< Fitowa 32 >

1 Sa’ad da mutane suka ga Musa ya daɗe bai sauko daga dutse ba, sai suka taru kewaye da Haruna suka ce, “Zo, ka yi mana alloli waɗanda za su yi mana jagora. Game da wannan Musa wanda ya fitar da mu daga Masar dai, ba mu san abin da ya faru da shi ba.”
Aa naho nirendre’ ondatio te nalaom-pizotso boak’ ambohitse añe t’i Mosè, le niropak’ amy Aharone ondatio nanao ty hoe, Miongaha, andranjio ndrahare zahay, hiaolo anay; fa i Mosè zay, indaty ninday antika niavotse an-tane Mitsraimey, nofi’ay ty nizò aze.
2 Haruna ya amsa musu ya ce, “Ku tuttuɓe zoban zinariya waɗanda suke kunnuwan matanku, da na’ya’yanku maza da mata, ku kawo mini.”
Aa hoe t’i Aharone am’ iereo, Apitsoho an-tsofim-bali’ areo naho amo ana-dahy naho anak’ ampela’ areoo o bange volamenao, le endeso amako.
3 Saboda haka dukan mutane suka tuttuɓe’yan kunnensu suka kawo wa Haruna.
Aa le napitso’ ondaty iabio o bange volamena an-dravembia’ iareoo vaho nendese’ iereo mb’ amy Aharone mb’eo.
4 Sai ya karɓi abubuwan da suka ba shi, ya yi gunki na siffar ɗan maraƙi, ya sassaƙa shi da kayan aiki. Sa’ad da mutane suka gani, sai suka tā da murya suka ce, “Waɗannan su ne allolinku, ya Isra’ila, waɗanda suka fitar da ku daga Masar.”
Rinambe’e am-pità’ iareo naho nitsene’e amam-pisokirañe naho namboare’e bania nitranaheñe, vaho hoe iereo, Intoy o ndrahare’oo, ry Israele, i ninday azo niakatse an-tane Mitsraimey.
5 Da Haruna ya ga haka, sai ya gina bagade a gaban ɗan maraƙi, ya yi shela ya ce, “Gobe akwai biki ga Ubangiji.”
Aa naho nioni’ i Aharone, le nan­dranjy kitrely aolo’eo vaho nikoike ty hoe: Hamaray ty ho takataka am’ Iehovà.
6 Saboda haka kashegari, mutane suka tashi da sassafe suka miƙa hadaya ta ƙonawa, da hadaya ta salama. Bayan haka suka zauna suka ci, suka sha, suka kuma tashi suka yi rawa.
Le nitroatse maraindrain-tsikiake iereo te loak’ andro nisoroñe naho nanese engam-panintsiñañe; le niambesatse ondatio nikama naho ninoñe vaho niongake le nihisa.
7 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Sauka, gama mutanenka, waɗanda ka fitar da su daga Masar sun ƙazantu.
Le hoe t’Iehovà amy Mosè, Akia mizotsoa! Fa naniva vatañe ondaty nendese’o niavotse an-tane Mitsraimeo
8 Sun yi saurin juyawa daga abin da na umarce su, sun kuma yi wa kansu gunki na siffar ɗan maraƙi. Sun yi sujada ga ɗan maraƙi, suka yi hadaya gare shi, suka kuma ce, waɗannan su ne allolinka ya Isra’ila, waɗanda suka fito da kai daga Masar.”
fa nivike aniany amy làlañe linilikoy; ie nampitranake sare bania naho nitalahoa’e naho nisoroña’e vaho nanao ty hoe, Intoy o ndrahare’oo, ry Israele, i ninday azo nienga an-tane Mitsraimey!
9 Ubangiji ya ce wa Musa, “Na ga waɗannan mutane, mutane ne masu taurinkai.”
Hoe t’Iehovà amy Mosè, Fa nitreako ondatio; inao! toe ondaty gam-pititia!
10 Yanzu ka bar ni kurum fushina yă yi ƙuna a kansu, in hallaka su. Sa’an nan in maishe ka al’umma mai girma.
Ie amy zao, angao iraho, hiforoforoa’ ty haboseko, ho forototoeko, vaho ihe ty hanoeko foko ra’elahy.
11 Amma Musa ya nemi tagomashin Ubangiji, Allahnsa ya ce, “Ya Ubangiji don me fushinka zai yi ƙuna a kan mutanenka, waɗanda ka fisshe su daga Masar da ikon hannunka mai girma?
Fe niambane am’ Iehovà Andria­nañahare’e t’i Mosè nanao ty hoe: Ry Iehovà, ino ty isolebora’ ty fifombo’o am’ondati’o nindese’o niakatse an-tane Mitsraime añe an-kaozaran-dra’elahy vaho an-kafatraram-pitàñeo.
