< Fitowa 32 >

1 Sa’ad da mutane suka ga Musa ya daɗe bai sauko daga dutse ba, sai suka taru kewaye da Haruna suka ce, “Zo, ka yi mana alloli waɗanda za su yi mana jagora. Game da wannan Musa wanda ya fitar da mu daga Masar dai, ba mu san abin da ya faru da shi ba.”
And it saw the people that he delayed Moses to come down from the mountain and it assembled the people to Aaron and they said to him arise - make for us gods which they will go before us for this - Moses the man who he brought up us from [the] land of Egypt not we know what? has it happened to him.
2 Haruna ya amsa musu ya ce, “Ku tuttuɓe zoban zinariya waɗanda suke kunnuwan matanku, da na’ya’yanku maza da mata, ku kawo mini.”
And he said to them Aaron tear off [the] rings of gold which [are] on [the] ears of wives your sons your and daughters your and bring [them] to me.
3 Saboda haka dukan mutane suka tuttuɓe’yan kunnensu suka kawo wa Haruna.
And they tore off from themselves all the people [the] rings of gold which [were] on ears their and they brought [them] to Aaron.
4 Sai ya karɓi abubuwan da suka ba shi, ya yi gunki na siffar ɗan maraƙi, ya sassaƙa shi da kayan aiki. Sa’ad da mutane suka gani, sai suka tā da murya suka ce, “Waɗannan su ne allolinku, ya Isra’ila, waɗanda suka fitar da ku daga Masar.”
And he took [them] from hand their and he fashioned it with tool and he made it a calf of molten metal and they said these [are] gods your O Israel who they brought up you from [the] land of Egypt.
5 Da Haruna ya ga haka, sai ya gina bagade a gaban ɗan maraƙi, ya yi shela ya ce, “Gobe akwai biki ga Ubangiji.”
And he saw Aaron and he built an altar before it and he called Aaron and he said a festival of Yahweh [will be] tomorrow.
6 Saboda haka kashegari, mutane suka tashi da sassafe suka miƙa hadaya ta ƙonawa, da hadaya ta salama. Bayan haka suka zauna suka ci, suka sha, suka kuma tashi suka yi rawa.
And they rose early from [the] next day and they offered up burnt offerings and they brought near peace offerings and it sat down the people to eat and to drink and they arose to play.
7 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Sauka, gama mutanenka, waɗanda ka fitar da su daga Masar sun ƙazantu.
And he spoke Yahweh to Moses go go down for it has behaved corruptly people your which you brought up from [the] land of Egypt.
8 Sun yi saurin juyawa daga abin da na umarce su, sun kuma yi wa kansu gunki na siffar ɗan maraƙi. Sun yi sujada ga ɗan maraƙi, suka yi hadaya gare shi, suka kuma ce, waɗannan su ne allolinka ya Isra’ila, waɗanda suka fito da kai daga Masar.”
They have turned aside quickly from the way which I commanded them they have made for themselves a calf of molten metal and they have bowed down to it and they have sacrificed to it and they have said these [are] gods your O Israel who they brought up you from [the] land of Egypt.
9 Ubangiji ya ce wa Musa, “Na ga waɗannan mutane, mutane ne masu taurinkai.”
And he said Yahweh to Moses I have seen the people this and there! [is] a people stiff of neck it.
10 Yanzu ka bar ni kurum fushina yă yi ƙuna a kansu, in hallaka su. Sa’an nan in maishe ka al’umma mai girma.
And therefore leave alone! me so may it burn anger my on them so I may make an end of them and I may make you into a nation great.
11 Amma Musa ya nemi tagomashin Ubangiji, Allahnsa ya ce, “Ya Ubangiji don me fushinka zai yi ƙuna a kan mutanenka, waɗanda ka fisshe su daga Masar da ikon hannunka mai girma?
And he entreated Moses [the] face of Yahweh God his and he said why? O Yahweh does it burn anger your on people your which you brought out from [the] land of Egypt with power great and by a hand strong.
