< Fitowa 32 >

1 Sa’ad da mutane suka ga Musa ya daɗe bai sauko daga dutse ba, sai suka taru kewaye da Haruna suka ce, “Zo, ka yi mana alloli waɗanda za su yi mana jagora. Game da wannan Musa wanda ya fitar da mu daga Masar dai, ba mu san abin da ya faru da shi ba.”
And when the people saw that Moses delayed to come down from the mount, the people assembled themselves to Aaron, and said to him, Arise, make us gods which shall go before us: for [as for] this Moses, the man that brought us out of the land of Egypt, we know not what is become of him.
2 Haruna ya amsa musu ya ce, “Ku tuttuɓe zoban zinariya waɗanda suke kunnuwan matanku, da na’ya’yanku maza da mata, ku kawo mini.”
And Aaron said to them, Break off the golden ear-rings which [are] in the ears of your wives, of your sons, and of your daughters, and bring [them] to me.
3 Saboda haka dukan mutane suka tuttuɓe’yan kunnensu suka kawo wa Haruna.
And all the people broke off the golden ear-rings which [were] in their ears, and brought [them] to Aaron.
4 Sai ya karɓi abubuwan da suka ba shi, ya yi gunki na siffar ɗan maraƙi, ya sassaƙa shi da kayan aiki. Sa’ad da mutane suka gani, sai suka tā da murya suka ce, “Waɗannan su ne allolinku, ya Isra’ila, waɗanda suka fitar da ku daga Masar.”
And he received [them] at their hand, and fashioned it with a graving tool, after he had made it a molten calf: and they said, These are thy gods, O Israel, which brought thee out of the land of Egypt.
5 Da Haruna ya ga haka, sai ya gina bagade a gaban ɗan maraƙi, ya yi shela ya ce, “Gobe akwai biki ga Ubangiji.”
And when Aaron saw [it], he built an altar before it; and Aaron made proclamation, and said, To-morrow [is] a feast to the LORD.
6 Saboda haka kashegari, mutane suka tashi da sassafe suka miƙa hadaya ta ƙonawa, da hadaya ta salama. Bayan haka suka zauna suka ci, suka sha, suka kuma tashi suka yi rawa.
And they rose early on the morrow, and offered burnt-offerings, and brought peace-offerings: and the people sat down to eat and to drink, and rose up to play.
7 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Sauka, gama mutanenka, waɗanda ka fitar da su daga Masar sun ƙazantu.
And the LORD said to Moses, Go, go down; for thy people, which thou broughtest out of the land of Egypt, have corrupted [themselves]:
8 Sun yi saurin juyawa daga abin da na umarce su, sun kuma yi wa kansu gunki na siffar ɗan maraƙi. Sun yi sujada ga ɗan maraƙi, suka yi hadaya gare shi, suka kuma ce, waɗannan su ne allolinka ya Isra’ila, waɗanda suka fito da kai daga Masar.”
They have turned aside quickly from the way which I commanded them: they have made them a molten calf, and have worshiped it, and have sacrificed to it, and said, These are thy gods, O Israel, which have brought thee out of the land of Egypt.
9 Ubangiji ya ce wa Musa, “Na ga waɗannan mutane, mutane ne masu taurinkai.”
And the LORD said to Moses, I have seen this people, and behold it [is] a stiff-necked people:
10 Yanzu ka bar ni kurum fushina yă yi ƙuna a kansu, in hallaka su. Sa’an nan in maishe ka al’umma mai girma.
Now therefore let me alone, that my wrath may wax hot against them, and that I may consume them: and I will make of thee a great nation.
11 Amma Musa ya nemi tagomashin Ubangiji, Allahnsa ya ce, “Ya Ubangiji don me fushinka zai yi ƙuna a kan mutanenka, waɗanda ka fisshe su daga Masar da ikon hannunka mai girma?
And Moses besought the LORD his God, and said, why doth thy wrath wax hot against thy people, which thou hast brought forth from the land of Egypt, with great power, and with a mighty hand?