12 Don me za ka sa Masarawa su ce, ‘Ai, da mugun nufi ne ya fito da su don yă shafe su daga fuskar duniya’? Ka juya daga fushinka mai zafi, ka ji tausayi, kada ka kawo masifa a kan mutanenka.
Aa vaho tsy hatao’ o nte-Mitsraimeo ty hoe te Nakare’e hijoia’e, hañohofa’e loza ambohitseo vaho ho mongore’e an-tane atoy? Iambohò o fifombo’o miloroloroo vaho ferenaiño tsy hampianto ondati’oo.
13 Ka tuna da bayinka Ibrahim, Ishaku da Isra’ila, waɗanda ka rantse da kanka cewa, ‘Zan mai da zuriyarka kamar taurarin sama kuma zan ba wa zuriyarka wannan ƙasa wadda na yi musu alkawari, za tă kuma zama abin gādonsu har abada.’”
Tiahio i Avrahame, Ietsàke vaho Israele mpitoro’o nifantà’o am-pañova’o naho nitsara’o ty hoe: Hampitomboeko ho mira amo vasian-dikerañeo ty ia’ o tarira’ areoo naho ze hene tane nivolañeko te hatoloko an-tarira’ areo vaho ho lovae’ iareo nainai’ey.
14 Sai Ubangiji ya yi juyayi, bai kuwa kawo wa mutanensa bala’in da ya yi niyya ba.
Aa le niheve’ Iehovà ty fandrotsahañe nisafirie’e hanoeñe am’ondati’eo.
15 Musa ya juya, ya sauka daga kan dutsen da alluna biyu na Alkawari a hannuwansa. An yi rubutun a kowane gefe, gaba da baya.
Nitolik’ amy zao t’i Mosè nizotso amy vohitsey, am-pità’eo i ravem-bato roe’ i fañinay rey, rave’e sinokitse ami’ty lafe’e roe, aolo’e vaho amboho’e.
16 Allunan aikin Allah ne; rubutun kuma rubutun Allah ne, da ya zāna a kan alluna.
Sàtan’ Añahare i rave’e rey vaho sokin’ Añahare i sokitse finandrak’ amo rave’eoy.
17 Sa’ad da Yoshuwa ya ji surutun mutane suna ihu, sai ya ce wa Musa, “Kamar akwai ƙarar yaƙi a sansani.”
Ie jinanji’ Iehosoa ty korà’ ondatio ami’ty fikontsiaña’e le hoe re amy Mosè: Hoe fikorahan’aly ty an-tobe ao.
18 Musa ya amsa ya ce, “Ba ƙarar nasara ba ce, ba ƙarar wanda yaƙi ya ci ba ne; ƙarar waƙa ce nake ji.”
Fa hoe re, Tsy ty fitreñam-pandrebake naho tsy ty fangoihoia’ o giokeo, fa ty fivolam-pihisa ty tsanoñeko.
19 Da Musa ya kusato sansanin, sai ya ga ɗan maraƙin da kuma mutane suna rawa. Sai fushinsa ya yi ƙuna, ya kuwa jefar da allunan da suke hannuwansa, allunan kuwa suka farfashe a gindin dutsen.
Aa ie narine i tobey naho naha­isake i baniay naho i tsinjakey, le niforoforo ty haviñera’ i Mosè naho navokovokom-pità’e i rave’e rey le nivolentsa am-poto’ i vohitsey.
20 Sai ya ɗauki ɗan maraƙin da suka yi, ya ƙone a wuta; sa’an nan ya niƙa shi ya zama gari, ya barbaɗa garin a ruwa, ya sa Isra’ilawa suka sha.
Rinambe’e i bania tsinène’ iereoy le tineno’e añ’afo ao naho nilisane’e ho deboke naho nafitse’e an-tarehe’ i ranoy vaho nampinome’e o ana’ Israeleo.
21 Ya ce wa Haruna, “Mene ne waɗannan mutane suka yi maka da ka kai su ga wannan zunubi mai girma?”
Le hoe t’i Mosè amy Aharone, Ino ty nanoa’ ondaty retia te nampanoe’o hakeo jabajaba hoe zao.
22 Haruna ya amsa ya ce, “Kada ka yi fushi da ni ranka yă daɗe, ka san yadda mutanen nan suke da saurin yin mugunta.
Aa hoe t’i Aharone, Ko anga’o hangosasàke ty fifombo’ i talèkoy; fohi’o ondatio, te raty tsereke.
23 Sun ce mini, ‘Ka yi mana alloli waɗanda za su yi mana jagora, game da wannan Musa dai, wanda ya fito da mu daga Masar, ba mu san abin da ya faru da shi ba.’
Ie nanao ty hoe amako, Itseneo ndrahare hiaolo anay; fa i Mosè zay, indaty ninday anay niavotse an-tane Mitsraimey, nofi’ay ty nizo aze.