12 Don me za ka sa Masarawa su ce, ‘Ai, da mugun nufi ne ya fito da su don yă shafe su daga fuskar duniya’? Ka juya daga fushinka mai zafi, ka ji tausayi, kada ka kawo masifa a kan mutanenka.
Why? will they say Egypt saying with evil he brought out them to kill them in the mountains and to make an end of them from on [the] surface of the ground turn from [the] burning of anger your and relent on the harm to people your.
13 Ka tuna da bayinka Ibrahim, Ishaku da Isra’ila, waɗanda ka rantse da kanka cewa, ‘Zan mai da zuriyarka kamar taurarin sama kuma zan ba wa zuriyarka wannan ƙasa wadda na yi musu alkawari, za tă kuma zama abin gādonsu har abada.’”
Remember Abraham Isaac and Israel servants your whom you swore to them by yourself and you said to them I will increase offspring your like [the] stars of the heavens and all the land this which I have promised I will give to offspring your and they will possess [it] for ever.
14 Sai Ubangiji ya yi juyayi, bai kuwa kawo wa mutanensa bala’in da ya yi niyya ba.
And he relented Yahweh on the harm which he had spoken to do to people his.
15 Musa ya juya, ya sauka daga kan dutsen da alluna biyu na Alkawari a hannuwansa. An yi rubutun a kowane gefe, gaba da baya.
And he turned and he went down Moses from the mountain and [the] two [the] tablets of the testimony [were] in hand his tablets written from [the] two sides their from this and from this they [were] written.
16 Allunan aikin Allah ne; rubutun kuma rubutun Allah ne, da ya zāna a kan alluna.
And the tablets [were] [the] work of God they and the writing [was] [the] writing of God it engraved on the tablets.
17 Sa’ad da Yoshuwa ya ji surutun mutane suna ihu, sai ya ce wa Musa, “Kamar akwai ƙarar yaƙi a sansani.”
And he heard Joshua [the] sound of the people (in shouting its *Q(K)*) and he said to Moses a sound of battle [is] in the camp.
18 Musa ya amsa ya ce, “Ba ƙarar nasara ba ce, ba ƙarar wanda yaƙi ya ci ba ne; ƙarar waƙa ce nake ji.”
And he said there not [is] a sound of singing of strength and there not [is] a sound of singing of weakness a sound of singing I [am] hearing.
19 Da Musa ya kusato sansanin, sai ya ga ɗan maraƙin da kuma mutane suna rawa. Sai fushinsa ya yi ƙuna, ya kuwa jefar da allunan da suke hannuwansa, allunan kuwa suka farfashe a gindin dutsen.
And it was just when he drew near to the camp and he saw the calf and dancing and it burned [the] anger of Moses and he threw down (from hands his *Q(K)*) the tablets and he broke in pieces them under the mountain.
20 Sai ya ɗauki ɗan maraƙin da suka yi, ya ƙone a wuta; sa’an nan ya niƙa shi ya zama gari, ya barbaɗa garin a ruwa, ya sa Isra’ilawa suka sha.
And he took the calf which they had made and he burned [it] with fire and he ground [it] until that it was fine and he scattered [it] on [the] surface of the water and he made drink [it] [the] people of Israel.
21 Ya ce wa Haruna, “Mene ne waɗannan mutane suka yi maka da ka kai su ga wannan zunubi mai girma?”
And he said Moses to Aaron what? did it do to you the people this that you have brought on it a sin great.
22 Haruna ya amsa ya ce, “Kada ka yi fushi da ni ranka yă daɗe, ka san yadda mutanen nan suke da saurin yin mugunta.
And he said Aaron may not it burn [the] anger of lord my you you know the people that [is] on evil it.
23 Sun ce mini, ‘Ka yi mana alloli waɗanda za su yi mana jagora, game da wannan Musa dai, wanda ya fito da mu daga Masar, ba mu san abin da ya faru da shi ba.’
