< Fitowa 31 >

1 Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
Le Seigneur parla encore à Moïse, disant:
2 “Duba, na zaɓi Bezalel ɗan Uri, ɗan Hur, na kabilar Yahuda,
Voici, j’ai appelé nommément Béséléel, fils d’Uri, fils de Hur de la tribu de Juda,
3 na kuma cika shi da Ruhun Allah, fasaha, azanci, da kuma sani cikin kowace irin sana’a,
Et je l’ai rempli de l’esprit de Dieu, de sagesse, d’intelligence et de science pour toute sorte d’ouvrage,
4 don yin zāne-zāne na aikin zinariya, azurfa da tagulla,
Pour inventer tout ce qui peut se faire par l’art avec l’or, l’argent et l’airain,
5 don yanka da shirya duwatsu, yin aikin katako, da kuma yin kowane irin aikin sana’ar hannu.
Avec du marbre, des pierres précieuses et divers bois.
6 Ban da haka, na zaɓi Oholiyab ɗan Ahisamak, na kabilar Dan, don yă taimake shi. Na kuma ba da fasaha ga dukan masu aikin sana’ar hannu, don yin duk abin da na umarce ka.
Et je lui ai donné pour compagnon Ooliab, fils d’Achisamech de la tribu de Dan. Et dans le cœur de tout ouvrier habile j’ai mis de la sagesse, afin qu’ils fassent tout ce que je t’ai ordonné:
7 Tentin Sujada, akwatin Alkawari tare da murfin kafara a bisansa, da dukan kayan aiki na tentin,
Le tabernacle d’alliance, l’arche de témoignage, le propitiatoire qui est dessus, et tous les vases du tabernacle;
8 tebur da kayansa, wurin ajiye fitila na zinariya zalla, da dukan kayansa, bagaden ƙona turare,
La table et ses vases, le chandelier très pur avec ses vases, et les autels du parfum à brûler,
9 bagaden hadaya ta ƙonawa da dukan kayansa, daro tare da mazauninsa,
Et de l’holocauste et tous leurs vases, le bassin avec sa base;
10 da kuma saƙaƙƙun riguna, tsarkakan riguna don Haruna firist da rigunan’ya’yansa maza, sa’ad da suke hidima a matsayin firistoci,
Les vêtements saints du ministère pour Aaron, le grand-prêtre et ses fils, afin qu’ils s’acquittent de leur office dans les choses sacrées;
11 da man shafewa, da turare mai ƙanshi don Wuri Mai Tsarki. Za a yi su kamar yadda na umarce ka.”
L’huile de l’onction, le parfum à brûler composé d’aromates pour le sanctuaire: ainsi, ils feront tout ce que je t’ai ordonné.
12 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa,
Le Seigneur parla encore à Moïse, disant:
13 “Ka faɗa wa Isra’ilawa, ‘Dole ku kiyaye Asabbataina. Wannan zai zama alama tsakanina da ku daga tsara zuwa tsara, saboda ku sani ni ne Ubangiji, wanda ya mai da ku masu tsarki.
Parle aux enfants d’Israël, et tu leur diras: Ayez soin de garder mon sabbat, parce qu’il est un signe entre moi et vous en vos générations, afin que vous sachiez que c’est moi, le Seigneur, qui vous sanctifie.
14 “‘Ku kiyaye Asabbaci, domin yă zama mai tsarki a gare ku. Duk wanda ya ƙazantar da shi, za a kashe shi; duk wanda ya yi wani aiki a ranar, za a ware shi daga mutane.
Gardez mon sabbat, car il est saint pour vous: celui qui le profanera mourra de mort; celui qui travaillera en ce jour-là, son âme périra du milieu de son peuple.
15 Kwana shida, za a yi aiki, amma a rana ta bakwai, Asabbaci ne na hutu, mai tsarki ga Ubangiji. Duk wanda ya yi wani aiki a Asabbaci, za a kashe shi.
Pendant six jours vous travaillerez, au septième jour c’est un sabbat, repos saint pour le Seigneur, quiconque travaillera en ce jour-là, mourra.
16 Isra’ilawa za su kiyaye Asabbaci, suna bikinsa daga tsara zuwa tsara a matsayin madawwamin alkawari.
Que les enfants d’Israël gardent le sabbat, et qu’ils le célèbrent en leurs générations. C’est un pacte éternel
17 Zai zama alama tsakanina da Isra’ilawa har abada, gama cikin kwana shida Ubangiji ya yi sama da ƙasa, a rana ta bakwai kuma ya daina aiki, ya kuma huta.’”
Entre moi et les enfants d’Israël et un signe perpétuel; car c’est en six jours que le Seigneur a fait le ciel et la terre, et au septième il a cessé son œuvre.
18 Sa’ad da Ubangiji ya gama yin wa Musa magana a kan Dutsen Sinai, sai ya ba shi alluna biyu na Alkawari, allunan duwatsu rubutattu da yatsan Allah.
Or, le Seigneur ayant achevé les discours de cette sorte sur la montagne de Sinaï, donna à Moïse les deux tables de pierre du témoignage, écrites du doigt de Dieu.

< Fitowa 31 >