceu com ele”.
24 Sai na gaya musu, ‘Duk wanda yana da kayan ado na zinariya, ya cire?’ Sa’an nan suka ba ni zinariya, sai na jefa cikin wuta, wannan ɗan maraƙi ya fito.”
Eu lhes disse: 'Quem tiver ouro, que o tire'. Então eles mo deram; e eu o joguei no fogo, e saiu este bezerro”.
25 Musa ya duba ya ga mutane sun kauce gaba ɗaya domin Haruna ya sa suka kauce, har suka zama abin dariya ga abokan gābansu.
Quando Moisés viu que o povo estava fora de controle, (pois Aaron os havia deixado perder o controle, causando zombaria entre seus inimigos),
26 Saboda haka sai ya tsaya a ƙofar sansani ya ce, “Duk wanda yake na Ubangiji yă zo wurina.” Sai dukan Lawiyawa suka taru wurinsa.
então Moisés ficou no portão do acampamento, e disse: “Quem estiver do lado de Javé, venha até mim”! Todos os filhos de Levi se reuniram a ele.
27 Sa’an nan ya ce musu, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Kowane mutum yă rataya takobinsa, yă kai yă kawo daga wannan gefe zuwa wancan cikin sansani, kowa yă kashe ɗan’uwansa, da abokinsa, da kuma maƙwabcinsa.’”
Ele lhes disse: “Yahweh, o Deus de Israel, diz: 'Cada homem põe sua espada na coxa, e vai e vem de porta em porta por todo o campo, e cada homem mata seu irmão, e cada homem seu companheiro, e cada homem seu próximo'”.
28 Lawiyawa suka yi yadda Musa ya umarta, a ranar, mutane wajen dubu uku suka mutu.
Os filhos de Levi fizeram de acordo com a palavra de Moisés. Cerca de três mil homens caíram do povo naquele dia.
29 Sa’an nan Musa ya ce, “An keɓe ku ga Ubangiji a yau, gama kun yi gāba da’ya’yanku da’yan’uwanku, ya kuma albarkace ku a wannan rana.”
Moisés disse: “Consagrai-vos hoje a Javé, pois cada homem foi contra seu filho e contra seu irmão, para que ele vos dê hoje uma bênção”.
30 Kashegari Musa ya ce wa mutane, “Kun yi zunubi mai girma. Amma yanzu zan hau wurin Ubangiji; wataƙila zan iya yin kafara domin zunubinku.”
No dia seguinte, Moisés disse ao povo: “Vocês pecaram um grande pecado”. Agora eu irei até Yahweh. Talvez eu faça expiação por seu pecado”.
31 Don haka Musa ya koma wurin Ubangiji ya ce, “Kaito, mutanen nan sun yi zunubi mai girma! Sun yi wa kansu allolin zinariya.
Moisés voltou a Iavé e disse: “Oh, este povo pecou um grande pecado e se fez deuses de ouro”.
32 Amma yanzu, ina roƙonka ka gafarta zunubinsu, in ba haka ba, to, ka shafe ni daga littafin da ka rubuta.”
Mas agora, se você quiser, perdoe o pecado deles - e se não, por favor, tire-me de seu livro que você escreveu”.
33 Ubangiji ya amsa wa Musa, “Duk wanda ya yi mini zunubi, shi zan shafe daga littafina.
Yahweh disse a Moisés: “Quem quer que tenha pecado contra mim, eu o apagarei do meu livro”.
34 Yanzu tafi, ka jagoranci mutanen zuwa inda na yi zance, mala’ikana kuma zai sha gabanku. Duk da haka sa’ad da lokaci ya yi da zan yi horo, zan hore su domin zunubinsu.”
Agora vá, conduza o povo ao lugar de que lhe falei”. Eis que meu anjo irá diante de vós. No entanto, no dia em que eu castigar, castigá-los-ei por seu pecado”.
35 Ubangiji kuwa ya bugi mutanen da annoba, saboda abin da suka yi da ɗan maraƙin da Haruna ya yi.
Yahweh atingiu o povo, por causa do que eles fizeram com o bezerro, que Arão fez.

< Fitowa 32 >