24 Sai na gaya musu, ‘Duk wanda yana da kayan ado na zinariya, ya cire?’ Sa’an nan suka ba ni zinariya, sai na jefa cikin wuta, wannan ɗan maraƙi ya fito.”
Le nanoako ty hoe, Ze am-bolamena, afaho; natolo’ iereo le nafetsako añate-afo ao vaho niboake ty bania tia.
25 Musa ya duba ya ga mutane sun kauce gaba ɗaya domin Haruna ya sa suka kauce, har suka zama abin dariya ga abokan gābansu.
Aa naho nioni’ i Mosè te nitsam­boro­­hotake ondatio (amy t’ie nampidadae’ i Aharone hitsikiha’ o rafelahi’ iareoo),
26 Saboda haka sai ya tsaya a ƙofar sansani ya ce, “Duk wanda yake na Ubangiji yă zo wurina.” Sai dukan Lawiyawa suka taru wurinsa.
le nijohañe am-pizi­lihañe an-tobe ao t’i Mosè nanao ty hoe, Ze mpiam’ Iehovà, mb’ amako mb’ etoa! Le hene nifanontoñe ama’e o ana’ i Levio.
27 Sa’an nan ya ce musu, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Kowane mutum yă rataya takobinsa, yă kai yă kawo daga wannan gefe zuwa wancan cikin sansani, kowa yă kashe ɗan’uwansa, da abokinsa, da kuma maƙwabcinsa.’”
Le hoe re am’ iereo, Hoe t’Iehovà Andrianañahare’ Israele: Songa mañombea fibara añ’ila’e, le mibelobeloa boak’ an-dalambey pak’ an-dalambei’ ty tobe toy le manjevoña: sindre an-drahalahi’e, songa an-drañe’e vaho fonga an-dongo’e.
28 Lawiyawa suka yi yadda Musa ya umarta, a ranar, mutane wajen dubu uku suka mutu.
Aa le nanoe’ o ana’ i Levio i nisaontsia’ i Mosèy vaho miha-telo arivo t’in­daty nikoromak’ amy andro zay.
29 Sa’an nan Musa ya ce, “An keɓe ku ga Ubangiji a yau, gama kun yi gāba da’ya’yanku da’yan’uwanku, ya kuma albarkace ku a wannan rana.”
Aa hoe t’i Mosè, Fa nanokam-batañe am’ Iehovà nahareo anindraoany, amy te fonga niatreatre anadahy naho rahalahy, hanoloram-pitahiañe ama’ areo anito.
30 Kashegari Musa ya ce wa mutane, “Kun yi zunubi mai girma. Amma yanzu zan hau wurin Ubangiji; wataƙila zan iya yin kafara domin zunubinku.”
Ie amy loak’ àndroy, hoe t’i Mosè am’ ondatio, Inao! Inahareo’nio, fa nandilatse an-kakeo jabajaba! aa le hiañambone mb’ am’ Iehovà mb’eo hey iraho; hera hahafijebañe i tahi’ areoy.
31 Don haka Musa ya koma wurin Ubangiji ya ce, “Kaito, mutanen nan sun yi zunubi mai girma! Sun yi wa kansu allolin zinariya.
Aa le nibalike mb’am’ Iehovà mb’eo t’i Mosè nanao ty hoe, Hoy Aba! ty habey hakeo’ ondatio te namboatse ndrahare volamena.
32 Amma yanzu, ina roƙonka ka gafarta zunubinsu, in ba haka ba, to, ka shafe ni daga littafin da ka rubuta.”
Aa ie henane zao naho mete, apoho ty tahi’ iareo, fa naho tsie, faopaoho amy boke sinoki’oy ty añarako.
33 Ubangiji ya amsa wa Musa, “Duk wanda ya yi mini zunubi, shi zan shafe daga littafina.
Le hoe t’Iehovà amy Mosè, Ze nandilatse amako, ie ty ho faoheko amy bokekoy.
34 Yanzu tafi, ka jagoranci mutanen zuwa inda na yi zance, mala’ikana kuma zai sha gabanku. Duk da haka sa’ad da lokaci ya yi da zan yi horo, zan hore su domin zunubinsu.”
Aa le akia hey, Iaolò mb’ amy toetse natoroko azoy mb’eo ondatio; hehe, hiaolo azo i irakoy vaho amy andro fitilihañey ty hampitilihako i tahi’ iareoy.
35 Ubangiji kuwa ya bugi mutanen da annoba, saboda abin da suka yi da ɗan maraƙin da Haruna ya yi.
Aa le nahitri’ Iehovà am’ondatio ty angorosy ty amy bania namboare’ iereoy, i tsinene’ i Aharoney.

< Fitowa 32 >