And they said to me make for us gods which they will go before us for this - Moses the man who he brought up us from [the] land of Egypt not we know what? has it happened to him.
24 Sai na gaya musu, ‘Duk wanda yana da kayan ado na zinariya, ya cire?’ Sa’an nan suka ba ni zinariya, sai na jefa cikin wuta, wannan ɗan maraƙi ya fito.”
And I said to them [belongs] to whom? gold tear [it] off from yourselves and they gave [it] to me and I threw it in the fire and it came out the calf this.
25 Musa ya duba ya ga mutane sun kauce gaba ɗaya domin Haruna ya sa suka kauce, har suka zama abin dariya ga abokan gābansu.
And he saw Moses the people for [was] running wild it for had let [it] run wild he Aaron for derision among [those who] rise against them.
26 Saboda haka sai ya tsaya a ƙofar sansani ya ce, “Duk wanda yake na Ubangiji yă zo wurina.” Sai dukan Lawiyawa suka taru wurinsa.
And he stood Moses at [the] gate of the camp and he said who? [belongs] to Yahweh to me and they gathered themselves to him all [the] descendants of Levi.
27 Sa’an nan ya ce musu, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Kowane mutum yă rataya takobinsa, yă kai yă kawo daga wannan gefe zuwa wancan cikin sansani, kowa yă kashe ɗan’uwansa, da abokinsa, da kuma maƙwabcinsa.’”
And he said to them thus he says Yahweh [the] God of Israel put everyone sword his on thigh his pass and return from gate to gate in the camp and kill everyone brother his and everyone friend his and everyone neighbor his.
28 Lawiyawa suka yi yadda Musa ya umarta, a ranar, mutane wajen dubu uku suka mutu.
And they did [the] descendants of Levi according to [the] word of Moses and it fell of the people on the day that about three thousand person[s].
29 Sa’an nan Musa ya ce, “An keɓe ku ga Ubangiji a yau, gama kun yi gāba da’ya’yanku da’yan’uwanku, ya kuma albarkace ku a wannan rana.”
And he said Moses fill hand your this day to Yahweh for everyone [was] on son his and on brother his and to put on yourselves this day a blessing.
30 Kashegari Musa ya ce wa mutane, “Kun yi zunubi mai girma. Amma yanzu zan hau wurin Ubangiji; wataƙila zan iya yin kafara domin zunubinku.”
And it was from [the] next day and he said Moses to the people you you have sinned a sin great and now I will go up to Yahweh perhaps I will atone for sin your.
31 Don haka Musa ya koma wurin Ubangiji ya ce, “Kaito, mutanen nan sun yi zunubi mai girma! Sun yi wa kansu allolin zinariya.
And he returned Moses to Yahweh and he said I beg you it has sinned the people this a sin great and they have made for themselves gods of gold.
32 Amma yanzu, ina roƙonka ka gafarta zunubinsu, in ba haka ba, to, ka shafe ni daga littafin da ka rubuta.”
And therefore if you will forgive sin their and if not wipe out me please from book your which you have written.
33 Ubangiji ya amsa wa Musa, “Duk wanda ya yi mini zunubi, shi zan shafe daga littafina.
And he said Yahweh to Moses who? [is [the] one] who he has sinned to me I will wipe out him from book my.
34 Yanzu tafi, ka jagoranci mutanen zuwa inda na yi zance, mala’ikana kuma zai sha gabanku. Duk da haka sa’ad da lokaci ya yi da zan yi horo, zan hore su domin zunubinsu.”
And now go - lead the people to where I have spoken to you there! angel my he will go before you and on [the] day visit I and I will visit on them sin their.
35 Ubangiji kuwa ya bugi mutanen da annoba, saboda abin da suka yi da ɗan maraƙin da Haruna ya yi.
And he struck Yahweh the people on that they had made the calf which he had made Aaron.

< Fitowa 32 >