12 Don me za ka sa Masarawa su ce, ‘Ai, da mugun nufi ne ya fito da su don yă shafe su daga fuskar duniya’? Ka juya daga fushinka mai zafi, ka ji tausayi, kada ka kawo masifa a kan mutanenka.
Why should the Egyptians speak and say, For evil did he bring them out, to slay them in the mountains, and to consume them from the face of the earth? Turn from thy fierce wrath, and repent of this evil against thy people.
13 Ka tuna da bayinka Ibrahim, Ishaku da Isra’ila, waɗanda ka rantse da kanka cewa, ‘Zan mai da zuriyarka kamar taurarin sama kuma zan ba wa zuriyarka wannan ƙasa wadda na yi musu alkawari, za tă kuma zama abin gādonsu har abada.’”
Remember Abraham, Isaac, and Israel thy servants, to whom thou sworest by thine own self, and saidst to them, I will multiply your seed as the stars of heaven, and all this land that I have spoken of will I give to your seed, and they shall inherit [it] for ever.
14 Sai Ubangiji ya yi juyayi, bai kuwa kawo wa mutanensa bala’in da ya yi niyya ba.
And the LORD repented of the evil which he thought to do to his people.
15 Musa ya juya, ya sauka daga kan dutsen da alluna biyu na Alkawari a hannuwansa. An yi rubutun a kowane gefe, gaba da baya.
And Moses turned, and went down from the mount, and the two tables of the testimony [were] in his hand: the tables [were] written on both their sides; on the one side and on the other [were] they written.
16 Allunan aikin Allah ne; rubutun kuma rubutun Allah ne, da ya zāna a kan alluna.
And the tables [were] the work of God, and the writing [was] the writing of God, graven upon the tables.
17 Sa’ad da Yoshuwa ya ji surutun mutane suna ihu, sai ya ce wa Musa, “Kamar akwai ƙarar yaƙi a sansani.”
And when Joshua heard the noise of the people as they shouted, he said to Moses, [There is] a noise of war in the camp.
18 Musa ya amsa ya ce, “Ba ƙarar nasara ba ce, ba ƙarar wanda yaƙi ya ci ba ne; ƙarar waƙa ce nake ji.”
And he said, [It is] not the voice of [them that] shout for mastery, neither [is it] the voice of [them that] cry for being overcome: [but] the noise of [them that] sing do I hear.
19 Da Musa ya kusato sansanin, sai ya ga ɗan maraƙin da kuma mutane suna rawa. Sai fushinsa ya yi ƙuna, ya kuwa jefar da allunan da suke hannuwansa, allunan kuwa suka farfashe a gindin dutsen.
And it came to pass as soon as he came nigh to the camp, that he saw the calf, and the dancing: and Moses's anger waxed hot, and he cast the tables from his hands, and broke them beneath the mount.
20 Sai ya ɗauki ɗan maraƙin da suka yi, ya ƙone a wuta; sa’an nan ya niƙa shi ya zama gari, ya barbaɗa garin a ruwa, ya sa Isra’ilawa suka sha.
And he took the calf which they had made, and burnt [it] in the fire, and ground [it] to powder, and strewed [it] upon the water, and made the children of Israel drink [of it].
21 Ya ce wa Haruna, “Mene ne waɗannan mutane suka yi maka da ka kai su ga wannan zunubi mai girma?”
And Moses said to Aaron, What did this people to thee, that thou hast brought so great a sin upon them?
22 Haruna ya amsa ya ce, “Kada ka yi fushi da ni ranka yă daɗe, ka san yadda mutanen nan suke da saurin yin mugunta.
And Aaron said, Let not the anger of my lord wax hot: thou knowest the people that they [are set] on mischief.
23 Sun ce mini, ‘Ka yi mana alloli waɗanda za su yi mana jagora, game da wannan Musa dai, wanda ya fito da mu daga Masar, ba mu san abin da ya faru da shi ba.’
