< Fitowa 31 >

1 Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
سپس خداوند به موسی فرمود:
2 “Duba, na zaɓi Bezalel ɗan Uri, ɗan Hur, na kabilar Yahuda,
«من بِصَلئیل را که پسر اوری و نوهٔ حور از قبیلهٔ یهودا است انتخاب کرده‌ام
3 na kuma cika shi da Ruhun Allah, fasaha, azanci, da kuma sani cikin kowace irin sana’a,
و او را از روح خود پر ساخته‌ام و به او حکمت، فهم، دانش و تجربه در همه زمینه‌ها بخشیده‌ام.
4 don yin zāne-zāne na aikin zinariya, azurfa da tagulla,
او در ساختن ظروف طلا و نقره و مفرغ،
5 don yanka da shirya duwatsu, yin aikin katako, da kuma yin kowane irin aikin sana’ar hannu.
همچنین در کار خراطی و جواهر سازی و هر صنعتی استاد است.
6 Ban da haka, na zaɓi Oholiyab ɗan Ahisamak, na kabilar Dan, don yă taimake shi. Na kuma ba da fasaha ga dukan masu aikin sana’ar hannu, don yin duk abin da na umarce ka.
«در ضمن اهولیاب، پسر اخیسامک از قبیلهٔ دان را نیز انتخاب کرده‌ام تا دستیار او باشد. علاوه بر این به تمام صنعتگرانی که با او کار می‌کنند، مهارت مخصوصی بخشیده‌ام تا بتوانند همهٔ آن چیزهایی را که به تو دستور داده‌ام بسازند
7 Tentin Sujada, akwatin Alkawari tare da murfin kafara a bisansa, da dukan kayan aiki na tentin,
خیمهٔ ملاقات، صندوق عهد با تخت رحمت که بر آن است، تمام ابزار و وسایل خیمهٔ عبادت،
8 tebur da kayansa, wurin ajiye fitila na zinariya zalla, da dukan kayansa, bagaden ƙona turare,
میز و ظروف آن، چراغدان طلای خالص و لوازم آن، مذبح بخور،
9 bagaden hadaya ta ƙonawa da dukan kayansa, daro tare da mazauninsa,
مذبح قربانی سوختنی با لوازم آن، حوض و پایه‌اش،
10 da kuma saƙaƙƙun riguna, tsarkakan riguna don Haruna firist da rigunan’ya’yansa maza, sa’ad da suke hidima a matsayin firistoci,
لباسهای مخصوص هارون کاهن و پسرانش برای خدمت در مقام کاهنی،
11 da man shafewa, da turare mai ƙanshi don Wuri Mai Tsarki. Za a yi su kamar yadda na umarce ka.”
روغن مسح و بخور معطر برای قدس. همهٔ اینها را باید درست مطابق آنچه به تو دستور داده‌ام بسازند.»
12 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa,
سپس خداوند به موسی فرمود
13 “Ka faɗa wa Isra’ilawa, ‘Dole ku kiyaye Asabbataina. Wannan zai zama alama tsakanina da ku daga tsara zuwa tsara, saboda ku sani ni ne Ubangiji, wanda ya mai da ku masu tsarki.
«به بنی‌اسرائیل بگو:”روز شَبّات را که برای شما تعیین کرده‌ام نگاه دارید، زیرا این روز نشانی بین من و شما و تمام نسلهای شما خواهد بود تا بدانید من که خداوند هستم، شما را برای خود جدا ساخته‌ام.
14 “‘Ku kiyaye Asabbaci, domin yă zama mai tsarki a gare ku. Duk wanda ya ƙazantar da shi, za a kashe shi; duk wanda ya yi wani aiki a ranar, za a ware shi daga mutane.
پس روز شَبّات را نگاه دارید، چون برای شما روز مقدّسی است. هر که احترام آن را بجا نیاورد، باید کشته شود؛ هر که در آن روز کار کند باید از میان قوم خود منقطع شود.
15 Kwana shida, za a yi aiki, amma a rana ta bakwai, Asabbaci ne na hutu, mai tsarki ga Ubangiji. Duk wanda ya yi wani aiki a Asabbaci, za a kashe shi.
در هفته فقط شش روز کار کنید و روز هفتم که روز مقدّس خداوند است استراحت نمایید. هر کسی در این روز کار کند کشته خواهد شد.
16 Isra’ilawa za su kiyaye Asabbaci, suna bikinsa daga tsara zuwa tsara a matsayin madawwamin alkawari.
این قانون، عهدی جاودانی است و رعایت آن برای بنی‌اسرائیل نسل اندر نسل واجب است.
17 Zai zama alama tsakanina da Isra’ilawa har abada, gama cikin kwana shida Ubangiji ya yi sama da ƙasa, a rana ta bakwai kuma ya daina aiki, ya kuma huta.’”
این نشانهٔ همیشگی آن عهدی است که من با بنی‌اسرائیل بسته‌ام، چون من در شش روز آسمان و زمین را آفریدم و در روز هفتم استراحت کردم.“»
18 Sa’ad da Ubangiji ya gama yin wa Musa magana a kan Dutsen Sinai, sai ya ba shi alluna biyu na Alkawari, allunan duwatsu rubutattu da yatsan Allah.
وقتی خدا در کوه سینا گفتگوی خود را با موسی به پایان رسانید، آن دو لوح سنگی را که با انگشت خود ده فرمان را روی آنها نوشته بود، به موسی داد.

< Fitowa 31 >