For they said to me, Make us gods which shall go before us: for [as for] this Moses, the man that brought us out of the land of Egypt, we know not what is become of him.
24 Sai na gaya musu, ‘Duk wanda yana da kayan ado na zinariya, ya cire?’ Sa’an nan suka ba ni zinariya, sai na jefa cikin wuta, wannan ɗan maraƙi ya fito.”
And I said to them, Whoever hath any gold, let them break [it] off: So they gave [it] to me: then I cast it into the fire, and there came out this calf.
25 Musa ya duba ya ga mutane sun kauce gaba ɗaya domin Haruna ya sa suka kauce, har suka zama abin dariya ga abokan gābansu.
And when Moses saw that the people [were] naked (for Aaron had made them naked to [their] shame, among their enemies: )
26 Saboda haka sai ya tsaya a ƙofar sansani ya ce, “Duk wanda yake na Ubangiji yă zo wurina.” Sai dukan Lawiyawa suka taru wurinsa.
Then Moses stood in the gate of the camp, and said, Who [is] on the LORD'S side? [let him come] to me. And all the sons of Levi assembled themselves to him.
27 Sa’an nan ya ce musu, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Kowane mutum yă rataya takobinsa, yă kai yă kawo daga wannan gefe zuwa wancan cikin sansani, kowa yă kashe ɗan’uwansa, da abokinsa, da kuma maƙwabcinsa.’”
And he said to them, Thus saith the LORD God of Israel, Put every man his sword by his side, [and] go in and out from gate to gate throughout the camp, and slay every man his brother, and every man his companion, and every man his neighbor.
28 Lawiyawa suka yi yadda Musa ya umarta, a ranar, mutane wajen dubu uku suka mutu.
And the children of Levi did according to the word of Moses: and there fell of the people that day about three thousand men.
29 Sa’an nan Musa ya ce, “An keɓe ku ga Ubangiji a yau, gama kun yi gāba da’ya’yanku da’yan’uwanku, ya kuma albarkace ku a wannan rana.”
For Moses had said, Consecrate yourselves to-day to the LORD, even every man upon his son, and upon his brother; that he may bestow upon you a blessing this day.
30 Kashegari Musa ya ce wa mutane, “Kun yi zunubi mai girma. Amma yanzu zan hau wurin Ubangiji; wataƙila zan iya yin kafara domin zunubinku.”
And it came to pass on the morrow, that Moses said to the people, Ye have sinned a great sin: and now I will go up to the LORD; it may be I shall make an atonement for your sin.
31 Don haka Musa ya koma wurin Ubangiji ya ce, “Kaito, mutanen nan sun yi zunubi mai girma! Sun yi wa kansu allolin zinariya.
And Moses returned to the LORD, and said, Oh, this people have sinned a great sin, and have made them gods of gold.
32 Amma yanzu, ina roƙonka ka gafarta zunubinsu, in ba haka ba, to, ka shafe ni daga littafin da ka rubuta.”
Yet now, if thou wilt, forgive their sin: and if not, blot me, I pray thee, out of thy book which thou hast written.
33 Ubangiji ya amsa wa Musa, “Duk wanda ya yi mini zunubi, shi zan shafe daga littafina.
And the LORD said to Moses, Whoever hath sinned against me, him will I blot out of my book.
34 Yanzu tafi, ka jagoranci mutanen zuwa inda na yi zance, mala’ikana kuma zai sha gabanku. Duk da haka sa’ad da lokaci ya yi da zan yi horo, zan hore su domin zunubinsu.”
Therefore now go, lead the people to [the place] of which I have spoken to thee: Behold, my angel shall go before thee: Nevertheless, in the day when I visit, I will visit their sin upon them.
35 Ubangiji kuwa ya bugi mutanen da annoba, saboda abin da suka yi da ɗan maraƙin da Haruna ya yi.
And the LORD afflicted the people, because they made the calf which Aaron made.

< Fitowa 32 >